Chapter 150
Chapter 150
wadda na tsana, Dan Allah baka ji a zuciyarka ka tozartani ba?" Da sauri ya ce " Ni ban tozarta ki ba, domin 'auren da na yi 'kaddarata ne, wadda ko muna tare ba zan iya tsallakewa ba. Ta ture shi ta ce "Ai kuwa zamu rayu a haka cikin damuwa, domin zuciyata ba zata huce ba, har sai ka yarda ka wulakantani, ka mini hukuncin da ya wuce laifina". Ya sake rungumeta tsantsan tamkar zai mayar da ita cikinsa ya ce "Anya mutum yana tozarta zuciyarsa da rayuwarsa? Amma tunda shine abin da zaisa ki yafe mini, shine abinda zanyi ki dawo mini da nutsuwata, to na yarda na wulakanta ki, amma wallahi ba intentionally na yi hakan ba, ki yafewa masoyinki, kamar yadda na yafe miki, ko na tuna abubuwan da kika yi mini, a take nake jaddada cewar Ubangiji ya zama shaidar na yafe miki, ya kuma hane ni tunowa". Da rawar murya ta ce "Ai ni ko ina son na manta din ba zai yiwu ba, a da kai din nawane ni ka'dai, kome zan yi maka na san ba inda zaka je ka kwana zaka dawo gare ni ne, amma yanzu fa? Zan dinga rabaka ne da wata muddin rai". Ta karasa cikin kuka na sosai. Shi kansa da ya tuna bala'in da ya shiga da ya ganta da Khalil ya gamsu ita din jarumace, domin shi akanta ba zai iya shanye abin da ita ta shanye ba, ya dinga ji har zuciyarsa yana taya ta Jin ciwon kaddarar nan da ta kutso musu. Ya Dora bakinsa daidai kunnenta ya ce "Daga yau din nan ba zan sake maimata miki wannan kalmar ba! Ki ri'keta ta zame miki jagora a zaman da ubangiji ya kaddara zamu yi". Ya nisa ya ce "Wallahi ban taba son wata halitta a doron 'kasa irin ki ba, Hajiya ce kawai ta fiki darajah a duniyata. Ke nake yiwa so na 'kauna, so na sha'awa, so na burgewa, wani irin so nake miki da a kullum ina tuna ki sama da sau sabain a rana, ke kadaice nake tuna abin takaicin ki, amma sai na tsinci kaina da yin murmushi. Ke kadaice kike mini iyashege ya burge ni. Ke kadaice macen da idan na kalla sai na tsinci kaina da yawan ambaton Alhamdulillah! Ke ka'daice macen da idan na ta'ba ki, ba ki mayar mini da marta ni ba, nake Jin bacin rai da tashin hankali. Haka nan ke ce macen da nake fatan idan na tsinci kaina a aljannah na fara tozali da ita cikin jerin matayen da ubangiji zai bani. Wallahi idan kika cire Hajiya ba wadda nake jin sonsu a raina da zuciyata irin ke da d'anki." Ya nisa ya cigaba da cewa "Ba zan miki karyar bana son Farida ba, ba zan miki karyar bata da wata daraja a idona ba, hakanan ba zance miki bana jin da'din zama da ita ba. Sai dai idan har gaskiya zan fa'da miki! Ina jiye miki a wayi gari Farida ta yi kunnen doki da ke a zuciyata, koma ta zarta ki, domin ita din mai hakuri ce, mai kawaici ce, ta sani na fi sonki, amma bata ta'ba tayar mini da hankali akan hakan ba. Zuciya a kirjina take kawai, amma bani nake sarrafa ta ba, ubangiji ne, Annabi kuma ya ce an gina zuciya da kaunar wadda yake kyautata masa". Jikinta ya laushi irin tubus din nan, tana gasgata dukkan furucinsa, ta kuma gasgata tana da kafiya da kaifin harshe. Tun ranar da ya auri Farida bata sake jin nutsuwa a zuciyarta akansa ba, sai yanzu. Ta nisa ta ce "Shikenan! Ka yi ha'kuri zan gyara, zan