Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 89

Chapter 89

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,195 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kun mayar masa da 'ya Bazawara? kaico na taya ku jin kunya". "Yanzu ku tashi ku kaini gurin Alh Isa". Sai da Mahmoud ya taimakawa Mk sannan ya mike. Fada sosai Mk ya sha a gurin Alh Isa, sai daga karshe ya sassauta ya ce " Ka yi kyan kai da ka yi saki 'daya tal, fatana ka janye ka mayar da matarka, kowa hakuri ya ke yi da abokin zamansa ,ta ci darajar mahaifinta". Kan Mk na kasa baice komai ba sai da Baban ya kammala sannan cikin ladabi ya ce "A mini afuwa Baba, a yi hakuri, a sani cikin addu'a ina cikin ru'dani mai yawa, ina rantsuwa da ubangiji ina cikin ru'danin da nake jin inama ajalina ya riske ni a yau saboda tsananin asarar da nake jin na tafka, ba yadda zan yi ne, abin ne ya fi 'karfina" Dukkansu jikinsu ya yi sanyi mussaman yadda yake maganar cikin rawar murya tamkar ba Mukhtar ba, namiji mai karfin zuciya. "Allah ya daidaita ya kawo mafita " cewar Alh Isa da ya rasa mai zaice, dan ya lura Mukhtar na cikin rashin nutsuwa da firgici, ya tabbatar kuma yana da gaskiya, sannan mai 'daki shi yasan inda yake masa yoyo. Dukkansu suka amsa da "Ameen, ya yin da Hajiya ba haka ta so ba, so ta yi ya wula'kanta mata shi, ya kuma tirsasa masa ya mayar da matarsa ko ba ya so. Har da Alh Isa suka 'dunguma zuwa gidan su Sa'a, Hajiya ce kawai ta ce ba zata je ba, bata san da idon da za ta kalle su ba. A tsakar gidan Baffa ya jagorancin zaman, Alh Isa ne ya yi karfin halin bayyana mutuwar auren wadda ya matu'kar dukan zuciyar iyayen na Sa'adah, juyin duniya ba wadda ba'a yi musu ba, amma sun 'ki bayyana menene dalilin da ya haifar da wannan tashin hankalin, kukan da Sa'a ke yi tamkar za ta shi'de ya sake 'daga hankalinsu. A hankali Mk ya ce "Baffa Ina rokon ka, kar yanke mini kauna, ka yafe mini, kaddarar muce ta zo da hakan, har wayewar garin YAU bamu san zamu tsinci kanmu a cikin wannan mawuyacin HALIN da muke ciki ba, ina kuma fatan itama ka yafe mata, ba laifinta bane Baffah". Gurin ya yi tsit sai shshshekar kukanta kawai ake ji, Mahmoud ya kamu da ciwon tausayin masoyan biyu, mussaman Sa'a kallo daya za ka mata kasan tana cikin tsaka mai wuya. Baffa ya nisa ya ce "Ba aurenta ne ya hadamu ba Mutari, ba kuma zai zama dalilin rabuwarmu ba, nasan halin girma irin naka, tsiyar a gunta take, yanzu kuma zata gane tsiyar har wasali gareta, domin na tabbatar laifin nata ne, ba zata 'ki zaman aure ta yi tunanin zata zauna a gabana ba". Ga mamakin Mk sai ya ji kalaman Baffa sun sake girgiza masa zuciya. Da sauri ya mi'ke ya koma kusa da shi ya ce "Baffa Dan Allah dan Annabi ka yi ha'kuri, idan ka yi haka bazan yafewa kaina ba, ka yiwa Allah ka barta ta ji da tashin hankalin da na jefata, ba laifin ta bane, nawa ne, Ni za ka hukunta ba ita ba". Ido kawai Baffah ya zubawa Mk da yake gurfane a gabansa yana rokonsa idansa jawur, ga wata irin rama da ya yi ta farat daya. A ransa fadi yake Iyah kin tafka asara, kubucewar miji irin Mutari abin ki shimfi'da tabarma azo a miki jaje ne. Ya tabbatar laifin na Iyah ne, amma ya 'boye laifinta, ya