Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 141

Chapter 141

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

jin da'din yadda ya fara samun lagonta dan haka ya sake lankwashe murya ya cigaba da 'kiran ba kakkautawa. Zuciyarta ta yi laushi tubus, ta sami sau'kin nauyin da ta yi adilin kishi, domin ta gasgata shi da ya ce har yanzu shine bai canja ba, ba kuma abin da ya ragu na soyayyarta a zuciyarsa. Cikin muryar tabarah ta zallan shagwaba ta ce "Haba Mana, Inna ta na cikin gidan nan fa! Ni dai ka daina, na amsa Na'am, Na'am Na'am". Ya zuba mata idanuwansa da suka kada tamkar ya tashi daga barci ne. Murya ba amo ya ce "Ba zan boye miki ba, sha'awar ki nake ji sosai, tunda muka rabu nake fama da matsanancin ciwon kai da mara, sosai na sha wahala a farkon shekaru uku da rabuwarmu, a lokacin da nake Uk, na sha zarya a gaban manyan likitoci, suka tabbatar mini rashin mace a kusa da ni ne dalili. Da na yi aure na samu sassauci, baya tashi sosai, ko ya tashin ma baya takura ni sosai, amma wallahi Sa'adah, tun ranar da muka kai ki gidan Anty Sumayya nake Jin alamun ciwon na neman takura ni, jiya ko runtsawa ban yi ba, adalilin yadda nake jin ciwon da marata take yi, ga gangar jikina taki sarrafuwa domin ba abin da take so ya rabeta sai ke". Ya bu'de dukkan hannuwansa yadda yakee mata tun fil azal, da rawar murya ya ke fadin "come closer to me my dear"! Kishin yadda ya tabbatar mata, bayan ya yi aure ya samu sau'kin ciwonsa, ya sake sawa ta hargitse. A tunzure ta ce "ka gaggauta tafiya ka rungumi wadda ta kwantar maka da ciwon rashin mace da ka yi fama da shi a baya! Wai kwana ka yi baka yi barci ba, kwana ka yi dai kana rarrashinta, kana kasheta da soyayya amma saboda ka mayar da ni bitacan shine ka karkace baki kana fa'din min tatsuniyar da ko Jawad yasan 'karya ne tsagwaronta, 'karya kawai". Jikinsa ya yi sanyi, tabbas gaskiyar Baffah ne akwai abubuwa da yawa da Sa'a ba zata canja ba, domin a jininta ne, gashi dai a zahiri hankali ya shigeta, ilimi ya ratsata, Amma kishi yasa agabansa ta karyata shi, ba shayi ko shakka. Wanda shi kuma ba zai ta'ba yarda ya sake daukan kaifin harshenta ba, a yanzu da take shekaru talatin da biyu. Ya mike ya ce "Ni ne mai fa'dar tatsuniyar karya? Ni Kika karyata, nine makaryaci?" Ta saci kallonsa, ta ga yadda ya bata rai sosai, ta yi shiru tana jin guiltiness na kamata, amma ta kasa bu'de baki ta ce masa sorry. Ya kada kai ya ce "Tabdi jam ashe kuwa da sauran ki". Dai dai lokacin Inna ta fito tsakar gida taga zogalen da ta ajiye wa Mk, yana gurin dan haka ta bude baki ta ce "Iyah zo ki daukar masa zogalen nan mana, nasan shi da son zogale". Farin ciki ya mamaye Mk! Ba dan komai ba, sai dan sassaucin da yake gani tare da Innah. Da azama ta amsa, ta kuma mike ta fita duk a kokarinta na kar Inna ta zargi wani abu. Ta dauko ta ajiye masa a inda yake tsaye, kamshinta ya cika masa hanci, da ta sunkuya ajiye masa zogalen, ya ga yadda siket din jikinta ya matu'kar fito da taswirar mazaunanta, sai ya matu'kar kidima, ya dinga kokawa da zuciyarsa domin kuwa, ba zai sake kulata ba, har sai ta bashi ha'kuri. A kausashe ya ce "juye mini a leda sai naje gida zan ci". Ta sake juyawa ta fita! Tana jin