Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 152

Chapter 152

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ya kamata ta fara tarewa, tunda itace suke tare, bai kamata ace ita zata je ta tarar da Sa'adah ba, shikuma ya yi hakan ne dan ya tabbatar da Sa'a ce uwargida ba dan wani abin ba. Amma sai ta ce "Allah ya Sanya alkhairi". Ranar laraba aka gama shirya komai na bangaren Sa'adah! duk inda tsari da haduwa wurinta ya kai, a ko ina kuwa, ba kananun kuda'de aka fitar ba. A ranar dai ta laraba Sa'a na zaune a tsakar gidansu ba hijabi a jikinta adalilin Inna ta je unguwa, ba zato ta ji sallamar Innar a tsakar gidan. Gabanta ya yanke ya fa'di, ta hau dube duben Hijabinta ashe a 'daki ta barshi. Zabura da waige-waigen da take yi ne ya ja hankalin Innah ta tsura mata ido, take ta gano abubuwa masu yawa da suka sauya a tare da Iyah. Kirjinta ya matu'kar cika, sannan ta yi fari ta 'dashe tamkar mai shafa man bleaching, sanin da Innah ta yi duk kwalliyar Sa'a bata yarda ta canja launin fatarta ba. Ta kalli fuskarta tana ganin yadda ta 'danyace, alamun dai mai shigar ciki 'karara. Dabas Innah ta zauna tana hirji. Ta jima tana kokawa da numfashi, sannan ta ce "mafarkina ne zai tabbata Iyah, ko kuwa yanzun ma mafarkin nake yi?" SURAYYA DAHIRU ✍️✍️. 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 *NA* *SURAYYA DAHIRU*. *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ 113-114. *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR*. *PROLOGUE*. *Masoyan FARIDA*! *Team FARIDA na so na ambato sunanku, sai na gane yawanku ba zai bari ba, Farida tana sonku, tana yaba muku, Ta ce na ce muku son so Fisabidillahi*.🥰 *MARUBUTA* *Hajiya Saliha A.A Zaria* *Hajiya Hafsat Sodangi*. *Hajiya Maimuna Beli* *Aunty Sumayya Takori*. *Hajiya Zulaihatu Sani Kagara* *SADIK ABUBAKAR*. *Fadila lami'do*. *Binta Abbale*. *Hassana 'Danlarabawa* *Maman Mama*. *Ayusha Muhd* *Kulsum Baffah Azare* *Umm Azghar*. *Gidan Iko* *Asiyah(asi beauty)* *Aisha jos* *Hafsat Bature* *Rabi'atu Shitu* *Aysha Dansabo*. *Da dukkan yan kungiyar lafazi writers da ma sauran marubuta gaba'daya* *Ina godiya sosai tare da fatan alheri.* *Allah ya 'kara Basira.* *Da* matu'kar kunya Sa'a ta ce "wanne irin mafarki kike magana Innah?" "Kul kika yi mini iya-shege Iyah! Ai kin san dai mai nake nufi, mike tsaye na ganki soasai". Ta 'ki mikewa sai 'boye jikinta da take yi. Salati sosai Inna take tana cewa Ni dama na da'de ina mamakin yadda aka yi kika sauko har kina nuna zakuwar ki akan ki tare, dan munafunci har kina cemin wai saboda ra'ayina zaki ha'kura ki tare ko ba kayan daki, ashe ke kin tare ma kawai ankara ne ban yi ba. To yanzu sai ki fa'da mini lokacin da kuka kunsa cikin dan asan ko auren na ku bai yiwu ba." Da rawar murya Sa'a ta ce haba Innah yanzu sai ki yi tunanin zan iya yin wannan ta'asar?". "To ina zan sani tunda daga ke har Muutar din ba mutunci ne da ku ba , bare kunya. Wato shiyasa kullum sai kin san yadda Kika 'kirkiro fita, ko dai da sunan zuwa gurin aiki, ko wani uzzirin da ba za'a hana ki fita ba? Oh ina zaune anmayar da ni garmaho, ko a dakin nan kuka yi abin da kuka yi?" Kuka Sa'adah ta saka, tana jin wata irin kunya tamkar ta tsaga kasa ta shige. Ta kasa magana, tana jin haushin