Chapter 8
Chapter 8
meyake fada. Ajiye robar hannunsa yayi yana kokarin dagota amma gaba daya jikinta ya sake. Ambatar sunanta yafara yana shafa fuskanta zuwa wuyanta kuka na zuwar masa sosai. Kuka me qarfin gaske babyn datake gefensu ta fasa wanda ya sakasa saurin juyowa yana rasa ya zaiyi. Kuka sosai baby tafara wanda ya sakasa sakin umman ya zauna tsakiyarsu yana sunkuyar da kai shima ya fara kuka yana wani sheshekan da har jikinsa rawa yakeyi. Ya jima a hakan batareda yasan me zaiyiba har babyn ta gaji tayi shiru ta koma bacci. Ummansa kuwa wata firgita ta fara tana jijjiga. Qanqameta yayi yana ambatar sunanta amma batasan ma yanayi ba. Kusan awa daya a hakan kafin jikinta ya sake sakewa tayi baccin wahala. Shima a gurin cikin jikinta baccin walaha da yunwa ya daukesa. Sai azahar ya farka ya fita gidan ya nufi gurin aikin lakar dayake zuwa yana dan tayasu suna basa nera dari. Acan yayi sallah yayita musu aiki har wanda yafi karfin shekarunsa. Daga can wani kokon ya sake siyowa ya kawo yasha shida umman wadda sedai ya bata daga kwancen dan bata iya tashi hakama gabaki daya ta koma kamar ba umman tasa ba sbd wasu abubuwa takeyi da fizge fizge da zabura. Yamma nayi yasan baba ila baya gida dan haka ya dauke babyn ya rufeta da zani kusan uku ya nufi gidan mama sakina da ita sbd tanada kuka. Harya isa gidan babu wanda ya taresa ya tambayesa sbd gudunsu ma akeyi a kauyen sbd camfa ummansa da akai da baqar mace. Mama sakin wuni tayi cikin damuwa da tinaninsu dan haka tana zaune tana hada saka da warwara tagansa ya shigo da zani kallo daya tai masa ta gane jaririyarce ya dauko. Cikeda mamaki da tsoro ta kallesa tana miqewa ta karbi 'yar tana cewa "Abdul meyasa ka fito da ita?? Yaya ummanku? Ya jikinta? Kasancewarsa mara hayaniya da rashin sabo da magana sosai sbd baida abokan wasa ko wasu yan uwan daya taso cikin gata yasa ita kadaice ma wacce yake magana da ita sosaima Ya dan dago kansa batareda ya kalleta ba yace "Tanata kuka ne tin dasafe, Umma kuma batada lafiya tanata firgita" Kasa cewa sakina tayi ta nufi daki takai yar da sauri tana fitowa ruwan zafi tafara dorawa kafin ta dauko abincinta na rana da bata samu ci ba sbd damuwa ta miqa masa tace "Maza zauna ka cinye yanzu" Zaunawa yayi yaci abincin ita kuma tana sauke ruwan dauko babyn tayi tahau yi mata wanka sbd batason baba ila ya dawo ya taddasu hakama batason yayi dare a hanya da 'yar. Wanka sosai me kyau tayi mata duk da bata taba haihuwaba batasan yaya akeyiba amma dayake anata haihuwa a gidan tana gani kuka tana dan saka hannu sai ta iya. Tana gama mata wanka kayan data siya guda daya na jiran haihuwar matar Gali 'dan mijinta ta dauko ta sakawa yar ta dauko madarar shanun datake da ita me kyau ta bata kuma cikin ikon Allah yarinyar tasha take ta koma bacci abinta. Sake nade masa ita tayi sosai ta basa tace maza ya koma. Karbanta yayi ya juya ya fice daga gidan. Koda ya isa gida ummansu ta tashi tana zaune ta zubawa kofa idanuwanta da sukai fari fes hakama bakinta ya bushe sosai. Cikeda mamaki da dan farin cikin ganin ta tashi ya qaraso yana cewa "Umma kin samu lafiya? Juyo idanuwanta da suke kamar a buge tayi ta zuba masa batareda tace komaiba sbd kamar ba yayanta bane take gani. Sake tambayarta yayi yaga ko kyaftawa idanuwanta basayi kallansu takeyi numfashinta baya fitama daidai. Babyn ya bude