Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 65

Chapter 65

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,195 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ji ta ce zasu yi magana, ya ce "Ina jinki". "Uncle so nake yi nima na cike jamb foam". Ya ji zuciyar sa ta buga, sai ya danne, cikin dabara dan ya fahimci inda ta dosa. Ya ce " da kam ina da buri ki yi a wannan shekarar, kafin lokacin da komai zai kammala na samun admission kin yaye Jawad sai ki fara karatun ki, ba wata matsala". "Yanzu kuma shikenan sai ba zan yi ba?" Ta fa'da da gatsali. "Ya sake dannar zuciyarsa ya ce " za ki yi mana, amma dai sai next year". Ta tunzuro sosai ta ce "kenan sai nan da shekaru biyu kake nufi zan fara?" Ba ja in ja ya ce " eh". Jin haka ta fara sakin magaganu "Ni wallahi bazan yarda ba, kafin nan da shekaru biyu only God knows mai zaka mayar da Ni". Ya yi shiru yana ta neman tsarin Allah ya kare zuciyar sa daga sharrin shaidan da fishi. Jin ya mata shiru ba'kin cikin ta ya karu,ta fashe masa da kuka mai sauti, tana fadin son kansa ya yi yawa, duk 'kawayenta kowa na karatu sai ita kadaice mai zaman banza da kashe wando. Rukota yayi zuwa jikinsa tana fizgewa, kan dole ya kwantar da ita, yasa hannun sa ya zagayeta. Ya ce "Duk kawayen na ki fa'da mini me kamar Jawad? fa'da mini mai miji irin naki da yake tsananin son ki". Ta yi shiru tana jan hanci, sai kuma ta ce "su ai ba'a tauye su ba, ba a rufe su a gida ana shirin tsofar da su ba". Ya yi shiru, yana nazarin maganganunta, da ya tabbatar kitsa mata aka yi. Ya sake fadin yanzu zaman aure ne ya zama abin kashe wando da tauyewa a gurinki? duk yadda Allah ya miki ni'ima, kin raina?" " Kawai ni son kanka ne ya dame ni" Mai na yi miki na son kai a zamantakewar mu?" "Gasu nan kala kala, ka sani haihuwa dole, sannan ka rufe ni a gida, kai kuma kullum kana ganin yanmata, wataran sai inji zaka w amarce da mai degree". "Su Halima sun zo too nan ko?" Ya fada ba tare da yasan a fili ya fada ba. "Ba su zo ba". "Hmmmm! kawai ya fa'da ya fara lalubarta a kokarinsa na son ya kawar da bacin ran dake neman taso masa. Ai kuwa ta buge hannun sa tana cewa " Dan Allah ka bari, kullum aikin kenan, ka fitine ni da daddare, danka ya tsotse ni da rana, ga kuma wadda yake cikima bai barni ba, so haba da wanne zan ji". Ai kuwa hakurinsa ya 'kwace ya ce "Duk ma wadda suka zo suka miki famfo, ke kuma kika yarda ina tabbatar miki kidahuma suka mayar da ke, sannan maganar karatun da kike ganin sun tsere miki da shi, su a gidajen iyayen su aka basu damar su yi". Maganar ta mata ciwo ainun a harzuke ta ce "wato ni iyayena basu bani dama ba kenan?" "Eh" kawai yace ya tsuke bakin sa, ai kuwa ta kara 'karfin kukanta, tana ta yunkurin tashi amma ya danneta ya'ki bata dama. Sosai suka yi rikici, saboda ya ki amincewa da ra'ayin ta, na ta yi jamb a wannan shekarar. Sai dai kan dole ya ajiye nasa fishin, Yana fadin ta yarda da shi, bazai taba juya mata baya ba, ita kanta yake so ba wani abu na kyan surarta ko zurfin ilimi ba. indai zata biyewa maganganun wasu, ba abin da zata ci ribarsa a rayuwar ta, ko karatun take