Chapter 140
Chapter 140
ya sauka fuskansa daga Sayd wanda yasha gabansa a hankali yana masa kallan tsana me tsananin gaske, Sake juyowa Ammar din yayi yana fita hayyacinsa zai sake nufar AZIZ Sayd ya sakar masa wani mahaukacin marin tareda kama hannunsa ya sake sakar masa wani marin idanuwansa ba rufewa shima zuciyarsa na tafasa tako ina jin yake ayau da suka fuskanci juna a matsayin su din babu boyo kaman zai iya kashe Ammar yakeji sbd radadi da tsana me karfi ce yake dannewa da boyewa tsawon lokaci amma banda yau. Kasa dena tasowa Ammar yai sbd gabaki daya ya fita hayyacinsa AZIZ yakeson shaqewa ya rabasa da duniya ko zasu samu salamar rayuwarsu daya riga ya lalata masu su duka kaf zaadens. Sayd da shima nasa idanuwan suke a rufe da zuciyarsa duk motsi daya idan Ammar yayi na yunqurin matsowa mugun naushin dayake fasa hancinsa yake sakar masa yana jin zuciyarsa na kasa samun sassaucin abinda yake ji ko kafan. Maheer dayake riqe da Dad dake neman rasa ransa hawaye ne masu tsananin radadi da ciwo shima suka gangaro masa ganin yanda hancin Ammar ke fidda jini. Juyawa AZIZ ya fice sbd shima zuciyarsa gap da sakasa hawayen tsananin ciwon dayake ransa.... Sayd kuwa saida ya tabbatarda Ammar ya zube qasa yana neman taimako kafin ya juya ya fice daga dakin hawayen d suka cika idanuwansa suna zubowa kan fuskansa ahankali. Barin asibitin sukai, Suna ficewa Maheer ya buqaci likitoci suyi gaggawan zuwa ga dad, Ammar ma gaggawar ficewa akai dashi daga dakin ana wucewa dashi inda zaa dubasa, Mimi kallo daya taiwa Ammar ta kusa yanke jiki ta fadi Saleem yayi saurin riqeta yana shiga tsananin mamaki da tsoron meya faru shima, Jamian tsaro likitocin zasu kira Maheer ya hanasu yana cewa su barshi issue din cikin gida ne. Hankalinsu dawowa yayi kan Dad da aketa kokarinsa ceto rayuwarsa datake nisa, Ammar ma aka gyarawa fuska duk bandage dawowa yayi dakin suka zauna zaman jimami da qunci sbd babu me iya magana idan ba ganin sukai Dad ya farfado ba, Maheer wasu hawaye ne masu zafi ne suka ganganro masa ahankali yana jin zuciyarsa na neman mutuwa, Idan dad bai tashi ba baisan ta ina zai fara rayuwarnan ba da sauran familyn da nauyinsu zai rataya akansa baida mai jagoransa, Ta ina zai fara fuskantar babbar matsalar da suka aikata su da yawa a wayi gari ace shi kadai ne zai fuskanceta sbd Ammar dai ya riga ya samu tabin kan da ba lallai ya karba hukuncin komaiba, Tayaya zai iya kubutar da jannah daga AZIZ shi kadai? Innalillahi wainna ilayhi rajiun"""' shine abinda zuciyarsa ke maimaitawa yanajin kaman zuciyarsa zata fashe. Mimi bata iya magana a yanzu karfinta ya qare tas tayi weak sosai batajin dadin zuciyarta ko kadan, Saleem ma kusan baida abin cewa ko tambaya sbd komaima a yanzu kamar baida amfani, Dukkaninsu qasar suke son bari su koma inda suka fito rayuwar zatafi musu dadi acan, Zasu bude sabuwar rayuwa su sake gina sunansu cikin kwanciyar hankali da Aminci. Ganin jikin Dad din yana sake nisa sai kawai Maheer ya kira jannah daya san dad din zaiso ace ya bude ido yayi mata ganin karshe. Koda Maheer ya sanar da ita ana sallar ishai lokacin dan haka sallar ta samu kawai tayi jikinta na dan rawa zuciyarta na wani irin rawar tsananin tsoro da tashin hankali. Ko mama bata tsaya fadawa ba ta fita hannuwanta na wata irin rawa. Ganin yanayinta ya saka falaq hanata driving tace suje da driver su kaita tinda dad din baya nan. Bata musa ba sbd bata cikin cikakkiyar nutsuwarta matsanancin tsoro ne ya rufeta sbd batasan tina mutuwa akan mahaifinta da shine rayuwarta. Tausayinta sosai falaq takeji sbd tasan irin tsananin so da kaunar datakewa Daddynta shi Jannah kewa Dad dinta dan haka kwatanta rayuwa babushi abune da shi kadai zai iya zarar da kai. Koda suka isa asibitin falaq bata fita motar ba ta bari jan din ta tafi ita kadai sbd ta fara ganinsa ta samu nutsuwa tukuna. Jannah na isa dakin a sanyaye ta