Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 9

Chapter 9

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,207 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

a ranshi yanzu, tunda akan kunnenki Baba direba ya tabbatar da shi kanshi ya fahimci irin son da yake miki, ke ma kuma ya lura kina son shi, haba Sa'adah!" Kukan da Sa'adah ke ma'kalewa ya kwace mata sosai, har Zainab ta ji to ko akwai wata magana data fada cikin kuskure wacce tasa ta kuka haka? Amma da ta tuna Sa'adah sarkin kuka ce ko ba dalili, yasa ta samin nutsuwa. Shiru ta yi, ba ta yi yunkurin hana ta kukan ba, ta san ko ba komai dai za ta sami salama a zuciyarta, sai da ta tabbatar ta yi ya ishe ta sannan ta ruko hannunta tana fadin ya isa haka, ki yi hakuri komai zai wuce ya zama tarihi, ki yi addu'ar zabin alheri, bawai zabin ranki ba." Ta mike tana cewa, "Kin ji har ana kiran Maghrib bari na tafi sai na sake shigowa, ko kuma sai na gan ki." Sa'adah ba ta ce mata uffan ba, ita ma Zainab din sanin halin 'kawarta tun fil'azal yasa ba ta damu ba. Ta juya ta fita, a tsakar gida ta tarar da Inna ta goya Khalifa ya nata barci, "Ah goyo ki kayi haka Inna? Ai sai yasa miki ciwon baya." Murmushi Inna ta yi tare da cewa, "Ku dai yaran yau da bakwa son goyo ne kuke kallon zai sa ciwon baya, alhalin shakuwa da tausayi ke 'karawa a tsakanin uwa da danta, amma ku boko da gayu ya hana ku goyo sai dai a hannu" Dariya Zainab ta yi tana fadin "Inna Allah ina 'ko'kartawa." "Allah Ya sa!" Inna ta fada tana kunto shi, yaro yasa kuka, wai shi an saukko da shi, ai ko Inna ta ce, "Juyo na sa miki shi a bayan." Cike da kunya da girmamawa tace, "To" Ta sunkuya ta sa mata shi har zanin Inna ce ta daura mata, sannan ta bar ta ita kuma ta hau kiciniyar gyara goyon. A gurguje suka yi sallama ta tafi ita kuma Inna ta yi bandaki da buta a hannunta. Ta idar da sallar Maghrib tana zaune kan sallayar tana jan carbi, wayarta ta hau 'kuwwa, hannu tasa ta janyo ta ganin sunan Hajiyar Bichi, yasa gabanta ya fadi, duk da suna waya lokaci zuwa lokaci, amma ba tasan dalilin faduwar gaban da ta ji a yau ba. katsewa ta yi sai ta kira ta, Hajiya ta ambata sai kuma tace, "Assalamu alaikum!" Ciki-ciki Hajiyar ta amsa. Sai jikin Sa'adah ya yi sanyi ta ce, "Lafiya kuwa Hajiya?" "Ba lafiya ba Sa'a, yanzu a ce za ki tafi wurin Jawad amma ki kasa fada mini? Na san kuma kinsan ubansa baya nan?" "Hajiya ni ban sani ba". "kin sani mana ai ba zuwa kike ranar da ake taron ba, amma wannan karon kin je saboda wanda kike gujewa haduwar ta ki da shi ba zai jeba, sai kuma Allah ya yi nufin haduwar taku wanda shi kadai ya san manufar hakan. Ban ga kuma laifinki don kin kame kanki ba. Laifinki daya da kika san dukkan ahalinki ba za su sami zuwa ba, sai ki fada mini mu tafi bibbiyu, wannan abu da kika mini sai nake ganin kamar ni ma fushin da kika dauka ya shafe ni ganewa ne ban yi ba sai yanzu." Cikin son kare kai da kuma iyakacin gaskiyarta tace, "Wallahi ko ka'dan Hajiya ba haka ba ne, ba abin da za ki mini nan duniya na yi fishi da ke, har gobe ke uwa ce. Tunani na bai ba ni na yi hakan ba, na ma yi tunanin direba zai kai ku tare da Antinsa, amma ki yi ha'kuri Hajiya" Take ko Hajiyar ta ce, "Na huce dama rashin fahimta ne, ki gaida Innar taki, kuma In sha Allah ina nan tafe cikin satin nan" "Allah ya kawo ki Hajiya!" Ta ajiye wayar tana jin idan akwai asarar da ta yi cikin rabuwa da MK to kuwa rashin nagartatciyar suruka irin Hajiya na kan gaba, jin kanta ya mata nauyi ne yasa ta ci gaba da ambaton Allah. Alkalamin SURAYYA DAHIRU ✍🏼✍️ [5/15, 19:03] +234 806 791 2288: 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.