Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 73

Chapter 73

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

cigaba da aikinsa amma bashi da sukuni ko kadan, ya kuma yi al'kawarin ba zai ce ta daina kukan da take yi ba. Aikuwa kusan raba dare ta yi, tana masa gunjin kukan da babu shagwaba, sai zallar bacin rai, irin kukan da me yinsa yake son a rarrashe shi, lura da hakan da yayi shikuma ya yi biris da ita, dan kuwa bai ga dalilin kukanta ba, shi ta musganawa, ta masa rashin kunya, bata bashi hakuri ba, shine take sa ran shi ya risina mata, lokaci ya yi da zai daina biyewa son zuciyar sa akan lamarin ta. A inda take zaune barci ya sureta, sai sakin ajiyar take yi. Sai da ya gama aikinsa, ya kammala komai, ya dauko Jawad ya kwantar da shi, ya dauko bargo ya lulluba mata, sannan ya kashe fitila ya kwanta bayan ya rungumo Jawad a jikinsa. Da asuba ta tashi ta ganta lullube da bargo, ta ji dadi, sai dai rashin tashinta ta yi sallah ya dakushe waccan jin dadin, ta kalleshi har ya dawo daga masallaci, ta zuba masa idon da ya kumbura saboda kuka, murya a dashe tace "Malam abin har ya gagareka tashina na yi sallah?" Ya yi mata shiru tamkar ba da shi take yi ba. Takaicinsa ya sake kumeta, tace "Ma'aiki dai yace Allah ya jikan mijin da ya tashi cikin dare ya kuma tashi iyalinsa suka yi sallar nafila, to ina kuma ga wadda ya tashi, ya kuma tashi iyalinsa dan sallar Farillah? ka rasa wannan ladan, ba nice da asara ba". Ya zuba mata ido yana kallon ta, Yana jin sabon tashin hankali na shigarsa, tabbas ta kerewa tunaninsa, an mata famfo fiye da duk yadda yake zato. Haka ta gama sakin magaganu sannan ta fita zuwa dakinta, don yin sallah. Kan Mk ya kulle, ya rasa mai zai mata, ya yi fushin, ya bagarar da ita, Amma duk a banza, wai ya zai mata ne? kawai sai ya tsinci kansa da daga hannunsa sama yana cewa "Allah kasan irin son da nake yiwa Sa'adah, Allah ka shirya min ita, ka bude kirjinta ta gane gaskiya, ta fahimci bani da nufin zaluntarta, ka zaunar da mu lafiya, Allah ka kara min ha'kurin zama da ita cikin adalci". Ya kishingida yana tunano kafin shigowar su Halima cikin rayuwar aurensu, ko ya ya taga ya canja mata, ta dinga tambayar me ya same shi, ko itace ta masa laifi? Ta dinga bashi hakuri kenan, ko yace bata masa komai ba, kawai yanayi ne, ko baya jin dadi ne, duk da haka hankalin ta baya kwanciya sai ya dawo da walwalarsa, amma a yanzu kusan sati uku suna dauki ba dadi, amma kullum da abin da zata yi da zai sake bakanta masa Rai, karon farko da ya fara zargin Anya kuwa dama Sa'adah da gaske tana sonsa? Ya dinga hasaso yadda yake gudun zuciyarta, har wasu da yawa suna ganin tsoronta yake ji, alhalin ba haka bane, kawai tsananin sonta da yake yi ne, yasa baya shiri da duk abin da zaisa ta koka, mussaman na rashin wani abu, zai ha'kura da dukkan bukatun kansa, matu'kar ita zata wadatu. Amma duk su Safina sun lalata mata tunani, sun jefa mata shubuha, wai yan mata ne da shi na banza! Tabbas suna neman raba shi da ita ne. A fili ya furta " Allah kana ganin masu son shiga tsakanin aure, Allah ka min maganinsu". Sai da ya isa makaranta! Ya na cikin motarsa ya ciro wayarsa, ya lalubo lambar Anty Sumayya, cike da girmamawa ya gaisheta, sai