Chapter 117
Chapter 117
*SADIK ABUBAKAR* 93-95. Ana idar da Sallar isha Baffa bai tsaya a shagonsa ba, saboda yadda ya ke zumudin tattauna al'amarin da Mk ya zo masa da shi a yammacin yau, dan haka kai-tsaye gida ya dawo. Sai da ya kamallah cin abincin da aka gabatar masa ya wanke hannu da baki. Ya kalli Inna ya ganta duk a takure tun safe haka ya ke ganinta sukuku. Cike da kulawa ya ce "me yake damun ki ne Salamatu?" A sanyaye ta ce "Ba komai jikin ne nake jinsa ba tsanani, amma lafiya ta kalau". Nan kuwa mafarkin da ta yi ne ya saukar mata da rashin walwala. "Allah ya rufa asiri" Baffa ya fa'da yana kallonta, ta amsa da "ameen a takaice. "Ina tafe da albishir mai dadi wadda na tabbatar zai tsananta jikin nan naki saboda tsananin karfin farin-cikin da zai saukar Miki a zuciya da ma gangar jikin ki gaba'daya". Ta gyara zama ta ce " Ai kuwa kana da Babban goro fari kal Baffan Iyah". Da murmushi ya ce "Abin da muka Dade muna addu'a da fatan ya kasance ne zai tabbata bayan mun debe kauna da samunsa". Zuciyar Innah ta sake takura amma sai ta shanye ta ce "Al'amarin ubangiji ya wuce hakan, yana zartar da komai a sadda ya nufa". "Baffa ya ce "kwarai kuwa komai nufin Allah ne, bana dai kukanmu ya kare domin ubangiji ya nufa zaman Iyah yana daf da karewa a gabanmu, dazun nan Mutari ya zo mini da wannan albishir din, tun yamman na so na fa'da miki, ganin ki wani iri yasa na ce wannan maganar mai dadice bari na bari sai mun zauna". Yana rufe baki ta fashe masa da kuka sosai fiye da wadda ta yi akan auren da Mk ya yi. Kuka sosai ta dinga yi, tana ambaton raini ne zaisa Mukhtar ya iya zuwa gabansa ya ce zai mayar da Iyah a yanzu, bayan ya gama wulakanta ta, ya gama cusa musu ba'kin ciki. Ba dan karfin imani ba da yanzu barin jikinta ba ya aiki saboda tsananin tozarcin da Muutar ya yiwa Iyah har da su, shine yanzu da aka samota da kyar zai dawo ya ce zai mayar da ita, saboda yana ganin komai ya ce maka haka zaka yi masa?" Baffa ya yi shiru yana sauraronta, wannan ne karon farko tun aurensu da ta zauna take fa'da masa magana cikin kara'di da daga murya, kullum harshenta a kasa yake dan haka ya mata uzziri domin ba dabi'arta ba ce. Ya zuba mata ido yana kallon yadda take kuka sosai tamkar yarinya karama. Ya ce "Yanzu wannan kukan na menene Salamatu?" Kai tsaye ta ce "Na ba'kin ciki ne, saboda wallahi na tsani duk abin da zai hada Iyah da Muutar, Jawad ne a tsakanin su ubangiji ya raya shi, amma ni kam na rufe babin wannan yaron mai kafirin ri'ko, da 'Kullaci da kuma rashin ragayya". "To kuma idan ubangiji bai rufe babinsa da Iyah ba fa? Ya ya zaki yi ne?" Kafin ta yi magana ya sake cewa na bashi dama ya nemi amincewarta, zan kuma ta ya shi neman yardarta". Ta kuwa sake fasa kuka tamkar wata sa'ar Iyah. Ya hassalo ya ce "lallai kin bani Babban goro fari kal Salamatu! na gode miki, amma abin da zan fa'da miki, 'daya ne, Ni ne na haifi Iyah kuma nine wakilinta, ko da shari'a ta bata damar ta zabi wadda ta aminta da shi, a matsayinta na bazawara, Nima kuma shari'ar bata ba ta bata damar yi mini kwangen biyayya ba, dan haka ba zance miki komai a yau ba, sai ta zo gidan nan a gaban ki zan tambayeta ra'ayinta. Da ra'ayin ta zaku ga