Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 31

Chapter 31

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,206 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yadda Inna ta kwantar da murya tana lallaba ta, tana cewa a ranta Inna ta koma lallashi. A fili kuma ta ce "To shikenan ki cigaba da addu'a Allah ya sa na ji ina son sa tunda na lura duk ya kwanta muku a rai" "Ai ni tunda na ji Baffanku ya yabe shi na ji ya kwanta mini a rai, kinsan mijin yayarki ma shi ne ya zaba mata, halayensa da nagartarsa kawai ya auna, shi yasa kema nake so ki masa biyayya kar ki yarda ya kubuce miki". Alkalamin *SURAYYA DAHIRU* ✍️✍️. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._* *KAR KU BARI A BARKU A BAYA WURIN KARANTA DADDAN LABARIN NAN*! *⚜️BUƊAƊƊIYAR SOYAYYA⚜️* NA *Jameey yar'mutan kankia*. *Promo* *Promo* *Promo* _Daga yau 21/5/2022 promo dinmu zai fara,har zuwa 30/5/2022 inshaa Allah,ga yanda promo din yake_. *#300-sau biyu a rana* *#500 -sau ukku a rana* *#700 -sau hudu a rana* _Kiyi man wanann number magana danjin ynda zaki biya 08160508316_. *MASU SON A TALLATAH MUSU HAJARSU KOFA A BUDE TAKE* _TUNTUBI_ 08032773332. *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. 36-37. Sannu a hankali cikin nutsuwa MK ke tafiyar da Sa'adah, a sati sau daya yake zuwa zance. Duk da ya karbi lambar wayar Inna tun da yanzu koyaushe wayar na hannunta amma ba kasafai yake kiran ba, duk a kokarinsa na ganin bai raba mata hankali ba, musamman da kullum jarrabawarsu kara kusantowa take yi. A bangarenta kuma sai ta ke ganin kawai rashin daukar ta da muhimmamanci ne yasa yake nuna mata rashin kulawa, musamman yadda Khalil ke kiranta safe da yamma sannan su raba dare ana musayar kalamai, shi yasa ya daina damuwa da rashin saurarar shi da ba ta yi a makaranta. A haka har aka rubuta jarrabawar JAMB, duk kokarin da MK ya yi na ganin Sa'adah ta samu rubuta jarrabawar abin ya ci tura! Saboda yadda Baffa ya ce masa "Ni sakandiren nan ma a dole na bar ta ta kammala ,yar uwarta aji uku kawai ta yi na aurar da ita, don haka ni ba zan barta ta tafi wata babbar makaranta ba, ta zo tafi karfina". Ya dan tsahirta sannan ya rufe maganar da cewa, "Idan Allah ya sa ta zo hannunka komai ma sai ta yi, amma ni a yanzu babban burina shi ne na sauke nauyinta da ya yi saura a kaina, na aurar da ita a hannun da ko ba na numfashi ba za ta koka ba". Kan dole MK ya ha'kura da maganar amma ya kudire a ransa Sa'adah za ta yi karatu har sai ta ce ya ishe ta. Gab da za su fara rubata WAEC wa'adin da MK zai yi a makarantar FGC ya cika, amma saboda yajin aikin da jami'o'i suke yi, yasa hukumar makarantar ta roke shi ya ci gaba da zuwa kafin lokacin da ASUU za ta janye yajin aikin. Kasancewar MK da sakamako mai daraja ta daya (First Class) ya fita, yana cikin wadanda Jami'ar Bayero za ta dauka don yin koyarwa. A haka suka ci gaba da tafiya a baibai tsakanin MK da Sa'adah, shi yana ganin ya ba ta lokacin da za ta yi karatu sosai, ita kuma tana masa kallon wanda bai girmama lamarinta ba, hakan ya sa take saurarar duk wanda ya nuna yana son ta ba tare