Mk da ya janyo mata wannan muzantar a idon uwarta. Ana cikin hakan Baffah ya shigo ya ce "me ya samu uwata take kuka har da hawaye ne?" "Kukan iskanci take yi, ba dama ta yi ba dai-dai ba, ayi magana sai ta bare ja'irin bakinta ta yi kuka tamkar yarinya kankanuwa." "Me ta yi da ba zaki iya hakuri zuwa jibi ta tafi dakinta, itama hankalinta ya kwanta ba?" "Hmmm! ciki ne da ita, daga na tambayeta yaushe suka yi cikin dan asan matsayin aurensu shine take wannan gunshekin kukan tamkar na daketa ne, ke kam wallahi kin ji kunya, ba dan ni na haife ki ba, da tuni ki ba'kanta ni a idon duniya". Kunyar da Sa'a take ciki ta sake nunkuwa, dan haka ta sake 'kara sautin kukanta dan ta kawar da su daga sake kunyata ta. Aikuwa dai Baffah ya ce "To ai a hankali zaki bita, ni na gasgata Iyah ba zata kunyatamu ba, ba ta yi shashanci a 'karancin shekarunta ba bare a yanzu da ta yi hankali, na kuma shaida Mutari ba zai ha'ince ni ba". Wani irin farin-ciki ya kama Sa'adah tana gasgata Mk da ya ce Baffah Babansa ne ba nata ba. Innah bata gasgata ta ba, amma Baffah ya shaideta ba zata yi Zina ba, haka ya shaidi Mukhtar ba zai lalata masa 'yah ba. Kuma hasashen Baffah shine gaskiya. Kawai Innah mafarkin da ta yi ne, yake sata wasiwasi. Ya sassauta murya ya ce "Yi shiru ki mini bayani" Ta kasa cewa komai saboda tsananin kunyar da ta tsinci kanta a ciki. Ya juya ya fita yana cewa yanzu nan na hango shi ya zo unguwar bari na ji daga bakinsa. Ganin Baffah ya fita! Ya saka Inna cigaba da sababinta, "munafukar banza, kika dinga cika bakin ba kya sonsa, kika yaudarar da ni da cewa ba zaki tare babu kayan daki ba, ashe kina zagayewa kuna abin da ranku ya so, saboda tsananin fitina da rashin kunya" Daga ganin yadda kika aune, ansan ciki ya kwana biyu a jikinki, yo ina ganin HALIN YAU ni Salamatu!". Sa'a ba baki sai kuka. Baffah kuwa shagonsa ya 'kira Mk. Cikin nutsuwa sosai ya ce "Mutari ka ce mini jibi juma'a Iya zata tare?" Kai tsaye ya ce "Eh Baffah". Ya numfasa ya ce "yanzu na shiga gidan na ji wani irin al'amari da ban fahimice shi ba, na tarar da Iyah da gyatumarsu a halin 'bacin rai saboda ta fahimci tana da juna biyu". Mk ya mi'ke da sauri , zuciyar Baffa ta buga a tunaninsa kaduwa ya yi da jin maganar saboda ba shi da alaka da cikin. Da azama Baffah ya ce "Ina zaka? Nutsu ka saurare ni, baka da alaka da cikin da yake jikinta ne?" Ya koma ya zauna ba kunya ya ce"Haba Baffah! Ni fa zaburar da na yi, zuwa zan yi na fahimtar da Innah ta daina yi mata fa'da, Ni zata yiwa, tunda nine Babba! Domin na san kai zaka shedi ne ba zan yi lalata da jininka ba! Amma sai na ji kana tambayar ko bani da alaqa da al'amarin. Kawai ayi ha'kuri Baffah! Abin da za a kallah a samu nutsuwa matatace, na kuma shaida akan ka'ida komai ya faru". Hankali Baffah ya kwanta sosai ya ce "To Allah ya rufa asiri". Mk ya mi'ke yana cewa "Yau ba doguwar hira Baffah na ji kunya ba ka'dan ba". Murmushi Baffah ya yi tare da cewa "ja'iri da kana jin kunya da baka yi abin da ka yi ba". Ya rufe shago ya koma gidan ya tarar har lokacin Innah na zubawa Sa'a sababi da gorin ta ji kunya, ta yi ciki a gida. Ita kuma sai kuka take yi tana jin takaicin abin da Mk ya janyo mata.

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});