kuma kiyaye, amma dai ka dinga mini uzziri, ni akan ka, bana iya sarrafa kishina, ka taya ni addu'a, ka kuma kara ha'kuri da ni, kar kuma ka bu'de kofar da wata macen zata kamo ni a zuciyarka". Ta fa'da hawaye na zubowa. Da sauri ya matsa ya rungumeta, yana jin tamkar an yaye masa wata katuwar masifa a rayuwarsa, yana jin wata irin salama tana mamaye dukkan zuciyarsa. Ashe wannan 'daaurin da 'kirjinsa ya yi, ashe wannan fargabar da yake tsintar kansa a ciki, duk saboda rashin samun aminci ne daga wajen Sa'a? A yanzu da ta yarda zasu zauna lafiya sai ya ji tamkar anyi masa bushara da gidan aljannah ne. A fili ya dinga fa'din "Alhamdulillah! Allah kasa karshen tashin hankalin da zamu fuskanta kenan, Allah ka sanya wannan shine karshen jarrabawar mu". Sau uku tana yun'kurin yin magana sai ta kasa, da ya lura da hakan sai ya ce "fill free, fa'da mini abin da ke ranki". Ta tura baki gaba ta ce "Amma dai ka yi mini al'kawarin ba zaka ha'da ni zama da wata matarka ba, kuma yanzu na tabbatar waccan part din na Amaryarka ne". Ya sake ru'ko ta sosai ya ce "Ban manta al'kawarin ba, amma sai nake ganin a waccan gidan da kika tsara yadda za'a gina shi, na miki wannan al'kawarin, yanzu kuma ai bashi bane". Da rawar murya ta ce"kar ka hadani zama da ita, kar ka bari na dinga ganin mua'amalarku, zaka iya rasa ni a dalilin ciwon zuciya ko hawan jinin farat 'daya". "Ina son ki koyi jarumta Sa'adah! Ina son hankali na ya tsaya a wuri daya, a yanzu da nake matu'kar mararinki, idan na rabaku zan halaka ne, Ina tabbatar miki zan tare ne a inda zuciyata tafi so, shi kuma adalci wajibi ne ka yiwa kowa. Addinin musulunci! Addinin adalci ne, ubangiji ya sani namiji ba zai iya raba soyayyar matansa ta zama daidai a zuciyarsa ba, sai akace an masa uzziri anan, ma'ana bai yi laifi ba dan ya so wata sama da wata ba. Har ilah yau Sharia bata ce dole abin da ka yi da wannan, idan ka koma wajen wannan ma sai ka yi mata irin wannan ba, domin ansan ba zamu iya ba. Amma duk da hakan sai da Annabi ya yi ta wasiyyar kar mu jingine mace, mu ratayeta ita ba sakakkiyar mace ba, ita ba matar aure ba, dole a rabon kwana, muhalli, abinci da sutura ya zama daidai (eqaul). Shari'ar musulunci ta yiwa mata gata da adalci, ta yadda ko ba ke aka fi so ba, to kuwa indai ana kan tsarin sharia din ba za'a ki wulakanta ba". Ya numfasa sannan ya ce "ki min hakuri zaki koma wanccan gidan amma ba yanzu ba, ki bari nima na koyi jarumtar da zan kiyaye ka'idojin shari'a". A hankali ta ce"To" ba dan tana so ba, sai dan kar ta cigaba da yi masa gardama yana ganin Farida ce mai biyayya kawai. Ya tsura mata ido yana kallonta, sonta sai huda dukkan sassan jikinsa yake yi, cikin kasalalliyar murya ya ce "har yanzu baki huce da ni ba, har yau baki yafe mini ba?" Murya ba amo ta ce "me yasa ka ce haka?" "Har yanzu ban ji kin kira suna na ba, Na sani kuwa idan kina fishi ne kike gatsa sunana dan ki nuna mini iyakata. Idan kuma ba kya son shiga shirgina sai ki yi maganar ki ba tare da kin kama sunan ba" Ta zuba masa wani irin kallon da yake kidima shi,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157