tamkar ta bashi ha'kuri ya fasa tafiyar, ta sani badan maganar da ta fa'da ba, da sai anyi kiran sallar azahar da ya tafi, haka Kuma zai ta zama yana rarrashinta da son ya jagwalgwalata. Amma yanzu zai tafi gurin matarsa, ya barta da kewa da bacin ran zuciya. Ta hango shi ya zaunar da Farida a cinyarsa yana bata zogalen a baki, tunda ta san shi da son dora mace a kan cinyarsa. Tana juye masa a ledar ta ri'ke, ta kasa bashi, kawai ta saka masa kuka. Ya yi sakare yana kallonta, yana ayyana ko sai yaushe zata daina kukan banza marar dalili, ya sani tafiya gida da ya ce zai yi ne ya mata ciwo. Tabbas kishinta ba zai bari su yi amarci mai da'di ba, ba zai bari su rayu cikin farin-ciki ba. Shikuma ya riga ya kudire duk runtsi ba zai rabu da FARIDA ba, zai yi kuma dukkan kokarinsa ya ga bai tashi a sahun masu shanyewar barin jiki ranar gobe ba. Wahala ne dai zasu dandana shi da ita tunda idan ranta ya baci, ko idan ya ganta cikin rashin nutsuwa shima hakan zai zama marar nutsuwar. Domin ya tabbatar itace jagorar farin-cikinsa. Ya daure ya kore raunin da yake neman sawa ya fasa tafiyar, ya kalleta sosai ya ce "Zaki san kin ce mini makaryaci, na rantse miki sai na miki abin da gaba idan zaki mini magana, sai kin tauna harshen ki sosai. Godài godài da ke amma lafazinki na yara 'kananu, ko Farida ai ba ta mini irin wannan iyashegen". Ai kuwa ta fàdi kan shimfidarta ta fashe da kuka, tana cewa "Na gode da cin fuska, kullum sai ka mini gorin na tsufa, saboda kawai na haifar maka Jawad! to wadda kake yiwa kallon 'kuruciya saboda Ubangiji ya jinkirta mata haihuwar ta girme ni da shekara guda, domin ina Sha bakwai na kammala sakandire, ita kuwa Sha takwas cif. Amma saboda son sai ka nuna itace mai daraja shiyasa kake bata kuruciya, ni ka maida ni tsohuwar mace, to koma menene dai, kai ka zuke mini komai, sannan daga kai har ita dukkanku kun girme mini". Ya Galla mata harara tare da cewa "Sokuwa marar wayo kawai, wacce ba abin da ta iya sai kaifin harshe da kukan banza". Ya juya ya fice, bayan ya dauki wayarsa a inda ya tashi, ya barta tana kukan banza nata. Sai da ya yiwa Innah sallamah, sannan ya fita. Ya fito ya bu'de but din, ya samu almajirai biyu, ya dinga basu kayan suna shiga da shi. Sai da suka kammala ya basu dari biyar ya ja motar sa ya yi gidan Hajiyar Bichi. Ya isa ya tarar da Hajiya cikin Shirin fita unguwa, ya zauna ya gaisheta, ta amsa da murmushin da ya jima bai ga ta yi masa irinsa ba. Ya murtsike kunya ya ce "Hajiya ki yiwa 'yarki magana, tana nemana da jidali, ta fa'dawa Baban Na'ibawa ba yanzu, zata tare ba, saboda Allah wanne shiri zata yi? Tunda tana jin maganar ki, ki mata magana, wannan ai tsokanar shari'a ne, an daura aure mace ta cigaba da zaman a gidansu". Hajiya ta daure fuska sosai! Ta zuba masa ido na tsawon lokaci, shikuma ya sunkuyar da kansa kasa, ba dan ya yarda ya yi laifin da take masa kallon tuhuma akansa ba. Ta nisa ta Nuna kanta ta ce " Ni ka zo kana fa'dawa wannan maganar? Shi Babanku kana jin nauyinsa, kana ganin mutuncinsa shiyasa ka kasa cewa komai a gabansa, sai ni da ka raina zaka zo ka yiwa rashin ta ido?" Ya kuwa maze ya ce "To ni ya zanyi ne?

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});