da tunanin ai tana da wanda take so ba! Musamman da a lokacin damina Baffa ya fi zaman Gogel saboda kula da noman da yake yi, ita kuma Inna zuciyarta daya ta dauka MK ne yake zuwa. A haka har ta kammala makaranta gaba'daya, cikin wannan yanayin ta hadu da Alhaji Mamman! Asibitin (Arewa Surgery) suka je duba Mahaifiyar Safina ita da Halima, sun fito harabar asibitin suka hadu da shi, ya nemi su shigo mota ya kai su, Sa'adah ta'ki amincewa amma da yake tare suke da Halima sai da ta rinjaye ta suka shiga motar, a hanya ya nuna ra'ayinsa akan Sa'adah, wanda sam-sam bai kwanta mata ba, musamman da yake ta gan shi dattijo da alamun yana da iyalai masu yawa a karkashinsa. A lokacin wayar hannun ba ta da yawa sosai kamar yanzu, sannan mai madannai ce komai tsadar wayar. Ya tambayi lambar wayarta, Sa'adah ba ta ce komai ba sai da ya sake tambayar a karo na biyu sannan ta ce "Ba ni da waya." Bai yi mamaki ba tunda a lokacin ba ta zama ruwan dare irin yanzu ba, ko iyayenta ma Sumayya ce ta sayo musu don ta ri'ka gaisawa da su tun da ita ba mazauniyar gari ba ce. Ita kuma ta gaje ta Inna. Halima ta ce "Ba Inna na da waya ba?" Shiru ta yi da alamun dai ba ta son ba da lambar ne, shi kuma sai ya ce "Yawwa 'kawarmu a taimaka a ba ni lambar Innarmu!" Haka Halima ta bude wayarta ta karanto masa lambar Inna saboda ta ga alamun za su sami kudi a tare da mutumin. Duk kokarinsa na son sai ya kai Sa'adah har kofar gidansu, amma hakan bai samu ba, saboda ta kafe akan idan aka gan ta cikin motar da ba a san mutumin ba, za ta fuskanci tashin hankali, wannan kalaman ya sake jin son ta sosai, ya san daga dukkan alamu da ga Babban gida ta fito ma'ana gidan tarbiyya. Kan dole ya kai su gidan su Halima wanda ita ko dar ba ta ji ba, hakan ya sa yake ganin anya iyayen Sa'adah ba tufka suke wannan 'kawar tana musu warwarba? A dan haduwar nan tasu ya lura da kamewar Sa'adah, ya kuma gane rawar kan Halima, a ransa yana rayawa da zarar ya sami Sa'adah zai raba ta da wannan kawar da idan kawancesu ya ci gaba da wanzuwa, zai ta ba tarbiyar Sa'adatu. Halima ta shige gida ta bar su, bai wani jima ba shi ma ya ce zai tafi don ya lura da Sa'adah kamar a tsorace take, kudi ya dauko har kimanin dubu talatin ya ba ta ya ce ta bawa kawarta goma a ciki. Ta tattaro dukkan kunya ta yaba a fuskarta tare da cewa, "Ka bar su ba zan karba ba!" Shi kuma ya na ta fadin "Idan ba ki karba ba, ba zan ji dadi ba Sa'adatu." Da kyar tasa hannu ta karba ta yi godiya bayan ya karbi address din gidansu, wanda kai tsaye address din gidansu Zainab Ma'aji ta bayar. Jiki na rawa ta shige gidan su Halima ta tarar da ita a falo da kaninta suna kallo kasancewar mamansu tana wurin aikinta, haka suka shige dakinta, kudin ta ciro ta nuna mata suka hau ihun murna! Halima na cewa "Ai tunda na gan shi na san akwai rodina tare da shi sannan ba matsolo ba ne." Dariya Sa'adah ta yi tare da cewa, "Kin ga kuwa takanas ya ba da naki sakon." Dadi ya cika zuciyar Halima da ta ji yawan kudaden da ya ba ta, haka ta sake jan Sa'adah zuwa Country

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});