Chapter 137
Chapter 137
jikin Zainab, itama idonta ya ciko ta kasa ce mata komai, tana tuki tana taya Sa'adah kuka. Da kyar Zainab ta shanye kukan ta ce "Ai Halima tana cikin bala'i ke har Safinan ma, domin dai saurayin Halima ya ki aurenta ne adalilin wastewarsu suke yi. Dake akwai alaka tsakanin su da gidan iyayen saurayin shine aka masta masa amma ko kadan babu kwanciyar hankali a tare da ita. "Ita Kuma Safina har yau dai bata karbi result dinta ba, kiga dai a bayansu da shekaru masu yawa kika shiga makarantar amma kin kammala kin barta". Aure kuwa shiru kake ji sai dai ana nan ana addu'a. Komai lokaci ne. Amma su kam hakkin kashe aure ne ya saka suka kasa samun nasu auren". Cikin kuka sosai Sa'a ta ce "Tabbas su Halima sun yi wa rayuwa ta illah, Amma kuma ai da gudunmawata, yarda na yi da su, sannan nima ina da tawa matsalar, bayan wadda suka cusa min, kawai iza mini wutar suke yi, Amma ni na hura abata. Dan haka na yafe musu, amma bana fatan mua'amala ta sake hadamu, rabona da su tun ina gidan Malam, in sha Allah kuma rabuwarmu kenan domin tarayya da su halaka ce, na rufe babinsu har abada, dan haka kema daina yi mini maganar su". Zainab ta dinga lallashin Sa'adah da maganganu masu taushi, tana nuna mata, ta yawaita addu'ar sau'kin kishi, itama zata taya ta, sannan yadda ta yi maganar a fita mata da shi waje suyi magana a gadarance, amma ya tashi duk da baya jin da'di ya isa ta gane har gobe ita ke jan ragamar zuciyar sa, sai dai dole ya yiwa Farida adalci domin matarsa ce, dole kuma zai sota. Zainab ta nisa ta ce "Dan Allah Sa'adah ki 'dore da kyawawan dabi'un ki, kar ki bari kishi ya mayar da ke 'yar gidan jiya, kin san dai yanzu ba ke ka'dai bace, kuma Wallahi duk son da namiji yake yiwa mace indai ta cika kishi da korafi, fita fit take yi a zuciyarsa. Ke ce uwargida tunda baki yi wani auren ba, dole ki 'dauki hakuri mai yawa. Ki koyi hakuri da juriya, duk yadda kike da mutum kar kiyi zancen abokiyar zamanki da ita mussaman dangin miji, domin duk ranar da abu ya ha'do ku da su, sai sun zayyane mata komai, a hada da sharri ma, daga nan girman ki ya zube a idonta, itama kuma ta sami damar da zata dinga fa'din munanan dabi'un ki". "Na gode miki Zainab! Na sani ke din mai sona ce ubangiji ya sanya mu cikin masu zumunci dominsa". Sa'a ta fa'di hakan a sanyaye. Zainab ta ce "gida zan ajiye ki, ko gidan Anty Sumayya?". A tunzure ta ce "gidan ubana zaki ajiye Ni, ai Ni da gidanta sai ta neme Ni". Zainab ta yi shiru! ta san tana tofawa baza su rabu cikin da'din rai ba. Wasu daga cikin halayyar Sa'a a jinita ne ilimi ko shekaru ba zai sa ta sauya ba, rikici na cikin abin da ba zata daina ba. A Daren ranar Baba Isa ya dawo asibitin ya fa'dawa Mk ranar juma'ah mai zuwa za'a mayar da aurensa da Sa'adatu, amma ta nemi abarta ta kintsa kafin ayi maganar tariya tunda titsiye ubanta ya yi mata, ba dan tana so ba. Ya ce " Na kuma yi mata wannan laminin, dan haka ba zata tare ba, sai ta shirya, wannan umarni na ne". Baban ya nisa ya ce "Soyayya da sanin darajar Dan Adam ne kawai ya sanya Malam Basiru zai sake baka aure a Karo na biyu! Ka sani da ni da mahaifinka ra'ayin mu