Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 75

Chapter 75

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yi karatu, to baza kiyi ba, idan kuma ya zama dole sai kin yi, sai dai kije a matsayin single amma ba matata ba". Hawaye ya balle mata, ta ru'ko hannuwansa cikin rawar murya tace "Na roke ka kar min haka! dan Allah kar bari na gasgata masu fadin ba zaka taba barina na yi ilimi ba". Ido cikin ido yace "gara ki gasgata su Sa'adatu, ada kam na kudiri aniyar ilimi sai kince ya isheki! amma Billahillazi yanzu na fasa, ba ki fara karatun ba, kina iya zagina, bare kuma na baki damar da kullum sai kin fita, kin yi cudanya da mutane daban daban, tunda na gane kawaye zasu iya rinjayar ki, zasu iya canja miki dabi'a, zasu iya ruguza mana kyakkawan zaman mu, daga lokacin na gane barinki karatu mai zurfi ha'dari ne, ilimin sakandiren da kika samu, yasa kina jin kina da yanci, Ina kuma ga kin shiga babbar makaranta, ki zauna ki yi rainon Jawad kawai, tunda nace ki cire loop din nan, amma sun zuga ki, kar ki bari ki tara yara mu tsufar da ke, to ki zauna ki tabbata da kuruciya". Kuka take yi, tana bashi ha'kuri, yace "na gama maganata, zabi na gareki, dan kuwa wallahi ba za kije ki koyo mini karatun raini da rashin da'a ba, a haka kina iya zagina,nan gaba kuma sai dai na ji mari." Kuka take yi tun daga kasan zuciyar ta, a duk tsayin rayuwarta a duniya a ranar ta fara sanin Ashe kuka ma kala kala ne, duk wadda tayi a baya na nisha'di da shagwaba ne, na yau ne take yin na zunzuruntun bacin rai. Ya kalleta yace "Ba abin damuwa bane Wannan fa, domin na riga da na baki damar ki, dan hakama nake ta dan jah baya, dan mu dan saba da rashin tarayyarmu, Ina tabbatar miki idan kin zabi makaranta akan aure! Wallahi zan dauki nauyin karatunki, kuma zan wanke ki a gun su Baffa, zan dauki laifin rabuwarmu Ni ka'dai." Murya na rawa tsabar kuka tace, "Dan girman Allah yaushe na zage ka?" "Kina nufin na miki sharri ba ki zage ni ba?" Ta sake ru'ko hannuwansa da kyau tana harhado kalmomi tace " Ni bance haka ba Malam! amma dan Allah ka yi hakuri, na canja Wallahi, ba zan sake ba" "A ranar da kika zage ni dama na tabbatar miki u will pay for it! zaki yi karatu da yardata ka'dai, idan na gamsu kin canja din da gaske, idan na tabbatar ba mahalukin da zai canja ni a zuciyar ki". Ya zare hannuwansa daga nata ya mike, itama ta mike ta tsugunna ta ru'ko kafafuwansa, tana fadin "Malam bazan iya barinka ba, dan Allah, ba dan halina ba, ka janye wannan kudirin ina son karatun amma da yardar ka nake so". Yace "idan kuwa kina son karatu da izinina, wallahi ba bana ba, to be frank Sa'adatu! ban san time din ba, har sai na gamsu ba third party a tsakanin mu, sai na gamsu na wuce zagi da diban albarka ta kowacce fuska daga gareki". Ta sake shi! sanin halinsa idan ya rantse shikenan ya gama magana, ta ha'kura tana jin bakin ciki tamkar ta mutu! ta huta. Kuka ba irin wadda ba tayi ba, Mk da kansa mamakin kansa ya ringa ji, bai taba zaton zai iya mata haka ba, sai dai wata'kila yadda take gasa masa duk maganar da ta zo bakinta yasa ya iya jarumta haka. Sa'adah tana ji, tana gani, ya hanata makaranta, duk ta zama wani iri, zaman nasu dai gashi nan, ta