kuma ya yi shiru ya na jin nauyin zartar da kudiransa. Jin yanayinsa yasa ta tambayarsa ko akwai matsala ne? Cikin jin nauyi ainun yace " So nake ki yiwa Sa'adah magana, mun dade cikin rashin nutsuwa, na yi iyakacin kokarina dan mu fahimci juna abin yaci tura, bana son na tayarwa da su Baffah hankali". Hakuri Sumayya ta dinga bashi, tare da al'kawarin yanzun nan zata kirata. Kai tsaye yace "ba waya a hannun ta". Jikin Sumayya ya sake mutuwa, shiyasa kwana da kwanaki tana gwada layin Iyah baya shiga, ta damu kwarai da rashin jinta, sai da Inna tace mata, lafiya ce take buya, Ni kaina an kwana biyu bamu gaisa ba, da kuma wata matsalar ce ai da mun ji, tunda mijinta kusan kullum sai yazo unguwar, kowacce juma'ah kuma zai shigo ya gaishe ni, ya bar Jawad sai zai tafi ya zo ya dauke shi, na fahimci Iyah! indai naji ta shiru haka, to cikine da ita. "Yanzu kana gida ne?" Ya girgiza kansa tamkar tana ganinsa "Ina makaranta, sai da yamma zan koma". Ai kuwa da yamma yan isa gida ba jimawa, Kiran Sumayya ya fado wayarsa, bai dauka ba, ya bawa Jawad wayar tare da cewa" sauri ka kai mata, Maman Gombe ce" dake tuni sun bar Jos tun shekaru biyu da suka wuce. Da gudu kuwa Jawad ya fita sai dai kafin ya isa inda take ya danna ok, ya fara yiwa Sumayya surutu, ita kuma ta biye shi, duk da ba komai take fahimta a hirar tasa ba. Fada sosai Sumayya ta yiwa Sa'adah, ta yi shiru tamkar tana jinta, sai da ta gama ta saka mata kuka tana fadin "Yana zaune da yan'uwansa kalau, amma ni yana ba'kin ciki da hadin kan dake tsakanina da ke, Ina zaune da shi ne kawai, amma ba irin wulakancin da baya mini, ya fifita farin cikin yan matansa akaina, ya koyo wata dabiar da ba tasa ba, ko kukan jini zai ga inayi ba ruwansa, shine har ya kawo karata?". Mamaki ya kama Sumayya tace "Ni kike fadawa wadannan maganganun? Eh na tabbatar Mijinki ba karamin ha'kuri yake da kaifin harshen ki ba, amma ki saurare ni da kyau, wlh idan baki canja ba, za ki jefa kanki a nadama mai yawa, wato ke har yanzu baza ki yi hankali ba? Kowacce mace da akwai inda take ha'kuri, ance miki auren wasa ne, ke naki ma wallahi ba matsala bace, kawai dorawa kanki kika yi, Ina ruwan ki da yanmatansa, ko aure yace zai kara Ina ruwan ki? Tun zuwan ku Jos na lura sai kin koya masa bagarar da lamarin ki". "Dan ke mijinki ba mai hayaniya bane, ba mai kule kulen mata bane shiyasa kike ganin bani da matsala" Sa'adah ta fada a tunzure. Cikin bacin rai sosai Sumayya ta ce "shikenan ki yi duk abin da kike so, ya dauka ina da wata kima a wurin ki! shiyasa yake ganin zan iya muku sulhu basai iyayen mu ba, amma tunda ban isa ba shikenan! Rayuwarki ce, kina da ikon yin duk yadda kika so, sai dai ki sani wadda bai ji bari ba, ba zai ki ganin hoho ba". daga haka ta kashe wayar ta, ta bar Sa'adah ri'ke da waya tana kunshekin kuka. Jikinta ya yi sanyi, tana Jin Aunty Sumayya uwace ta wuce ta yi misayar yawu da ita! Dan haka sai ta sake kira, Sumayya ta daga tana cewa "menene?" Cikin kuka Sa'adah tace "Na ji! kiyi ha'kuri". Sumayya da bata da zafi, tace "yauwa Iyata, ni nasan indai a cikin Innarmu kika fito ba zaki 'ki jin abin da na fa'da miki ba, saboda kinsan nan

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});