Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 18

Chapter 18

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

hutu tare da 'kannen shi. ba musu ya amince, har gida suka zo suka dauke ta, sannan suka dauki hanyar jos kwata, ta yamma da Bauchi😀. Wannan hutun yana cikin abubuwan da Sa'a bata Mantawa da shi, domin kuwa ta yi matu'kar jin dadin zama da 'kannen Idris yadda suka kasance yara kamammu, marasa hayaniya amma kuma yan kwalliya ne na sosai, shiyasa abotar su ta yi da'di. Sumayya kuwa ba ta matsa musu, hatta abinci wadda suke so shi zata ce su yi, mai gidan kuma kusan kullum sai yasa direbansu ya zaga dasu, sunga gari, da wuraren sha'katawa , sannan kuma duk fita sai ya basu kudin kashewa, wadda ba abin da suke siya sai kayan kwalliya ko dai abin da ya shafi sutura. Ba abin da ya dame su illah tunanin mock exam din da suke fargaban fitowar ta, tunda dukkan su set daya suke Amma makaranta daban daban. Haka suka 'kare hutunsu cikin jin Dadi da mutunta juna, da kanshi Idris ya kawo su har gida tare da kayan tsarabar ni'ki ni'ki, barin ma dankalin turawa da dangin su cabbage da Kara's, harta atile kamar wadda za'a ci a tsawon wata. Baffa da Inna sai godiya suke,tare da sake godiya ga Allah, na yadda Sumayya ta sami mijin daya San alheri yake kuma rama alherin da kyautatawa da mutunci. Barinma idan ta zauna tana bawa Inna labarin daular da Anti Sumayya ke ciki, sai dai ta yi murmushi mai nuna yadda zuciyar ta ke cikin farin ciki. Ba zata yi magana ba sai dai ta bige da cewa kema Allah ya ba ki mijin rufin asiri, yasa ki dace kamar na yar'uwarki. Ita kuwa kai tsaye take cewa "Amma fa Inna gaskiya ni bana son irin tsarinsa, ace mutum duk inda matarka zata fita kace sai ta zumbula hijabi har 'kasa, kuma wai dole sai ansa safa? ko 'dan wanne mazahaba ne?" Cikin mamaki Innar ta zuba mata ido, tare da tafa hannu tana sallallami tace "ke kuwa Iyah wannan tsarin da yake yi na martaba shari'a ne bai Miki ba? Na mijin kwarai shi ke kishin matarsa, ya 'dora ta akan ka'idojin shari'a, wadda zasu gudu tare su kuma tsira tare! "Daular da ya sanyata a ciki ta burge ki, kina kuma fatan ki samu irinta, amma abin mamaki, hijabin da Ubangiji ne yace a saka shine bai miki ba? Anya Iyah, Baffan ku bai yi kuskuren barinki shiga wannan makarantar da ta ke sake girmama burinki ba?" Da sauri tace "Haba mana Inna! ni fa ba cewa nayi kar asa hijabi ba, gani na yi tana da tsala tsala dogayen riguna tunda ga kan yan 'kasashen Oman, Qatar, Saudi, Dubai, masu tsadar gaske masu kauri, amma wai dan 'kauyanci kuma sai akawo hijabi a maka, bayan su karan kansu hijaban ne". Ta fa'da tana fashe wa da dariya. Allah ya shirye ki kawai, Inna ta fada tare da mi'kewa ta yi tsakar gida, tana fadin wannan dogon burin na ki yana ban mamaki Iyah. Ban da 'karya da fariya, da kai kanka inda Allah bai kai ka ba, gidan uban wa kika san 'kasashen da suke sarrafa riguna masu tsada? Naga dai ke kam baki da halin samun su, ban da Allah ya miki gata ya baki yar'uwa mai halin girma tana baki kuncen su, wasu ma ko saka su bata yi, ta ke baki, amma har ki zauna ki karkace baki kina min lissafin inda ake sarrafa su?". Ta cika fam saura 'kiris ta fashe cikin turo baki tace "Amma Inna abin har da gori?" Da sauri tace "Eh dole na goranta