Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 121

Chapter 121

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

da ba garinmu daya ba,shi daga Bichi, Ni kuma daga Wudil. A lokacin da Kabiru zai auro uwarka Rabi, mahaifina ne ya zo ya karbar masa, duk da ga kannen mahaifinsa nan hakan ya faru ne bisa amincewar mahaifin nasa da yan'uwansa. Ka san dai kaine dansa namiji na farko amma baisa sunan mahaifinsa ba, sai ya saka sunan yayana da ya fa'da a ruwa ya rasu a shekarar". Ya yi shiru yana goge hawayen da ya kasa maida su, dukkan jikin Mk da 'Karfi ya yi sanyi, da kyar 'Karfi ya ce "Sannu Baba sai a ha'kuri!" Ya saki ajiyar zuciya mai nauyi fiye da ta farko ya zarce da cewa "A bayan mun yi aure har mun haife ku na samu matsala da Zuwaira na yi fishin zuciya na saketa, na yi rantsuwar na gama zama da ita. Bana mantawa dawowar mahaifinka daga Bichi ya samu labarin rabuwarmu a bakin yara, da ya juya Ashe Wudil ya tafi a yammacin, wajen karfe takwas na dare sai gashi ya dawo da ita. Washagari na tashi da azumin kaffara domin bazan iya kunyata Kabiru ba, ko na nuna masa bai isa ya yi hukunci a gidana ba. Har yau din nan ban sake tada maganar ba sai yanzu da nake baku labarin, amma kai sai ka nuna mu iyayenka bamu isa ka mana alfarmar cigaba da zaama da matarka bare kuma wannan abokin naka". Ya ja hankici ya goge fuskar sa ya ce "Har Kabiru ya kwanta dama bashi da aljihun kansa, haka nima bani da nawa, koman mu daya ne, Ina da ikon zartar da hukunci a gidansa haka nima yake da cikakken iko, shiyasa na tsorata ainun hankalina yake tashi idan na kalli al'amarin da ka yi mini, na baka umarni, ka kafe ka kasa yi mini alfarma, sai nake ganin da mahaifinka yana da rai da ka ga 'kwanjina. Amma tunda ni ka'dai na saura muku sai na biku da yadda kuke so tunda ubangiji ya nuna mini wannan zamanin da ya zama iyaye sun koma agwagi." Mk ya ce "Ka yi hakuri, ka kara hakuri Baba" Ya nisa ya ce "na ha'kura amma ka sani ni ba zan iya zuwa wajen Malam Basiru ba, bani da wannan kwarin guiwar, domin har yau din nan girmama ni yake tamkar shakikin yayansa ba kuma dan kowa yake mini hakan ba, illah dan kai domin ni ban san shi ba, sai adalilinka" Hankalin Mk ya sake tashi ya ce " Duk cikin Kano bani da wadda ya fika Baba! Idan kuwa ka ha'kura to kaine mai karba mini aure a ko ina". Alhaji ya ce " ka fadi Gaskiya! sai dai na san daddako irin na Malam Basiru da irin yadda ya girmama lamarinka zai iya tirsasa yarinyar nan ko bata so ya dawo maka da ita dan soyayyar da yake yi maka. Ni kuma na ta'ba fa'da muku kai da ita daya kuke a gurina nine alkalinku, alkalanci na gaskiya zanyi a tsakanin ku. Zan je na nemar maka aurenta kadai, idan na ji a bakin yarinyar da amincewarta zan nema maka aurenta". Da sanyin muryar ya ce "fishi take yi da ni Baba! Amma da zarar anyi auren zamu dai-dai ta, tana sona wallahi" "Ashe dai ta san ciwon kanta, domin kuwa ka yi mata laifin da duk wadda ba ya jin tsoron zuciyarka zai fa'da maka cewa "komin girman laifin da ta yi maka, hukuncin da ka dauka akanta ya yi tsauri, ya wuce makadi da rawa, ko kadan babu a ragayya cikinsa". Jikin Mk ya dinga bari sosai, shi da