bude ta shigo dukkaninsu suka dago jajayen idanuwansu da duk suka jeme suka zuba mata. Sanyi qafafunta sukai ta tako ahankali hawayen cikin idanuwanta na saukowa ta nufi gadon Dad din wanda yake kwance kamar ba rai a jikinsa yayi mummunan jemewan data sakata rintse idanuwanta tana zaunawa bakin gadon ta dora hannunta akan nasa tana fashewa da kuka mara sauti. Tsit dakin yayi kowa ciwon ransa na qaruwa kukanta na ratsa kunnuwansu. Mimi ce ta bude baki Ahankali batada ko wani karfi sosai ciwon dayake cin zuciyarta na bayyanuwa cikin mutuwar jiki tace "Mahaifinki bai hada soyayyarki data komai da kowa ba amma ayau mijin da kika zaba kikace shi kikeso wanda a hakan mahaifin naki ya zabi farin cikinki akan familynsa shine yake neman neman ganin bayan mahaifinki da ahalinki, Me ahalinmu sukai masa dayake neman ganin bayanmu? Wane irin miji ne zai cakumi mahaifin matar dayake aure bayan yasan baida lafiya sosai??? Jannah me kikeyi da wannan mijin? Me zakiyi da miijin dayake neman rayuwar ahalinki? Kalli fuskan Ammar kiga abinda yayi masa, Wannan shine mijin da zuciyarki ta zabar miki akan ahalinki da suka zabeki fiyeda rayukansu? Wannan shine sakamakon soyayyar da mukai miki tin kina yarinya? Dago jajayen idanuwanta tai cikeda mamaki da tsoro harma da fargaba me tsanani tana kallan Mimi kafin ta maida kallanta kan fuskan Ammar da sai a lokacin ta lura nade take da bandage mummunan duka ne a fuskan ba kyan gani. Waya Ammar ya fidda ya nuna mata hotinan da yayiwa AZIZ a lokacin daya shaqo Dad ya zubar. Mummunan faduwa gabanta yayi ta dago cikin slow ta kalli Maheer wanda idanuwansa suke jajir ya kasa kallanta. Kan Saleem ta maida kallanta wanda ya saukar da idanuwansa da sukai jajir shima a hankali yana jin ciwo da radadin abun har qasan zuciyarsa. Wani irin nauyi me girman gaske taji yana danne kirjinta ta juya ta kalli mahaifinta hawayen baqin ciki na gangaro mata tareda da jin soyayyar AZIZ LIMBA na sauka daga zuciyarta ahankali tana zubewa. Ammar kuwa bude bakinsa dayake rawa sosai kamar me koyan magana sbd kansa dayake a juye tin dazu da azabar duka ta tayar da ciwonsa yana bubbuga kansa da hannunsa idanuwansa na sake rinewa da ja yace "AZIZ LIMBA makashi ne, Shine ya kashe Daddy mahmoud, Shine yake kashe kowa, Shine ya kama su Abraham, Shine yakeson kashe dad, Idan ya kashe dad zai kashe kowa, Kema jannah yace saiya kashe ki, Zai kashe kowa, Bazai dena ba saiya kashe kowa dayake zaadens sbd Qanwarsa, Qanwarsa ce a kirjin jannah, Qanwarsa ta mutu, Yace saiya kashe kowa, Ya fada da bakinsa....... Shiru sukai dakin ya sake daukan shiru maganganun Ammar na futa hayyaci ne kawai suke tashi ahankali kuka na zuwar masa. Maheer zuciyarsa ta gama saddakar da komai vazan iya hana ammar maganar data saka su mimi shiga tinani ba sbd komai dai yazo karshe da alama. Mimi gabaki daya hawaye take tsiyayarwa na baqin cikin jin Ammar na magana a zare basuda abinda zasu iya yi, Saleem ma baqin ciki da ciwon zarewan Ammar din ne ya hanasa fahimtar abinda Ammar din yake
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119
- 120 Chapter 120
- 121 Chapter 121
- 122 Chapter 122
- 123 Chapter 123
- 124 Chapter 124
- 125 Chapter 125
- 126 Chapter 126
- 127 Chapter 127
- 128 Chapter 128
- 129 Chapter 129
- 130 Chapter 130
- 131 Chapter 131
- 132 Chapter 132
- 133 Chapter 133
- 134 Chapter 134
- 135 Chapter 135
- 136 Chapter 136
- 137 Chapter 137
- 138 Chapter 138
- 139 Chapter 139
- 140 Chapter 140
- 141 Chapter 141
- 142 Chapter 142
- 143 Chapter 143
- 144 Chapter 144
- 145 Chapter 145
- 146 Chapter 146
- 147 Chapter 147
- 148 Chapter 148
- 149 Chapter 149
- 150 Chapter 150
- 151 Chapter 151
- 152 Chapter 152
- 153 Chapter 153
- 154 Chapter 154
- 155 Chapter 155
- 156 Chapter 156
- 157 Chapter 157
- 158 Chapter 158
- 159 Chapter 159
- 160 Chapter 160
- 161 Chapter 161
- 162 Chapter 162
- 163 Chapter 163