daya, shawarar mu daya, hakanan neman kudinmu daya, abin da Zan fa'da maka yau, na tabbatar da yana raye a gabansa zan fa'da maka domin ka sani idan ina waje baya ta'ba nuna shine ubanku yana dora ni akan komai nasa matu'kar anan Kano ne, da bashi da dan'uwan jini. To ka saurare ni da kyau ni na karba maka amanar yarinyar nan, idan har ka bari ta wulakanta ina rantse maka da Allah ni ka wulakanta, na kuma tabbatar idan har ka wulakanta ni, zaka wulakanta Kabiru, hakkin abotarmu ba zai bari ka ga haske ba, ko bayan ba raina, ina maka wasiyya akan yarinyar Malam Basiru domin ni dai banga mai arziki a wannan zamanin irinsa ba, Ubangiji ya bashi wadatar zuciya, ya bashi alheri mai yawa, wadannan kuma sune kololuwar arziki". Da tsananin farin ciki Mk ya ce "Na ji Baba, in sha Allah ba zan sake kunyata ku ba, komai zata yi zan yi ta ha'kuri, zan kara hakuri akan ha'kuri. Ya sauko ya durkushe a gaban dattijon ya ru'ko hannun sa ya ce " Baba ina maka shaida baka watsar da iyalin amininka ba, har yau din nan da tsufa ya cimma maka sosai, baka huta da yi mana hidima ba. Ina yi maka fatan samun aljannar da Annabi ya yi bishara ga masu kyautatawa iyalan wadda suka rasu". Jin wannan albishir din ya sake 'karfafawa Mk jiki, domin zuciyarsa ta yi haske. Washagari da safe aka sallame shi. Ya isa gida bisa rakiyar Dr 'Karfi, tarba na mussaman ya samu daga Farida. 'Karfi bai jima sosai ba ya tafi. Mk ya dinga biyewa Farida na yadda take ina ka saka da shi. Ya fito wanka ya tarar da ta ajiye masa kaya a bakin gado, gajeran wando ne tiri kwata kalar ruwan 'kasa, sai farar riga ti.shet ya fesa body spray ya sanya kayan da ta riga ta feshe su da turaransa na Versace. Tawul din da ya dauro, ya dauka ya rataye shi a bandakin, yana fitowa ita kuma ta shigo dauke da tiren kayan abinci. Yana zaune bakin gado yana kallon yadda ta yi masa shimfida, ta fara zuba masa abincin da ya kasance dankalin turawa da miyar albasa sai gashashiyar kaza, gefe yankakkiyar kankana ce jawur da ita, an lullubeta da ledar rufe abinci. Sama sama ya ci abincin, ya mayar da hankalinsa wurin shan kankana, ya kalleta ya ce "zanga ranar da zaki daina bani lemo da safe". Ta mike da sauri tana cewa"wallahi na dafa maka shayin ga su cups nan flask din na manta". Cikin kankanin lokaci ta kawo masa, da kanta ta zuba masa, tunda ba ma'abocin shan shayi da madara bane. Bayan ya kammala ta 'ballo masa magungunansa ya sha. Ya mike ya ce " Bari na sauka na dan kewaya, bana jin ciwo a tare da ni, amma sam jikina babu karfi". Ta ce "hakan ma babu laifi, ko na dauko maka lucozade it will help". Ya kalleta ya ce "Bari na kewayo dai, so nake mu yamutsa shimfidar can." Ya yi nuni da gado. Kunya ta kamata ta yi murmushi, ba tare da ta sake cewa komai ba. Ya juya ya fita. Hakan kuwa aka yi, domin bai wani jima ba ya dawo, hakanan duk yadda yake jin rashin kuzari, sai da ya zartar da kudirinsa. Duk yadda take ro'kon ya bari ya warware sosai, amma bai ji ba. Sai fa'di yake "kewar ki na yi sosai, har addu'a nake na samu sauki na dawo gida, ba dan komaai ba, sai dan na kasance tare da ke". Da'di ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157