koma shiru, ba walwala sosai, kullum cikin kunci take amma bakinta dif, sai kuma yanayin data koma ya dame shi, fata yake su koma kamar da, rayuwar farin ciki, amma abin na neman cin tura, a zahiri dai suna zaune lafiya amma kuma babu nisha'di a cikin zaman. Saboda su Halima da suke fadin "dama ai sun san pooling dinta yake yi, ba wata makarantar da zai barta, duk dan'iskan namiji zai yi iya yinsa ya kulle matarsa a gida saboda sun San Annabi baya tuntuben harshe, duk abin da ka yi da matar wani, sai anyi da taka. Wattanni kusan biyu zamansu ba armashi, bata masa komai na laifi, amma kuma ta dadare ranta, suna cikin haka, aka fara babban zabe na kasa, kowa yasan Malaman jami'oi ne baturen zabe, Dan haka wata guda aka dauka ana yiwa su Mk horo na mussaman kan yadda zasu kare muradan yan kasa, kar su yarda ayi amfani da su, ayi wa dimokaradiya kafar ungulu, Malaman addini suka dinga musu wa'azi na suji tsoron Allah su yi gaskiya a cikin aikin da za su yi, karshe suka rufe bayanin da cewa duk wadda aka bashi kudi dan ya yi magudi, to ya karbe kudin ya adana, sannan ya yi adalci, ma'ana ya fadi sakamako na gaskiya. A yanzu da suke shiga shekaru biyar da aure shi da kansa ya tabbatar tsoron ta yake yi, idan akwai abin da ya tsana to ta share shi, ko ta tsiri fushi, ko ya fita sai ya dawo, yasan yadda ya yi ya shawo kanta, yayin da ita kuma take jin kanta a sama komai take so sai ta same shi, SUMAYYA kanta mamakin yadda Sa'adah ta dawo take yi, kullum cikin tsadaddun sutura take , hatta salooon din da Sa'adah take zuwa one in town ne, kullum suka yi waya sai ta mata nasiha ta saukaka buri, ta rage dorawa mijinta hidimar da bai kai ya yi ba. Itakuwa sai tace da ba zai iya ba, ai da bai yi ba, ya hanani karatu ai kuwa dole yamin yadda nake so, tunda idan ban ci ba ma, na waje ne zasu ci, har Sumayya ta gaji ta zuba mata ido tana mata addu'a. Rannan da yamma Zainab Ma'aji ta ziyarce ta, kasancewar ana daukan lokaci kafin su hadu a dalilin Zainab din tana karatu ne a Jami'ar jahar kaduna(K.a s.u). ba kowanne hutun ma take zuwa Kano ba, sai take barin hoste ta tafi gidan kanwar mahaifiyarta ta yi hutunta indai ba mai tsayi bane. Mamamki ta tsaya yi ganin yadda Sa'adah ta koma, ta goge sosai, fatarta ta yi fresh tabbacin tana samun tsadadden mai, tasan Sa'adah Yar gaye ce, amma ko kusa ba kamar yanzu ba, da ta ke samun dukkan wants dinta. Sauyi sosai ta gani tunda ga jikinta, da abubawan more rayuwa na gidan, da cima ta mussaman, ga wata irin ginshira da ta gani a tare da ita. A sanyaye Zainab tace "Kin zama wata Hajiya ko big madam zance? lallai Uncle a gaishe shi, ina Jawad? hatta maganar Sa'adah ta canja sai anfitar mata da wani salo na daban. lamarin da Zainab ta dinga dariya tana fadin ko za ki yiwa kowa wannan iyashegen ban da ni. Suka yi dariya gaba daya sannan suka shiga hira, a gidan Mk ya tarar da ita, ta gaishe shi da girmamawa, shikuma ya dinga mata barka da zuwa cikin karamci, a dan dawowarsa da ya yi , Zainab ta fahimci abubuwa biyu, Uncle Mk ya gama lalacewa akan soyayyar kawarta, yayin da ita kuma Sa'adah take amfani da hakan take yin duk abin da take so. Zainab ta

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});