Chapter 112
Chapter 112
jikinta, tare da sake cewa "kina addu'ar na samu kudin ya kai na siyan jirgin naki kuwa?" Inna da take gurin ta ji Hawaye na neman kwace mata, ta mike ta shige dakinta, tana jin dadi da tausayin yadda Jawad yake girmama lamarin uwarsa. Dawowarsu Nigeria ya sake wayo sosai, aka saka shi a makarantar Intercontinental college tsananin hazakarsa yasa suka dauke shi J s 3, maimakon aji biyu da zai shiga. Iya turanci gangariya da Jawad ya yi ya janyo masa farin jini ainun a gurin malamai hatta student son abota suke da shi. A haka ya Saba da wani dan ajinsu Muhsin Sani Yar-gaya, a hirar su da Muhsin Jawad ya fahimci Malam da Mami sun rabu ne, wato divorce ne a tsakanin su. Kusan Muhsin ne ya cusa masa dabi'ar kin Farida a dalilin shi Muhsin din mahaifiyarsa ta rasu shekaru biyu, sannan amaryar Baban su azabtar da su take yi, shi da yayarsa makaranta nan da suke zuwa ne kawai bata yi nasarar rabasu da ita ba, hatta magana da mahaifinsu sai a sace suke yi da shi domin shima tsoronta yake ji. A hankali Jawad ya fara janyewa Farida idan ana son aga damuwar sa to weekend ne ace zai tafi gadon kaya. Ba irin rarrashin da Farida bata yi masa amma ya kame daga yawan yi mata hira, idan kuwa yaje gidan a takure zai zauna tamkar bai santa ba, abin ya damu Farida sosai hatta Mk ya damu, ya tabbatar kuma ba zaluntarsa take yi ba tsiya ce kawai irin ta 'Dan Yau. Har aka kai jallin da kuka yake zuwa gidan, idan Hajiyar Bichi ta ce da Mk ya barshi tunda baya son zuwa, ya kafe sai yaje. Rannan dai da abin ya ishe Mk a gaban Hajiya ya dinga fa'din "ko zai shide sai ya je gidan, da suka rayu shekaru biyu tana masa wahala bai 'ki ta ba, sai yanzu saboda ya samu shashar uwa tana kitsa masa maganganun iyashege to kanta zata cuta ta kuma cuci 'danta. Ya kalli Jawad da yake bayan Hajiya yana kuka da hawaye ya zare masa ido ya ce "idan na kuma jin kace mini zaka unguwa uku sai jikinka ya fa'da maka ai can ba gidanku bane, kana kin gidan ubanka kana kwadayin gidan wasu, zo ka shige girma da arziki tun ban tashi ba, kuma nan din ma ba zaka dawo ba can din da baka so a can zaka zauna". Jawad ya rushe da kuka yana cewa "Hajiya ki ce ya dawo da Ni dan Allah". Aikuwa haka ya tafi da shi yana kuka , sai dai kaya kala biyu Hajiyan ta bashi tabbacin zai dawo kenan. Shiyasa ya rage sautin kukan nasa. Wannan matsalar gaba'daya Mk Sa'adah ya jinginawa ita ya dinga tunanin hanyar da zai magance ta. Ana haka Jawad ya dinga wani irin zazzabi, karshe farankama(chicken fox) ta feso masa a jiki. Hajiyar Bichi da kanta ta bugawa Inna waya ta sanar musu, Inna bata yi kasa a guiwa ba ta zo ta duba shi har da tsarabar kayan dubiya, ba yadda bata yi da Sa'adah akan su tafi tare su dubo Jawad amma ta ki. Da kyar Inna ta shawo kanta bayan taje da kwana biyu, Suka shirya Suka je da Zainab Ma'aji wacce a lokacin wattannin ta biyar da aure, da kuma cikin wata hudu a jikinta. Ma'aikaciya ce a hukumar kidaya ta kasa reshen jahar Kano. Cikin kwalliya sosai Sa'adah take, ta dawo wata irin mace da gayu da ilimi suka ratsata mussaman da Alhaji Mamman ya sake dawowa cikin rayuwar ta, ba karamin kudi yake sakar Mata ba, ita kuma