yi, wasu sai sunce ta 'ki aure da sauran maganganun marasa Da'di. Sannan ba abin da yake ruguza Jin dadin zamantakewar aure irin ka bawa wasu dama su shigo cikin matsalar gidanka. Tun a daren suka shirya, ya saukar da ita, daga famfon su Halima. Haka rayuwar ta cigaba da gungurawa da su,har Allah ya sauki Sa'adah lafiya, ta haifi kyakkawar yarinya mai kama da ita kwabo da kwabo, sai dai yarinyar da lalura ta zo, ko kuka bata yi ba. Aka ri'ke su a asibiti, ko numfashi sai da oxygen take zuka, kwanata biyu tace ga garinku nan. fadin irin tashin hankalin da Sa'adah ta shiga ma, bata lokaci ne, domin tunda ta dora ido akan yarinyar nan, sonta ya shigeta fiye da na Jawad. Ashe mai gajeran kwana ce. Kan dole ta ha'kura, ba kunya ta karbi Jawad a hannun Inna ta cigaba da shayar da shi ba tare da an ro'ke ta ba. Mk ya dinga tarairayarta da lallashi, da nuna soyayya har ta warware ta cigaba da jegonta cikin salama. Da yardarsa da amincewarsa suka je asibiti aka aunata, aka dora ta kan maganin tsarin iyali da ya dace da jininta, duk dan ta samu ta huta ta gyagije, shima ya samu hutawa da ita, da sau'kin gorin da ta ke masa na ya maida ta akuya😃. *SURAYYA DAHIRU*. ✍🏼✍🏼 25/03. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._* *A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba*. *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. 63/64. *Shekara daya a gaba*. Zuwa lokacin shekarun su uku da aure, a shekarar Allah ya yiwa Hajiya Babba rasuwa, a dalilin ciwon siga da ya kamata, ba'a gane da wuri ba, har ya taba kodarta, kwananta uku a asibiti ta rasu! mutuwar da ta gigita dukkan yan gidan su Mk dama wadda yasan Hajiya, barin Hajiyar Bichi da akayi zaman makoki ita tana gadon asibiti. Kwarai suka shiga alhinin rashinta, sai dai ita mutuwa duk yadda zaka yi, ba zata dawo da mutumin data dauka ba, dole aka ha'kura aka bita da addu'a. Mafarin dawowar Hajiyar Bichi Kano gaba'daya kenan, kullum ta Allah sai ta yi kukan rashin Hajiya, ko na ido, ko na zuci, karshe sai ta musu addu'a tare da mijinsu, tana fatan itama ta riske su cikin aminci. Mutuwar Hajiya Babba yasa Hajiyar Bichi ta gane abubuwan da Hajiyar ta kare , mussaman na rashin tasowar fitina a tsakanin yaran, tunda ta kwanta dama, yaran gidan kansu ya fara rabuwa mussaman manyan yaransu mata na 'dakin Hajiya Babba, da suke ganin dama kamar mallake musu uwa Hajiyar Bichi ta yi, kawai Samira a cikinsu bata biye musu to kuma itace karamar su. Haka Hajiyar Bichi take ta ha'kuri da su tunda dai uwarsu ba abin da bata mata na alheri ba, duk yadda suke 'da'darewa da ita, yi take yi kamar bata gane manufar su ba, Abbas da Akil ne basa bata matsala, ko dan su maza ne? Su Halima sun sami nasarar samun admission, dan haka ba sosai suke zuwa gidan Sa'adah ba, saboda sun koma new side. Amma duk ranar da suka sami sararin zuwa gidanta sai Mk ya gane saboda yadda take daukan sabbin dabi'u. Ranar wata litinin Safina da Halima sunje students affairs na cikin Jami'ar, gun a cike da dalibai kowa na yin abin da yake gabansa. Suna daga can baya, kamar

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});