Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 81

Chapter 81

Halin Yau Book 1 Complete Hausa Novel 1,197 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tsayawa ya bi ta kansa. Ta shiga damuwa da tsoro irin wadda bata taba shiga ba, tsoron ta 'daya idan iyayenta suka ji mai ya jawo wannan tashin hankalin, wanne irin kallo zasu yi mata,? Ta 'kudiri aniyar yau zata bashi, ha'kuri ta kuma nemi ya barta taje ta gaida Aunty Sumayya. Haka akayi, taran dare ta yi wanka, ta shirya cikin kwalliya ta burgewa, tana jin dirin motarsa da kiciniyar bude gate, ta fita a hanzarce ta shiga kicin mai ma'kwabta ka da 'dakinsa ta tsaya. Ai kuwa ya shigo da sauri, ganinsa rungume da kayan wankinsa da ya kai wanki, jikinta ya sake yin sanyi, komai zata yi masa, idan zai kai wanki zai shiga har 'dakinta ya hada kayanta akan nasa ya kai musu wankin amma banda Wannan karon. Kafin ta yi yunkurin shiga dakin nasa sai ta ga ya fito ya fita da alamun ya yi mantuwane, dan haka sai ta yi wuf ta shige 'dakin, yana shigowa kuwa ya rufe 'dakin bayan mukulli har da sakata ya sanya. Yana shigowa ya ganta lafe jikin wadirof, ga mamakinsa sai yaji kwalliyar da ta yi, bai ji komai na burgewa akanta ba, hakanan kamshin ta da ya cika masa hanci bai yi tasiri a jikinsa ba, kyakkawar fuskarta da ke sanya shi nisha'di, a yau ba'kanta masa rai ta yi, hakanan surarta da ke jefa shi cikin shauki, a yau takaici ya ji ya maye gurbi. 'Bacin ransa ya dawo sabo fil tamkar yanzu take gasa masa maganganun da suka zame masa tamkar 'digar dalma a zuciya, suka yi awon gaba da kaso mai yawa na matsananciyar soyayyar da yake mata. Baice mata komai ba, ya shiga rage kayan jikinsa, ya shige wanka, tana tsaye ya fito ya shirya, ya tada sallar shafa'i da wutiri. Sai da ya idar ya zauna bakin gado ya kalleta, ya ga duk ta takura, ta susuce, ta lalace, idonta ya fada alamun dai tare suke 'dan'danar 'bacin rai. Kafin ya yi magana ta rigashi! Ta tsugunna ta ri'ke gadon ta ce "Dan Allah Malam ka yi ha'kuri, ban taba jin nadama irin wadda nake ciki ba". "Ba ki mini komai ba, abin da ke zuciyarki ki ka amayar, sai dai ina so ki sani wallahi ba ki fara nadama ba, ina tabbatar miki za ki shiga NADAMAR da ta zarce wadda kike ciki, da kinsan yadda na tsani ganin ki da hakan ka'dai ya isa ya saki nadama, da kinsan yadda kika wanke kanki a zuciyata da kin gane asarar da kika yi ba ka'dan bace". Kuka ya goce mata, ta rarrafo da nufin ri'ke shi, ya zabura ya mike tsaye cikin bacin rai ya ce "idan kika yi kuskuren sa hannun ki a jikina, na rantse miki sai na miki abin da za ki gamsu ba ki da sauran 'kima a gurina. domin duka zan miki irin yadda ake na'dawa 'yantattatun matan bariki idan angama cin moriyar su". Kukan ya tsaya mata! da gaske ta yi kuskure, irin kuskuren da ake yi sau daya amma sai an nemi hanyoyi gyara dari bai gyaru yadda ake so ba. daga jiyo magana a bakin shedanun mata ta ara ta yafa, har ta zo ta fa'dawa mijin aurenta wadda da gaske samun irinsa zai yi wahala. Ta zauna 'dabas tsakanin gado da wadirof ta dinga kuka, mai cin rai, na tsantsar nadama. Daga inda yake ya ce "Ta shi ki bar mini 'daki ban bukatar ki a cikinsa". Ta kasa koda kwakwkwaran