Chapter 29
Chapter 29
amma da a ce zan miki zabi ki karba, to da ba zan tsallake shi ba. Idan kuma kin kafe shi ma bai miki to lallai ki tsayar da wanda ya miki da zarar kin kammala makaranta zan aurar da ke, ki ri'ke wannan!" Alkalamin SURAYYA GWARAM ✍️✍️. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._* *TALLAH* *TALLAH*! *KAR KU BARI A BARKU A BAYA WURIN KARANTA DADDAN LABARIN NAN* *⚜️BUƊAƊƊIYAR SOYAYYA⚜️* _NA_ *Jameey yar'mutan kankia*. *Promo* *Promo* *Promo* _Daga yau 21/5/2022 promo dinmu zai fara,har zuwa 30/5/2022 inshaa Allah,ga yanda promo din yake_. *#300-sau biyu a rana* *#500 -sau ukku a rana* *#700 -sau hudu a rana* _Kiyi ma wanann number magana danjin yanda zaki biya 08160508316_. *MASU SON A TALLATAH MUSU HAJARSU KOFA A BUDE TAKE* _TUNTUBI_ 08032773332. *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. 34-35. Baffa na rufe baki, Inna ta yi caraf ta ce "Gara ka jaddada mata don ni a halin da nake ciki da ita, ban ki ka kawar mini da ita a cikin wannan watan ba." 'Dan murmushi ya yi mai sauti tare da cewa, "Anya Salamatu ba gaskiyar Iyah ba ne da take cewa kin fi nan nan da Sumayya?" Da sauri ta ce "Hmm Ni yaushe ma na ga yayar tata bare har na nuna son kan da take korafi? Mafi yawa ai karamin 'da ya fi shiga rai, sai idan halinsa ne marar kyau ko ba ya jin magana". Ya sake fadada fara'arsa ya ce "Ato ni ma dai na ce ban taba ganin wacce ba ta ririta autarta ba sai ke". Da sauri Sa'adah ta ce, "Ai ni Baffa Inna ba ta dauke ni a auta ba, ALLAH ne ya mayar mata da ni auta akan dole." "To ki dinga jin maganar da ake fada miki, ki rage dogon buri, sannan ina sake jan hankalinki akan yaron nan kar ki bari ya kubuce miki." Ta yi kasa da kanta, nuna alamun kunya, a ranta fadi take "Son sa nake sosai Baffa daina jan hankalina" 😀 Sa'ade ke nan. Daga haka ya sallame ta ta mike tana fadin "Sai da safe." Tana zuwa, ta zube kan katifa tana jin wani irin nisha'di na tsirga mata, idonta a rufe wani irin shauki yana mamayar ta. Can kuma ta fara tunanin maganar Baffa in da ya ce, "Shagon aski! Kar dai The Boss barbing shop?" Duk titin ba katon shago irinsa, shago ne da ya samu karbuwa wurin samari yan kwalisa da kullum suke dafifin zuwa gyaran suma ko yin aski. Ashe shi yasa kwanaki ta gan shi agun? A fili ta ce, "Hadadden guy dan boko da yin aski?" A take wani sashi na zuciyarta ya ce mata ai ya huce takaicin bani-bani a wurin iyaye da dangi, ya kuma kere sa'a a tsakanin abokai masu jiran gwamnati ta ba su abin yi. Maimakon ta ji abin alfahari ya yi, ta yabawa kokarinsa na dogaro da kafafunsa, sai ta ji tana jin kunyar ace saurayinta wanzami ne 😁. Washegari da wurwuri ta shirya ta biya wa Zainab Ma'aji, a hanya ta ba ta labarin yadda ta kaya tsakaninta da MK, murna sosai Zainab ta yi tare da cewa "To ki kiyaye abin da ya ce baya so, sannan ki kama bakinki." Duk sa idon su Halima ba su iya gano soyayyar da ke tsakaninta da Malamin nasu ba, saboda yadda suka rufe kofar da za a gane