Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 1

Chapter 1

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,220 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

[5/11, 17:15] ~fatieshak🌹: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ *Bismillahir Rahmanir Rahim* *Ina farawa da sunan Allah, ina neman tsari da rubuta 'Barna! Ina rokon na yi rubutun da za'a 'karu , ayi amfani da shi.Tsira da aminci ga shugaba Annabi(S.A.W.).* *GARGADI* _A kiyayi taba min labari na ta kowacce siga, Hakkin mallakar tawa ce ni ka'dai, Dole sai da izinina kafin a karanta shi a kowacce irin kafar sadarwa, wadda ya shiga hakkin mallaka kuma ubangiji ya isar mini._ *JAN KUNNE* *Gaba'daya Wannan labarin kirkirarsa aka yi(Fiction)!haka sunaye da garuruwan da ke ciki bana kowa bane, na zabe sune kawai dan 'kawata labarin, dan haka duk wadda yaci karo da abin da ya yi kamacanceceniya da rayuwar sa bada shi ake ba, arashi ne kawai* *JINJINA* _GA MARUBUCIYA_ *FADILA LAMIDO* *SUGARI BA KI YI FARIN BANZA BA*. *SADAUKARWA* _Tun daga farkon labarin har zuwa karshen sa gaba'daya sadaukawa ne ga shugaban kungiyar_ *LAFAZEE WRITERS* *SADIQ ABUBAKAR*. 1-2 Harabar makarantar kwana ta Gwamnatin Tarayya da ke garin Kiyawa (FGC Kiyawa), cike take mak'il da motoci da jama'a kama daga iyayen yara, da su kansu daliban rukuni-rukuni, gungu-gungu, cike da walwala sai ciye-ciye ake yi kasancewar yau ake ziyarar dalibai (visiting day). Daga can gefen lambun makarantar, wata matashiyar uwa ce da a 'kalla ba za ta wuce shekaru talatin da biyu ba. Zaune take kan lallausar darduma wacce da alamu da ita ta zo, gefenta kulolin abinci ne da kuma ledoji masu dauke da tambarin *Sahad Store.* Zaune take tana baza ido ta ga ta ina tilon dan'ta zai bullo, ba ta ankara ba ta ji an rungume ta tare da ambaton "Mamiii!" Cike da dariya ta dago kai. "Jawad wai ba ka san ka girma ba ne? ba don a zaune nake ba ai da ka kayar da ni." Ya sake komawa ya kwanta a jikinta tare da cewa, "Nayi kewarki Mami! Ina Inna?". "Ta ce, a gaishe ka, shekaranjiya ta tafi Gamawa biki" "Ki ce ba ta yi mini girebar ba kenan?" Ya fada cikin turo baki irin na sakalan yara. "Wace ita? Ai ranar Laraba yini ta yi tana hidimar girebarka, bata samu sukuni ba sai da ta kammala." Sai a lokacin ya saki fuskar yana cewa, "Allah Sarki Innata!" Ya tashi a jikinta ya ci gaba da cewa, "Ina yini?" Ta amsa tana bin sa da kallon mamakin irin girman da ya 'kara cikin lokaci 'kalilan da ba ta gan shi ba, tana mamakin inda ya sami girman jiki tun da dai daga ita har mahaifinsa ba wani girma ne da su na a zo a gani ba, hasalima in ba ka sani ba cewa za ka yi 'kaninta ne. "Kai Mami sai kin gano munina!". Ya fada yana rufe idonsa da hannuwansa. Ta yi murmushi, "Girmanka ne yake ba ni mamaki Jawad ka kerewa tsawona fa!" "To, Mami aike tsayinki kadan ne, ni kuma irin tsayin Babana na yi." "A'a, kai kam sai ka fi shi tsayi duka-duka fa watan jiya ka yi sha uku amma ka zan'kale haka!" Cikin shagwaba ya fara fadin "Haba mana Mami ki daina fada, kar ajiyo. I am 15 fa!" Ta kwashe da dariya tare da cewa "Mantawa na yi ashe ka fi ni sanin ranar haihuwarka?". Daidai lokacin ya zuge Jakarta ya dauko tsaleliyar wayarta ya mik'a mata, ''Bude mini na kira malam na ji ko ya dawo." Ba ta ce uffan ba, ta karba ta bude masa