Chapter 46
Chapter 46
halinta na son kayan 'kawa. Hatta kayan fitar biki masu kyau aka tanadar mata shike nan sai hankalinta ya kwanta. musamman da Sumayya ta ha'kur'kurtar da Baffa ya yarda za a kai mata gadonta 'kirar Dubai. Kafin ranar 'daurin aure gidan amarya ya fito fes komai ya ji, Sumayya ta yaba 'kwarai da kokarin MK da iyayensa, saboda haka sai ta sa aka mayar da gadon dake dakin MK zuwa dakin dake cikin falon wanda babu komai a ciki, shi kuma aka saka masa hadadden gadon Dubai. Kicin aka sake 'kawata shi da tsirarrun kayan alfarma, aka rufe gidan ana jiran isowar TV da Fridge da kuma amarya! don Mk tuni ya tare a cewarsa gadi yake yi.😁 *05/06* Ranar aka daura auren Mukhtar Kabir Bichi da Sa'adatu Bashir Gogel, a Masallacin Sahaba dake Kundila, kamar yadda Baffa ya ce ba za a yi party ko ka'de-ka'de ba hakan ce ta kasance. Amma kuma ya tsaya an yi abincin 'daurin aure da yini na fitar kunya, duk wanda ya halarcin auren Sa'adah mace ko namiji ya ci abinci mai rai da lafiya don kuwa Bijimin sa Baffa ya yanka, duk tanadin Baffa a shirya abincin fita kunya ya kare. A lokacin sarkar gold din dubu hamsin babba ce, ita ya siyawa amarya da shawarar Sumayya da take ta 'koda irin kokarin da MK da iyayensa suka yi. Sai kuma 'dinkunan da ya mata na kwalliyar amarci. A Daren da aka daura aure suna zaune a gabansa ita da Sumayya da mahaifiyarsu, bayan ya yi addu'a ya ce, "Duk wani burina a yau ya cika Iyah, ina kyauta zaton na dan'ka ki a hannu na gari don Allah ki bi mijinki, nasan kinsan idan mijinki, ya yarda da ke to Ubangijinki ma ya yarda da ke, idan kika ri'ke wannan kadai za ki gane komai za ki yi a 'dakin mijinki ibada ne. Ibada kuwa sai an daure domin za ka ci karo da abin da kake so da wanda ba ka so. Na ro'ki ki yi koyi da yar uwarki wurin boye sirrin aurenta, har yau din nan Sumayya ba ta taba fa'din ga laifin mijinta ba, mun sani ba fa don ba ya mata laifin ba ne, haka shi ma yana ri'ke da ita cikin ha'kuri da girmamawa. Ina sake miki nasiha ki zama mai ha'kuri, baki da'yan aure wallahi hakuri ne ya fi yawa, ina fatan ki yi ko yi da mahaifiyarki wurin ha'kuri da biyayyar aure!" Ya janyo ledar dake gabansa ya fito da sallaya da kur'ani ya mi'ka mata, ta miko dukkan hannunta biyu da suka sha adon lalle ta kar'ba, yace "Ki rike ibada da kyau ita ce za ta jagorance ki duniya da lahira." Ya kalli Sumayya yana fadin "Ina abin da nace ki ajiye?" Da sauri ta mi'ka masa dama ta shigo da shi ya karba ya sake mika wa Sa'adah yana fadin, "Ki rike tsabta da kwalliya da ma ba na jin ki a wannan bangaren. Inda nake da shakku akan biyu ne. ki 'karanta buri Iyah kin dai san ni ubanki ba kowa ba ne, ki yi alfahari da abin da yake hannunki, ki daina sha'awar wanda suka fi ki ko kuma wanda ba tsarin tarbiyarku daya ba, a yanzu da za ki koma 'karkashin mijinki, ina hada ki da Allah kar ki dinga dora masa hidimar da ba zai iya ba, ko ba ra'ayinsa bane. Da ace za ki rabu da harkar kawaye to ina tabbatar miki za ki 'karantawa kan ki buri saboda ba kya hangensu. A karshen karshe na yafe miki dukkan kurakuran da kika mini, ina fatan Allah Ya lullube rayuwarki da albarkaSa, ya ba ki zuri'a mai albarka, ya kuma hore miki ha'kurin zaman aure." Daki ya yi shiru sai