Chapter 28
Chapter 28
maganar aure za ki yi tsalle ki ce bai miki ba, amma kina son abin hannunsu saboda kawai kin 'dorawa kanki sai kin daura abin da kike gani a jikin yaran da 'karfin iyayenku ba 'daya ba" Ta nisa tana jiran ko Sa'adah za ta yi magana sai taji sabanin hakan, duk da dai ta lura jikinta ya sake yin laushi fiye da 'dazu, don haka sai ta sake cewa, "Ki ajiye wannan dabi'ar, sannu a hankali idan kina da rabon yin arzikin za ki yi shi ne. Yanzu dai babban misalin da zan miki da yayarki ne, duk da cewa lokacin da aka aurar da ita ba ki da wayon da za ki gane komai, mijinta ko mashin din da kika raina mai hawansa ba shi da shi, amma a yau mene ne bai mallaka ba? A saninki 'kasashe nawa ya debi iyalinsa suka fita? Wace irin hidima da karamci ne ba ya mana ke ma shaida ce tunda dai ko wannan makarantar da kike yi ba don shi ba, da ba ki yi ta ba, da ace farko ta raina matsayinsa da yanzu ta cim ma wannan jin dadin da kowa ke mata kallon tana ciki? Tsakanin ki da Allah ba don ta sau'ka'ka buri ba ta kai wannan matsayin?" Kai Sa'adah ta girgiza wa mahaifiyarta don kuwa harshenta ya mata nauyi, amma a ranta tana raya in dai akan zaben miji ne an wuce wannan babin, zuciyarta ta riga da ta aminta da MK Bichi kuma shi ma ai talaka ne tunda ko mota ba shi da ita. Jin da'di da son kayan 'kawa kuwa ba mahalukin da ba ya so sai idan bai samu ba, ita a jininta ne son gayu ba wai fariya ko 'karya ta sa a ranta ba. 😀 Don haka ba ta dauki maganar ajiye dogon buri da aka mata nasiha da wani muhimmanci ba. "Kullum addu'a ta Allah ya ba ki miji nagari wanda zai kula da ke da amana, ke ma irin adduar da za ki rike ke nan. Dauki abinci maza ki ci kar ya gama hucewa, Allah ya miki albarka." Ajiyar zuciya ta sauke ta ce "Amin na gode?" Sannan ta ja abincin ta hau ci, danwaken fulawa ne da yaji mai da'din gaske, tana ci tana yaba yadda Innarsu ta iya sarrafa abincin gargajiya masu da'di, kawai dai abincin zamani ne ba ta yin su ko kuma don za su ja kudi ne? Sai ta tsinci kanta da cewa "Allah Inna na kusa daina cin abinci mai nauyi." Cike da mamaki ta ce "Me za ki dinga ci to?" Murmushi ta yi, ta ce "Chips, chicken, sai dangin su pizza, da indomie da kwai, sai na bi bayansu da ababen ruwa irin su juices da yougurt ko hadadden shayi hadin kauri." Salatin da Inna ta 'dauka ne ya sa ta dakatawa tare da tunanin ta yi subutar baki. "Ashe duk togaciyar da na gama yi miki bai shiga kunnenki ba? A gidan uwarki kika san wadannan kayan, wadda ba ta alfahari da abin da ta bude ido ta gani a gidansu, sai hangen kayan wani da ba ya rufa maka asiri! Nasan kina nufin idan kin je gidan miji ne kike tunanin wannan rayuwar za ki yi" Ta kafe ta da ido tana mata kallo mai tsanani sannan ta ci gaba da cewa, "To saurare ni da kyau aure ya wuce wasa tun wuri ki cire wannan tunanin a ranki, gabadaya aure ibada ne, duk abin da akace ibada ne, to ba son ranka za ka yi ko zaka gani ba, sannan ba abin da ke ri'ke da aure gabadaya sai ha'kuri don haka ki cire wannan tunanin