} https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ *SADAUKARWA GA* *SADIQ ABUBAKAR*. *ALLAH KA JIIKAN* _HAUWA M. HASSAN_ *(FINE GIRL)* _UBANGIJI KA ALBARKACI SU FA'EEZA_. 13-14 Tsawon kwanaki addu'ar za'bin alheri ya dinga yi tsakaninshi da Sa'adah ba 'kak'kautawa, kuma ALHAMDULILLAH, ya ji takurar da yake ji akan zama da ita ta kau, ya sami sau'kin nauyin da zuciyarshi ta yi akan ta. Ranar Juma'a bayan an sau'ko Masallaci kai tsaye gidan su ya zarce kamar yadda ya saba a falo ya tarar da Hajiya zaune kan sallaya, tana lazimi. Ya jima yana zaune kafin ta shafa addu'arta ta juyo ta kalleshi, a nutse ya shiga gaishe ta tare da tambayar jikinta kasancewar kwanaki biyun nan fama take ta yi da zazzabin cizon sauro. "Jiki kam na ji sau'ki sai rashin 'karfin jiki wanda sai a hankali." Ta fada tana daddanna 'kafarta. "Hajiya 'kafar ciwo take miki ne?" Ya fada cike da kulawa. Ta ce, "Ba wani ciwo kawai kasala ce!" "Sannu idan kin gama shan maganin ba ki ji daidai ba, sai na mayar da ke wajen likita." Da sauri ta ce "Kai raba ni da zancen Likitan nan na ji sauki." Dariya ya yi! dama tsokanace wannan zazzabin ma da 'kyar ta yarda ta je asibitin bare ta yarda ta koma. "Har yau ba ka ce mini komai akan maganar Sa'a ba?" Murmushi ya yi "Oh! Hajiya ai na ga ba ki da lafiya ne." "A a na ji sauki " Gyara zama ya yi sosai ya fuskance ta, "Hajiya!" Ya kira sunanta. "Na'am!" Ita ma ta amsa tare da mi'ka dukkan natsuwarta gare shi. "Kamar yadda na ce miki zan yi addu'a, to na yi! kuma na ji tsoro da razanin da nake ji a tattare da zama da yarinyar nan ya gushe daga zuciyata, amma..." Sai kawai jin ta ya yi tana ambaton Alhamdulillah! tausayinta ya kama shi na ganin tsananin murnar da take yi akan abin da ba tabbacin yi yuwar faruwar shi. Ya san Sa'adah, ta kyautata mata matu'ka. Lamarin da Hajiya ta tattara dukkan kaunar da take mishi ta mi'ka mata, duk irin laifin da za ta mishi tofa a idon Hajiya ba laifi ba ne sai ta ce ai yarinya ce, 'kuruciya ce ba kuma hankalinsu 'daya ba. Har ya fara yi wa Sa'adah kallon macijiya ta sare shi, ta kuma koma gefe ta lullube uwarshi da alheri, haka nan hatta 'yan uwansa, mussaman Samira da Hafsatu basu dauki lamarin Sa'adah da wasa ba, saboda yadda ta kyautata musu iyaka, ya san ba ta da rowa, tana da saurin sabo, ba ta kuma sa ido a lamarinsa da 'yan uwanshi, komai zai musu kuwa, wani lokacin ma ita take ankarar da shi. Shi har mamakin ta yake yi yadda duk wani rikicinta, fa'danta, rashin kirkinta, da kuma rashin ha'kuri duk akan shi ya 'kare. Ta 'dago tana kuma ambaton ALHAMDULILLAH. "Hajiya abin da nake so ki gane yarinyar nan fa yanzu gaba'daya ba yadda kike zaton ta ba ne, na tana son dawowa 'dakinta,

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});