shesshekar kukan Sa'adah, Baffa ya nemi Inna ta ce wani abu, ta girgiza kai tare da cewa, "Duk abin da zan fada na dade ina mata bita indai mai ji ce ai ta haddace su. Fatana Allah Ya albarka ci aurenta." Cikin soyayya mai yawa Baffa ya kalli Sumayya ya ce, "Saura ke babbar yaya uwa ta biyu!" Ta yi murmushi cikin sanyin murya ta ce, "Komai kun fada Baffa, fatana a ce duk ta ji ku da kunnen basira, ta kuma ri'ke 'yan'uwansa da girma, musamman iyayensa. Ki rike su da mutuntawa komai za su miki kar ki nuna kin ji haushi ki yi hakuri, ki sake ninka kulawarki a kansu, duk kuma wanda ya je gidan, ki karbe shi da sakakkiyar fuska su ji tamkar a gidan yar'uwarsu mace su ke saboda sakewa da walwala." Baffah ya nisa yace " idan Kika bi maganganun mu kin tsira! Idan kuwa kika je kika biyewa 'kawayen banza da son zuciya ki tabbatar ke 'kadai za ki dauki 'bacin ran da zai same ki, ki bi mijinki ko zaluntarki yake yi ki bishi da addu'a idan abin ya gagara, sai mu shiga, amma idan ke Kika bijire to fa kisani baki da wurin zama a gidannan". Ya rufe zaman da doguwar addu'a ya kuma rike ta a hannunsa ya tafi kai ta 'dakinta da kansa a motar Alhaji Isa da ya zo daukar Amarya. 'Yan'uwan Baffa da na Inna da suka zo, sai mamakinsa suke yi da ya hana su zuwa kai amarya, ya tafi da kansa ya kai 'yarsa dakinta. A lokacin kam ya zo da sabuwar dabi'ar da ta sha banban da al'ada, ashe shi yasa yasa aka kai su suka ga gidan amarya tun jiya? *SURAYYA DAHIRU*. ✍️✍️ 🌺 *HALIN YAU*! 🌺 •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* ✍️ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana ɗamfare da bin ƙa'idar Adabin Hausa.``` ```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` ✏️✏️✏️ ____________(✪)______________ https://mobile.facebook.com/Lafazi-Writers-Association-104448621878916/ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·• *_Dokɑr hɑkkin mɑllɑkɑ me lɑmbɑ tɑ 68, tɑ nunɑ cewɑ sɑtɑr fɑsɑhɑ bɑbbɑn lɑifi ne dɑ yɑke dɑidɑi dɑ sɑtɑr dukiyɑ._* *A guji taba ko sarrafa labarin nan ba tare da izinin mai Hakkin mallaka ba.* *SADAUKARWA GA* *SADIK ABUBAKAR* *TUKUICI GA* _*AISHA IBRAHIM BAFARAWA*_ (*BEAUTY*) *MK DA SA'ADAH NA GAISUWA* 👍 49-50. *GIDAN AMARYA* A gidan su Baffa suka tarar da su Baba Umaru da Baba Idi da kuma MK. Tunda Baffa ya fa'da musu a wurin 'daurin aure cewar shi zai kai amarya 'dakinta kar a turo mata, sai suka fasa komawa Bichi a yau, suka ce su za su karbi amarya da kansu. Haka Baba Umaru ya tisa MK da jan kunne iri-iri akan ya ji tsoron Allah ya ri'ke matarsa cikin tausayi da adalci, komai za ta yi ya dauke kai ya fahimtar da ita cikin ruwan sanyi. Baba Idi ya nisa ya ce, "Sannan zan fa'da maka gida naka ne, amma kayan ciki na matarka ne, kana dai ganin irin mutunci da karamcin da aka maka, to ina ro'konka! ka nuna kai ma ka san mutunci ta hanyar zama da yarinyar nan da kyautatawa, ba hankalinku 'daya ba, mata lamarinsu yana da gigitarwa. Amma idan aka yi ha'kuri da su, aka musu afuwa sai a ji dadin zama da su, saboda masu rauni ne, kuma masu tausayi ne". Alh Isa kuwa cewa ya yi, "Abin da zan fada muku ni ne uban Mukhtar, ni ne uban Sa'adatu, sannan ni ne alkalinku dukkanku 'daya kuke a gurina.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157