kamar yadda ya bukata. Lambobi ya shiga daddanawa har ya jera lambar da ke adane a 'kwa'kwalwarsa a cikin wayar ya danna kira ya kara a kunne, tamkar da ma jiran kiran ya shiga ake yi, ya ji an dauka ba tare da ba ta lokaci ba, sallama ya yi tare da fadin, "Malam!" Daga cikin wayar aka amsa da, "Jawad kana lafiya? Ka gan ni nan ina kan hanyar zuwa wurinka." Cike da murna yace. "Ka dawo daga Bauchin ke nan?" "A'a ban dawo ba yanzu dai nake kan hanyar dawowa na iso Babaldu zan biyo ta Dutse na iso Kiyawa." Dadi ya kama Jawad, ya shiga masa addu'ar isowa lafiya, tare da cewa, "Ina wajen da muka zauna a waccan ziyarar." Ya kashe wayar yana cewa "Oh! Allah ya so ni, jiya fa da na yi masa waya ha'kuri ya ba ni akan ba zai sami zuwa ba sai satin sama, saboda yana Bauchi, ko don bai ji na amsa masa na ha'kura ba ne, shi yasa ya bar komai ya taho?" Ita dai ba ta sa masa baki ba har ya kammala maganarsa. tana nazarin lokaci a agogon hannunta daya nuna 'karfe biyu har da mintuna talatin da biyar. "Ko ina ne Babaldu kuma? Ko har zai iya isowa kafin hukumar makaranta ta rufe shigowa?" Tabe baki ta yi tana ji a ranta to ina ma ruwanta? Amma wani sashi na zuciyarta na fada mata saboda Jawad ne, ina mama ba wadda ya zo mini? Ya katse mata tunani, "Baban Khalifa ne ba lafiya yana asibiti ka ga ai bai kamata na yi maganar mu taho tare da wani cikinsu ba." "Me ya same shi?" Ya tambaye ta cike da nuna damuwa. "Malaria yake ta yi har ta kada shi." "Muma Mami ita ake ta yi anan, Allah ya sauwa'ke ya bashi lafiya, to yanzun a tasha kika sauka?" Ta girgiza kai tana cewa, "Shatar mota muka dauko ni da iyalan gidan Ma'aji. Ka ci abincin sai mu je ku gaisa, suna can gefen mata." Bayan La'asar ba da jimawa ba, ya iso cikin makarantar sanye yake cikin tsadadden yadi fari 'kal! 'Kafar shi dauke da takalmi cover ba'ki, kansa cike da gashi, ya dora hular zanna-bukar wadda ba ta rufe gashin ba, 'kamshin turaren Versace ke tashi a jikinsa. A hankali yake tafiya cikin nutsuwa, matsakaicin jiki ne dashi, amma dogo ne yanayinsa daya da tauraron wasan kwaikwaiyon nan Yakubu Muhd, ba yadda za ka yi ka kalle shi ka ce shi ya haifi Jawad, sai dan tsananin kamar da Jawad ke yi da shi. Tun kafin ya'karaso Jawad ya hango shi, don haka ya kwasa da gudu ya nufe shi. Ga mamakin Sa'adah, sai ta ga ya 'daga Jawad cak ya yi juyi da shi tamkar yadda yake masa yana yaro. Ya dire shi, ya ru'ko shi ta gefen shi suka doso ta, wadda duk ilahirin mutanen dake wajen sai da suka bi su da ido suna sha'awar Jawad da Babansa. Kujera ya samo masa ya zauna daga gefe, amma ba wani tazara da inda Sa'ada ke zaune, ta juya musu baya. Hira suke cike da doki. "Amma anya Jawad kana karatu kuwa? Ina *C.A* Result dinka?" Ya zura hannu a aljihun wandon shi ya zaro takarda ya mika masa ya karba ya bude yana dubawa, fara'arsa na 'kara fadada, ya ninke ya kalli dan nasa ya ce, "That is my boy weldone! Ka ci gaba da dagewa." "Ni da zan zama direban jirgin sama, ai dole sai na yi karatu Malam, ko ka manta?" "Murmushi kawai Malam din ya yi yana satar kallon gefen da Sa'adah ke zaune kamar ko yaushe ta ci kwalliya ta burgewa cikin tsadadden leshi doguwar riga(bubu), hannayen ta sun ci jan lalle da zobunan Dubai Gold, 'kamshinta na dindin na

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});