kansa ya san kunyar Baffah ya jita irin wadda bai yi zaton anan kusa akwai wadda ya ta'ba jin irin wannan kunyar ba. Amma ya tabbatar da ya fito ya fa'di laifin da ta yi masa na cigaba da mu'amala da tsohon saurayinta, da ba wadda zai dora masa irin wannan laifin na bai yi adalci ba, domin munin abin ya baci, ba ta da hurumin yin hakan ta kowacce fuska tunda ba muharraminta bane bata da alaka da shi ta kowacce fuska, sai tsohuwar soyayya. Amma son da yake mata ba zai bari ya fadi wannan al'amarin ba, domin da yawa wasu zasu zargeta, zasu kyamaceta, tunda idan ya ce tana tare da wani ne musabbmabbin rabuwar kowa da abin da zai raya a ransa, ba a kuma isa ace sai kowa ya yarda ba barna suke aikatawa ba, shi yasa ya zabi ya boye a ransa shi ka'dai, amma kuma dole su nisanta da juna tunda ba abin da shaidan ba zai dinga raya masa ba, zai dinga zarginta ne ko da kuwa ba hakan bane a zahiri kasancewar sa dan Adam mai rauni ba a ma'asumi ba". *UZZIRI* *Duba da muna cikin kwanakin nan masu tarin falala da albarka, sai nake ganin ya kamata mu jingine Wannan labarin dan samun damar ribatar kwanakin da ubangiji ya rantse da su, ba lallai mu riski na wata shekarar ba*. *Dan haka zamu tafi hutu sai bayan sallah idan muna cikin rayayyu zamu zo mu karasa abin da ya yi saura in sha Allah. Dafatan ubangiji ya karbi ibadunmu ya sa mu yi hidimar sallah lafiya, kar mu manta da yiwa KASARMU addu'a.* *Ubangiji ya bamu damuna mai albarka*. *Na gode muku sosai da yabawar ku kan rubutuna*. *Surayya Dahiru* ✍️✍️ Surayya Dahiru. ✍️✍️. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 NA *SURAYYA DAHIRU*. •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®️_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ *_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai dai da satar Dukiya._* _*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_ *Barkan mu da ibada! Barkan mu da bikin farin-ciki. Ina fatan ubangiji ya karba mana kyawawan aiyukanmu, ya shafe mana kurakurai. Ina yi mana Barka da bikin Babbar sallah, ubangiji ya dawo mana da Alhazanmu lafiya, ya kuma zaunar mana da kasar mu lafiya.* *Allah ya maimata mana*. 96-97. A tunaninsa space din da ya bayar a tsakanin su, dan ya samu zuciyar sa ta nutsu ne, ta daina wasiwasi akan ta, ashe laifine tunda ba kowa ne yasan azabar da yake dandana adalilin hakan ba. A sanyaye ya ce "shikenan Baba na yarda da hukuncinka zan kuma yi biyayya akansa in sha Allah". Tari ya sarke shi sai da ya lafa masa, ya ce " duk Ranar da kuka dai-dai ta da ita ka zo ka dauke ni, ka kaini gabanta, tunda nema muke yi". Suka yi godiya sosai suka Mike bayan sun ajiye masa kudi. A mota Mk ya ce "Karfi ka ji dadi da dake Ni, duk yadda aka yi dama kana son ka samu damar da zaka dakenin shine yau da Ubangiji ya ara maka dama, ka cire tausayi ka tafka mini bulalar da sai da na ji tamkar na saki fitsari a wurin". Cikin dariya sosai 'Karfi ya ce "Ashe baka iya tsiya ba, da ka saki fitsarin ai kaga dole na yi bi'kin wurin da ka bata, dole kuma na ruga wajen Farida na karbo maka wasu kayan ai ko banza ka wahalar da ni".

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});