a ranki. ki yi fatan Allah ya ba ki miji nagari, da hankalinki zai kwanta, domin komai za ki samu idan ba kwanciyar hankali ina tabbatar miki ba za ki ji dadinsa ba Allah ya shirye ki, adduar da zan dinga miki ke nan." Ta fada da iyakacin gaskiyarta, domin ta lura addu'a ce kawai za ta canja mata Iyah ba hantara ko nuna fishi ba. *** MK yana isa gida ya tarar da Hajiyar Bichi ta zo, a falo ya tarar da su ita da Hajiya Babba suna cin makani wanda ba ya tantamar daga Bichi ta taho da shi, da murna ya hau fadin, "Hajiya ashe da gaske kike da wuri za ki dawo?" Dariya ta yi ta ce "Allah Ya yarda ban dade ba". Suka ci gaba da hirarsu har su Abbas da Ahamad suka dawo aka ci gaba da hirar da su, Maghriba ce ta dakatar da su. Bayan sallar Isha MK ya tarar da Hajiya Babba a dakinta, ya gama kame-kame da soshe-soshen 'keya, sannan ya ce "Hajiya so nake aje a tambayar mini izinin magana da wata yarinya a wajen mahaifinta." Dadi ya kama ta, ta shiga fadin "Alhamdulillah! Allah Ya sa abokiyar arziki ce, ina ne gidan nasu?" Sake kasa ya yi da kansa da kyar ya ce "A babban layin Unguwa Uku suke mahaifinta mai karamin karfi ne amma mutumin kirki ne, na san shi tun kafin nasan yarinyar." Farin ciki ya bayyana a fuskar Hajiiya Babba ta ce, "Yanzun nan za mu tattauna da Hajiyar Bichi tunda Allah ya sa ta zo garin, gobe In Sha Allah zan je har gidan Babanku Alhaji Isa (Aminin mahaifinsu ne) na shaida masa. Sai ya je ya tambayar maka, tunda ka kammala karatun kuma ka iya harkar kasuwanci ba za mu ji tsoron aurenka ba, bare da ikon Allah da wuri za ka sami aikin yi ka ci gaba da rike mu gabadaya." Koda ta sami Hajiyar Bichi da maganar fatan alheri kawai ta yi tare da cewa, "Hajiya Babba ai ke ce uwarsa, ni 'yar addua ce!" Wannan biyayyar da tun fil'azal Hajiyar Bichi ke yi wa Hajiya Babba ta taimaka kwarai wurin samun zaman lafiya a tsakaninsu, tare da saukaka kishin junansu matu'ka da gaske. A satin aka tambayo masa izinin magana da Sa'adah, a take kuma Baffa ya ce ya bashi damar ya nemi yardarta ba don yana jin tsoron halin dan yau ba, da a take zai ce ya ba shi ita, to tsoron kar ta ce ba ta sonsa ta kunya ta shi yasa ya ce idan har sun daidai ta kansu to ya ba shi, aka yi murna aka rabu ana addu'ar Allah Ya sa hadin Allah ne. A ranar Baffa ya zaunar da Sa'adah tare da mahaifiyarta ya ce, "Bakin da suka bakunce ni a yammacin yau, zuwan Iyah ne. Yaron nan Mutari ne ya turo a ba shi iznin neman amincewarki, ni kuma na ba shi dama ya nemi yardarki ba don Ina jin tsoron kada ki yi mini *HALIN YAU* ba, da kai tsaye zan ce na ba shi su zo ayi maganar aure. Saboda yaron nutsatstse ne , ya san mutuncin manya mai kokarin neman na kansa ne, kullum ya zo shagon askinsa sai ya zo ya gaishe ni, ban kuma taba jin hayaniyarsa da wani ba, kiga dai yadda shagon yake cika dam da matasa amma ban taba jin an ce ana fada da shi ba. Da shi muke sallar Magariba da Isha kullum yana sahun gaba, ba zan miki dole ba
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157