motsi. tace "ka yi hakuri ba dan ni ba, ka dubi girman Allah ka yi hakuri". Jikinsa ya yi sanyi yace "Na ji, amma dai tashi ki fita, ina bukatar ka'daici ne, duk sadda nake da bu'katar ki a dakin I will let you know". "To ka daina rufe 'dakin, na yarda duk sadda na zo ka kore ni, amma ka daina rufewa". Ya zuba mata ido yana jin takaicinta na sake kama shi, amma da yake so yake ta fita ya shaki iska marar takura sai yace mata to a takaice. Ganin ya amsa mata sai ta tashi ta bude 'kofar ta fita tana fadin " ka yi hakuri, ka yi barci mai cike da walwala". Ya bita ya rufe kofar, ya dawo ya karanto adduar barci ya kwanta. Washagari da sassafe ta shirya masa abincin karyawa ta zauna zaman jiran ya bu'de 'kofar, ai kuwa yana budewa ya ganta da tiren abinci, a bakin kofar dakin, yasa kai zai wuce ta ce, " Ina kwana?" Ya amsa a gajarce, "ga abinci na gama". ya girgiza kai ya ce "ki daina wahalar da kanki wurin yin abinci saboda Ni, na riga da na 'yanta ki daga dukkan yi mini hidima kowacce iri ce". "Cikin rawar murya ta ce "kace fa ka yi hakuri?" "Da ban yi hakuri ba, da baki ganni akan 'kafufuna ba, da ina can akan gadon asibiti saboda ba'kin cikin ki, da ban yi ha'kuri ba, da ban tsaya ina miki magana ba". Ta goge hawaye ta ce "ka kara hakuri dan Allah nasan na yi ba dai dai ba". Ya girgiza kai ba tare da ya ce komai ba, ya fara tafiya, da azama tace " Malam! Umman fanshekara gobe zata tafi Gombe, dan Allah ka bar ni mu tafi tare, ni sai na dawo ko jibi ne". Ya juyo a zabure tamkar wadda ta fadi mugun abu ya nunata da yatsa ya ce" dama nasan duk wannan saukar da kan da kika yi, kina da bu'kata ne, ba kya tashi mutunta ni, ko kwantar mini da kai sai kin ganni da kudi, ko kina son na barki kije wani guri". Cikin kuka sosai ta ce "Haka ka dauke Ni?" "Kin wuce hakama ke kam, saboda ke ciki ce mai manta kyautar jiya, mai manta alheri, da kina da hankali, da baki cemin za ki tafi yawo Gombe ba, kawai tafiya za ki yi kanki tsaye". Ta zuba masa ido ta ce "dubo Anty Sumayya ne yawo?" A kausashe ya ce "ke kika san Sumayya, ni mai na hada da ita! ko dole nace?" Tashin hankali 'baro 'baro ya bayyana a jikinta gaba'daya, lalle da gaske Mk ya shiryawa tashin hankali iri iri, wai Anty Sumayya ce yake fadin sunan ta gatsal, duk da ya girmeta da shekaru biyu amma Anty yake cemata, sannan kuma har yana cewa mai ya ha'da da ita?. Ta kalleshi baki na rawa ta ce "Dan Allah Malam ka yafe mini, mu zauna lafiya ba zan iya kar'ban wannan tashin hankalin daga gareka ba, na rantse maka ba zan kuma maka laifi ba, zaman lafiya zamu yi, fiye da yadda ka ke so". Ya yi murmushi ya ce "na la'anci zaman lafiyar da ki ke so mu yi Sa'ade, zuciyarki bata da alheri, kwakwalwarki ba ta da tsinkaye, harshenki yafi na maciji dafi, ba sauran zaman lafiya tsakanin mu, idan har kika zauna lafiya da ni ban yafe miki ba". "Zuwa Gombe, ko yanzu kina iya tafiya, sai dai idan ina da hakki akan ki, ba za ki ga alheri a yayin tafiyar da dawowar ba in sha Allah". Ya ja dogon tsaki yana fadin shashar yarinya da bata san mutunci da kyautatawa ba". Ya sake jan dogon tsaki ya fice,

Table of Contents

Chapters

157 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});