bata kwangen yin sutura ta daukar hankali. Komai nata daukar ido yake yi, ado take a yanzu irin wadda bata yi zaton zata yi irinsa ba, amma kuma cike da hankali da nutsuwa. A wannan lokacin ta kammala karatunta tana makarantar horar da lauyoyi ta Bagauda(call to Bar). A motar mijin Zainab Suka je bayan sun tsaya a hanya sun masa siyayya ta sosai, kai tsaye suka shiga gidan ba wani nauyi domin dai Sa'a ta kan zo gaida Hajiyar duk da ba kasafai ba. A falon Hajiyar suka tarar da Mk yana shafawa Jawad calamine lotion a jikinsa ko ina jikin Jawad din maganin ne adalilin duka jikinsa ta feso masa har fuska, farin maganin ya maida Jawad wani iri. Suka gaisa da Hajiya cike da girmamawa, suka tambayi mai jiki. Zainab ce ta gaida Mk cikin mutunci, har tana cewa "Uncle rabon da na ganka har na mance". Ya yi murmushi yana cewa "kina cikin daliban da nake cikiyarsu Zainab! Ya mijinki da Yara?" Ta 'kasa kuma kallon Sa'a kawai ya ke yi zuciyarsa na wani irin tsalle, yayin da ita ta yi tamkar bata ganshi ba, ko arzikin gaisuwa bai samu ba, ko Jawad da yake kusa da shi, sau daya ta masa sannu ta maida hankalinta wurin Hajiya. Rashin gaisawar da basu yi ba, ya ta'ba Hajiya kwarai da gaske, yayin da Mk ya dinga fargabar wayewar da cigaban da ya gani a tare da ita, kwarai da gaske ta banbanta da Waccan Sa'adan da ya rayu da ita. Zainab sai zungurar ta take yi akan ta gaishe shi, amma ta yi mirsisi. Suna zaune Ahamad ya shigo ya ganta yana cewa "yau wa nake gani kamar Antina" Da murmushi sosai ta ce "Nice me zan Samu?" Ya mi'ka mata 'datar da yake ci, aikuwa ta karba ta hau ci, hakan kawai sai da Mk ya ji haushi dan me zata ci ragowan yawun Ahamad? Ta mi'ka masa mukallin mota tana cewa "daure ka debowa 'danka kayan dubiya da mamarsa Zainab ta kawo masa". Da azama ya karba, ya dinga shigo da kayayyaki har Hajiya ta ce " wanne irin hidima kuka yi haka Sa'a? Sai kace wadda zai bude shago?". Ran Mk ya baci saboda yadda yaga uban kayayyakin ciye ciye masu tsada sai kawaia zuciyarsa ta kisima masa Bazawarinta ne ya yi wannan siyayyar. Ya dinga huci karshe ya fice bai ko sake kallon kayan ba, da kyar ya ce da Zainab ta gaida gida. Jawad ya warware ya koma zuwa School amma rashin son zuwa gidan Farida na sake ruruwa a ransa kullum da kuka yake isa gidan, sannan har yaje ya dawo sai ta 'kure da ya yi mata magana har zane shi Mk ya yi amma bai canja ba. Kan dole Mk ya samo masa makarantar kwana ba tare da ya yi shawara da kowa ba, da kyar aka samo makarantar saboda anci karfin zangon karatu na biyu. Sai da komai ya kammala na makaranta ya fa'dawa Hajiya dan kar ta hana, Kan dole ya dauki Jawad ya kai shi makarantar gwamnatin tarayya ta Kiyawa, a kokarinsa na nisanta shi da masu hure masa kunne da masu son cusa masa muguwar dabi'a. A dai dai wannan lokacin aka dawo da Mijin Sumayya aiki Kano, da Karin girma sosai. Tuni dama sunyi gininsu a gandun albasa layin kwankwaso, da farin ciki Suka tattaro Suka dawo kano cikin gidansu na alfarma. Zainab ta haihu ta sami Musa sunan uban mijinta ne, Sa'adah ce ta yi masa inkiya da Walid. Farida ce dai shiru har yanzu da suke
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157