matsayata". Haka tsofaffin masoyan suka kwana zuciyoyinsu ba da'di amma Inna ta ta nan kan ba'kanta tana fatan ko zaman mota kar Allah ya sake hada su bare zaman aure, shekaru bakwai yarinya na zaune, sai yanzu tana shirin tsayar da miji zai lallabo ya watsa maneman, kai Muutar ya cika tabbataccen marar kunya, kuma marar mutunci, ta tabbatar zai iya aikata abin da ta gani a mafarkinta sai dai da ikon ubangiji ba da Iyanta ba. A bangaren Sa'adah kuwa ta shanye murnar dawowar Mk, domin sai da suka zauna da Suamayyah ta sake gane ba 'karamin wauta ta yi ba da ta bari ta ji da'din dawowarsa cikin rayuwarta, domin washagari da zata fita zuwa kotu hawaye Sumayya ta dinga yi tana cewa "Iyah yanzu dai da kike da shekaru talatin da biyu ai ya kamata ace kin fahimci ba abin da mace zata ri'ke a duniya sama da martabarta da 'kimarta. Domin kyau da arziki duk suna samun tawaya, amma idan mace ta ri'ke darajarta to ko da tsufa ya yi wa kyakkawar surarta tawaye wannan 'kimarta da ta ri'ke zata bata kariya. Kar ki bari matsananciyar soyayyar da kike yiwa Mukhtar tasa ki kasa gane a yanzu kinfi bu'katar ki yi daraja a maimakon samun son zuciyar ki. Sa'adah da take jin magaganun Sumayya har cikin kanta ta dago ta kalleta, sai ta ji a yau tausayin Sumayya ne ya kamata saboda yadda take ganin rauni da wata irin fargaba a kwayar idanuwanta, tana kuma ganin wata irin soyayya da jini kawai ke samar da ita saboda tsananin karfinta da amincinta. Ta matsa ta rungumeta cikin rawar murya ta ce "Na gode Anti! Ko yau Baffah da Inna suka barmu na san Zan yi kukan rashin ganinsu ne, da kuma adduionsu gare ni, Amma ba na rashin gata ko rashin samun wani abu ba, na tabbatar ubangiji ya zaba mini ke ki zame mini Yar uwa kuma garkuwa domin ya san idan ban samu irin wannan katangar ba zuciya ta tana iya tarwatsewa adalilin jarbawar rayuwata mai zafi ce, Ina tabbatar miki Anty ke ka'dai idan na kalle ki na ga tarin kaunar da kike mini fiye da ta ya'yan cikin sai na yi ta godewa ubangiji domin gatan da ya yi mini mai girma ne". Suka dinga kuka tamkar anyi musu Rashi ne. Da kyar suka rabu Sumaayya ta bita har hanyar waje tana fa'din ki rufe dukkan kofofin da kika san Mukhtar zai gan ki, idan kuma kaddara ta sake hada ku, to ki rufe dukkan kofofin da zai ji kayyawan kalmomin bakin ki domin shi din bai cancanta ba, bai dace da ke ba, shekaru bakwai da Kika yi, ba shi kika tsaya jira ya zo ya miki alfarmar mayar da aurenku ba. kin yi wadannan shekarun ne kawai dan gina Goben ki, da samarwa kai nutsuwa. Sa'adah ta kasa bu'de baki ta yi magana domin kuka ne zai kwace mata mai karfi, saboda kalaman Sumayya tausayi su ke baata. Tana tafe tana yiwa Sumayya addu'a da dukkan ahalinta tana fatan shakuwa da soyayyar da Jawad da Khairat suke yiwa juna ta bisu har girmansu dan su sake hada zuri'arsu ta zama dunkulalliya. Tana isa kotun sai ta sake tarar da shari'ar da ta bata mamaki, mahifin Khalil hukumar ya'ki da yiwa kasa zagon kasa da ta'annati wato (E.F.C.C) ta gurfanar domin tuhumarsa da take yi da sama da fa'di da ma'kudan kudaden da ya wawure a lalitar gwamnati a laokcin da yake shugaban maaikatan gwamnati (Head of
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157