kuma tsaya kai da fata wurin nema mata sassauci da aminci a gurinsu. Baffa ya dafa kan Mk ya ce " Madallah da mutanan kirki irin ka, madallah da mutane masu irin dabi'ar ka, madallah da zuciya mai adalci irin ta ka! Saboda kai zan bar Iyah ta zauna a gidan nan, ban taba jin takaicin rashin ya'ya da yawa ba sai yau, da ace Ina da wata 'yar! da wallahi taron nan bazai watse ba sai na musanya maka da ita". Kwalla ta 'kwacewa Mk ya na jin kunya da tausayin Baffa na sake masa rubdugu, wacce irin kauna ya ke masa haka, anya bai yi rashin kirki da ya kasa yin ha'kuri da 'yarsa ba?" Ba zato suka ji Mk na cewa "Baffa me yasa ba zaka ba ni umarni na mayar da ita ba, sai ka yi fatan ka bani yar'uwarta idan hakan ya yiyu ka haramta mini ita gaba'daya fa?". Ba ki 'daya jikinsu ya dan yi karfi saboda kalaman Mk, wadda suke bushara da zai iya daidaitawa da matarsa, yanzu ko anjima. Inna ta ce "Tunda baka da wata da za ka bashi, ai sai ka mayar masa da wadda ka ke da itan". Cikin kuka sosai Sa'adah ta ce " Na gode Innah". *Surayya Dee* ✍️ 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 NA *SURAYYA DAHIRU*. •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ *_Doka mai lamba ta 68 ta nuna cewa satar fasaha babban laifi ne da yake dai da satar Dukiya._* _*A guji taba wannan labarin ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.*_ *Gaisuwa da fatan alheri ga wadannan groups din* *LAFAZEE FANS* *DANDALIN MUM KHADY* *HAFSAT SODANGI fans* *DAGA DAJI 1&2 fans* *PAID GROUP na BINTA ABBALE* *DANDALIN SADA ZUMUNTA NA ANNURI.* *JIDDA REAL FANS* *FADILA LAMIDO FANS* *SADNAF NOVELS GROUP* *TASKAR AISHA MICHIKA* _*Dama sauran wadanda ban ambato ba, mu hadu a shafin gaba, Kuna da yawa Allah ya bar kauna_*. *MK, SA'A DA FARIDA NA GAISUWA* *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. 79_80. "Ba zan ba ka umarnin da na san kunya da nauyi ne zaisa ka yi shi ba. Ba ni na maka umarni ka auri Iyah ba, ku ka hada kanku, ka aureta bisa ra'din kanka, ka zauna da ita cikin shekaru bakwai, Ni da mahaifiyarta shaida ne akan kyakkawan rikon da ka mata, haka nan, ka na girmama mu da dukkan zuciyarka, kana jin nauyi na tun kafin na baka aurenta, idan har za ka iya sakin Iyah, to ni kuwa bazan yi son zuciya ba, na tabbatar abin ne ya fi 'karfin ka". Ya nisa ya cigaba da cewa "Zan so kwarai ace na mutu na barta a hannun ka, domin Ina da yakinin ba za ta wulakanta ba, amma ya na iya da HALIN 'dan YAU mai yin aiki da son zuciya, daga baya kuma ya jinginawa tsautsayi da 'kaddara". Alh Isa ya muskuta ya ce "Tun kafin mu zo nan, na umarceka da ka janye, ka mini gardama, amma yanzu kana cewa ya baka umarni ka mayar da ita, Ni baka jin nauyi na Mukhtar?" Kunya iri iri ta sake rufarwa tashin hankalin da Mk ya ke ciki, a sanyaye ya ce " A a Baba bayan nauyin ka da nake ji, wallahi kallon uban da ya isa ya zartar da hukunci akai na na ke maka! Abin da yasa ban amsa ba, ina jin tsoron kada na mayar da ita a yanzu auren ya lalace gaba daya, saboda zuciyoyin mu cike suke da bacin rai mai ya.." Cikin dimaucewa Sa'adah ta katse shi da cewa "Ni zuciyata ba komai sai

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});