akwai wata alaka a tsakaninsu da ta wuce Malami da dalibarsa. Khalil ne kawai ya kasa gamsuwa musamman yadda ya lura Sa'adah ta yi matu'kar sauya masa, sannan ta toshe duk kofar da suke samu su yi hira, zai mata letter sau goma bai fi ta ba shi amsa daya ba a dukunle. Wannan sauyin da yake gani a tare da ita yasa ya sake kullatar MK yana ganin tun zuwansa makarantar ya canja masa Sa'arsa. Saboda haka ya sake daukar samfurin nuna rashin da'a a gaban Uncle MK, duk lokacin da ya zo ajin sai Khalil ya yi abin da zai harzuka zuciyarsa, wanda hakan ya janyo kiyayya mai tsananin gaske a tsakaninsu, wata rana an fita break ya samu ya yi magana da ita a dalilin ya sa Halima ta tsayar masa da ita, duk tambayar da ya mata idan laifi ya mata ta yafe masa. Ta ba shi amsa da cewa, "Khalil ba ka mini komai ba, kawai ganin jarrabawarmu ta gabato akwai bukatar mu fuskanci karatunmu ne." Kai tsaye ya ce, "Zan so wannan dalilin ya zama shi ne gaskiyar magana, amma na san idan na rantse ba zan yi kaffara ba, cewar akwai wani dalilin ba wannan ba. Ni koma mene ne zan yi ha'kurinsa amma idan wannan mugun Malamin is behind your changes, to ba zan yafe masa ba!" Ya fada cike da 'bacin rai. A tunanin Sa'adah tunda ya turo a ba shi iznin neman amincewarta, an kuma bashi ai zai dinga zuwa zance, sai ta ga an kwashe kwanaki kusan goma bai zo ba, bai kuma sake waiwayar ta ba ko a makaranta, wannan abu na ci mata tuwo a kwarya musamman da a safiyar yau 'yan ajin nasu suka yi laifin da gaba'daya ya zane su, amma da ya zo kanta sai ta ga ya dage iya karfinsa ya zabga mata bulala har hudu maimakon bibiyu da ya yi wa kowa. Abin ya tsaya mata a rai sosai, sai kawai ta tsiri fishi da shi, ya lura da fishin da take yi amma sai ya share, tun ranar da ya gan ta tana hira da Khalil ya ji gabadaya ya rasa inda zai sa ransa shi yasa da ya samu damar dukan yan class din ya ninka nata dukan! Ranar wata Juma'a da yamma Sa'adah na zaune a tsakar gida tana yanke farce ta yi kwalliya da daguwar riga ta shadda purple (Mai ruwan Shanshanbale) a lokacin surfani aikin sama ake ya yi, dinkin ya yi kyau sosai! Innarta sai mita take yi, akan har yau Muutar bai zo ba, ganin Sa'adah ta yi shiru ba tare da ta ce komai ba, sai ya harzuka ta, ta zuba mata ido ta ce, "Iyah ba magana nake yi ba ne kika mini kunnen uwar shegu?" Tura baki ta yi da ya zame mata jiki cikin yanayin tabara ta ce, "Ayya Inna ni ma ban sani ba fa!" A tunzure ta ce, "Kin sani Iyah kawai dai kin nuna masa halin naki ne" "To ni a ina zan nuna masa halin nawa tunda ko a makaranta ma ba kula ni yake yi ba, ni wallahi na fara tantamar shi ya aiko yana so na? Shekaranjiya ba ki ga dukan da ya mini ba." Jikin Inna ya yi sanyi ta fara wasiwasi tana fatan Allah ya sa lafiya, amma sai ta ce, "Allah ya sa dai ba wani abin ba ne." Tana rufe baki yaro ya yi sallama ya ce, "Wai ana sallama da Sa'adatu" Da sauri Innar ta ce, "Je ka ce
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157