miki, dan na ga nema kike ki manta cewa ke'din ba yar kowa bace, face malam Basiru mai 'yar tireda😀wadda ko hanyar inda jirgi ya ke sauka ba ki ta'ba zuwa ba, Amma kina bada labarin 'kasashen duniya, wallahi Iyah ki canja wadannan halayen da nake ganin kina sake arowa kina yafawa". Shiru Sa'a tayi amma takaici ke cin ta shikenan sai mutum ba zai fadi ra'ayin sa ba? Sai a hau mishi gore-gore, har a nemi cewa ya raina shari'a? Hawaye ya siraron mata, ta goge ta tashi ta yi 'dakinta, tana fatan Allah ya bata miji mai kula da iyali kamar Idris, amma ba mai a'kidunsa na asalin bahaushen arewa ba. Kayanta na makaranta ta shiga fitowa dasu tunda ga kan uniform, sandal, school bag dukkan su sabbi ne, ta shiga shirya su ta yadda gobe sai dai ta dauka a kammale. Ba tasan meyasa ta ke 'dokin komawa makarantar ba wannan karon? domin kuwa tunda Mk Bichi yaje makarantar ko hutun weekend ne fargaban zuwan Monday take yi. Wata'kila kuma dan ta sami sau'kin kunyata ta da yake yi ne. Amma Kuma duk da sau'kin da ta Sami a bangaren shi, haushin shi da tsanar shi na nan cike a zuciyar ta. kwanukan abincin su ta wanke su tas kafin ta kammala wanke wanken har gawayin ya fara kamawa, dan haka ta cika tukunya ta dora ruwan wanka, tana gama wanke kwanukan, sai kuma ta hau share tsakar gidan hadi da wanke dan matsakaicin bandankinsu, kafin wannan lokaci kuma ruwanta yayi zafi, ta juye ta shiga wanka! bayan ta maida ruwan kunu da ta jefa mishi tsamiya kan wutar. Tana fitowa a wanka innarta ma ta fito tsakar gida, tana ganin yadda Sa'a ta gyare mata gida tsab. Da'di ya kamata na yadda ko kadan Iyah bata da son jiki. Ba zato ta ji anrungumeta tare da cewa "morning Innah" Ture ta tayi tare da cewa "oh ni kam Ina kallo a gun ki". Dariya tayi tare da fadin "Inna gaisuwar kawai shine abin kallon"? Wuceta ta yi tana bude ruwan dake Kan gawayi, ganin yana shirin tafasa yasa ta fara shirin dama kunun, ita kuma sa'a tayi 'daki tana shiryawa. Cikin 'kankanin lokaci da dama kunun, ta kuma dauko fulawar data kwaba a 'karshen dare dan yin fanke, ganin ta tashi sosai yasa ta maida mai kan wutar tana shirin suya, tana kwashe kaskon farko Sa'adatu na fitowa ta shirya amma bata sanya uniform ba. Ganin yadda innarta ke kwaso fanke yayi brown ya tashi sosai, da'di ya kama Sa'adatu. Sai kawai tafara rawa tana juyi tana wa'kar "Mamana, mamana! mai sona, mai tattalin zuciyata". Kwafa Inna ta yi tana fadin "zanga sadda za ki girma Iya" "Idan Kinga na girma sai kin haifa min 'kani ko 'kanwa". Ta wuce ta dauko, kofi da plate tana fadin "Allah Inna Ina son 'kanne gashi Anti Sumayya tayi min nisa bare na dinga debo su Khalifa". Ta fa'da cikin muryar tausayi tamkar hakan zaisa innar ta haihu yanzu yanzu. Numfasawa Inna ta yi sannan tace "Ai kin kusa samun 'ya'ya ma indai kina da rabo, ba'di iyanzu ai kina dakin ki ". Daure fuska tayi, sannan tace "Nifa sai na fara karatu". Da sauri Inna tace "Inma karatun za ki zama sai dai a dakin ki, tun yanzu kina ruwan ido kowa ya zo kice ba kya sonsa, amma kuma kina son duk wani abu da zai 'kullo ya baki". Mi'kewa ta yi bayan ta debi kunu da fanken tana cewa "To Inna ai ba ro'konsu nake yi ba, Kuma Annabi yace ba kyau mai da hannun kyauta baya"

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});