daga zaninta ya dora mata a hannunta yana cewa "Mama sakina tai mata wanka ta saka mata kaya" Babyn ta saukar da idanuwanta ta zubawa ido tsawon mintina kafin ta dago ta zubawa Abdul din idanuwan shima Shima ita yake kallan cikin tsoron irin kallan datake musun. Sakin babyn tayi da sauri ya tare tareda daukanta ya ajiye gefensu yana cewa "Umma kin gaji ne? Har lokacin batace komaiba bata kuma dena kallansaba kaman wanda bata saniba ko bata taba ganiva. Zamewa tayi ta koma ta kwanta tareda zubawa babyn gabanta ido. Har dare yai suka kwanta batareda sun samu abinda zasu ci ba umman batai magana ba har lokacin hakama bata dena kallansu ba. Cikin tsakar dare cikin bacci yaji motsin umman ya bude idanuwansa sai yaga ta tashi zata fita ko dan kwali babu a kanta hakama bata ko iya tsayuwa da kyau. Kasa daukanta kafafunta sukai ta zube qasa kanta na buguwa da bangon kofar fita dakin take goshinta ya fashe da jini. Tashi yayi da sauri yana riqota cikin tsoro da tashin hankali yana cewa "Umma ina zaki? Zaki bandaki ne? Kallansa ta juyo tanayi kafin ta dago hannunta dayake wani irin rawa ta nuna masa kofa batareda tace komaiba. Kofar ya kalla kafin ya kalleta sai ya rasa me zai fada ya kamo hannunta kawai ya dawo da ita kuma ta biyosa kamar yarinya qarama. Kwantawa suka koma sukai take kuma saita koma baccinta. Gari na wayewa yaje yayo aikinsa ya dawo mata da koko ya sake dafa mata ruwa ya sake ficewa. Sai yamma ya dawo musu da tuwon dawa da miyar kuka dan kadan wanda aikin wahala yayi ya samosa. Kasa cin abincin umman tayi duk yanda yayi sa ita dan haka kaman yanda yake bata koko haka ya zauna ya bata abincin a baki da kansa. Babyn kuwa sake kaita yayi gurin mama sakina ta bata irin madaran jiya tasha ya dawo da ita gida. Yana dawowa a hanya ya hadu da ummansa tana tafiya tana jiri ba dankwali akanta, Da sauri ya kama hannunta suka juya gida yana mamakin abinda ya samu umman ga jikinta duk jini. Suna komawa gida ya zaunar sa ita yana mata magana amma kwata kwata batacewa komai kallansa kawai takeyi. Hawaye ya fara batareda yasan me zaiyiba. Da daddaren ranar ma so biyu tana kokarin fita yana dawowa da ita tim anan ya fahimci ummansa ta kamu da wani sabon rashin lafiyar. Kuka ya ringa yi har safe kuma da safen ma daqyar ya iya fita yabarta. Koda ya dawo bata fita ba amma tana zaune babyn nata kuka sosai kamar bataji sai kallanta takeyi idanuwanta sunyi jajir kamar zasu fashe. Daukan babyn yayi ya zauna gaban umman ya fada jikinta yana fasa kuka shima yana ambatar sunanta. Kukansa ne ya saka wani irin hawaye masu tsananin zafi da ciwon da bata saniba tsinke mata tana qanqamesa tana jin tsananin sonsa shi kadai dan shi kadai take jin sonsa amma babyn kwata kwata kamar bata santaba dan kanta dake kokarin juyewa koma ya juyen. Sun jima a hakan suna kuka duka su ukun harda babyn da suka matse a tsakiyarsu. Sun jima a hakan kafin umman tayi bacci da babyn shi kuma ya fita sallan magrib yana dawowa a gida yayi ishai sukai baccinsu. ***kwanaki suka fara tafiyar musu ahankali ahankali ya fahimta da kyau kamar ummansa ta haukace sedai hauka bame tashin hankali ba wanda asalin yunwa da infection ne daya mummunan shigarta a gurin haihuwar me mugun karfi daya juyar mata da kai kwata kwata ta manta wai haihuwa tayi. Mama
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163