Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 13

Chapter 13

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sun dena zuwa irin guraren dake kaman kasuwa ko tasha gurin aikin nema ko sanaa sbd bayason ana kallan ummansa da ummitan dan haka Local government yake zuwa dasu har makarantarsa wadda yake gaf da kammalawa yanzu. Har ciki a ke barinsa shiga dasu saiya kaisu bayan ajinsu yace su zauna karsu tashi saiya gama ya fito. Haka zasu sauna suyita wasa a gurin harya gama batareda da damuwa da abinda dalibai ke fada akan mahaifiyarsa da rabin ransa dayake jinta kaman shine babanta sbd BAABAH take kiransa dan bata san kowa ba bayanshi da ummanta hakama shi take kallo ubanta tinda umman ta koma kaman ita tare suke wasa duk da umman ta dena magana. Daga makaranta shagon dayake aiki yake wucewa dasu ya siya musu abinci suci ya ajesu guri daya suyita walwalansu harya gama se yamma su nufo gida sbd baya kaiwa dare sbd su duk da megidansa yana son ya ringa kwana shagon sbd yadda dashi da yayi da kuma kokarinsa tareda amanarsa amma sam baya iya hakan sbd kare mutuncin ummansa da Ummitansa dan haka duk abinda yake samu a aiki ko sanaa yamma nayi yake wutowa gida dasu su wanka suci dan abinda ya samu ya ringa koyawa ummita dan karatun yara har suyi bacci itada umman ya gyara musu gurin kwanciya ya kaisu su kwanta shima ya zauna gadinsu dan baccinsa rabi da rabi ne akansu sam bayada wata irin yadda da kowa gashi basada koda rabin gidan a zube dan haka baya wani bacci akansu. Ranar wata alhamis ya samu wani aiki a wani sabon kamfani da zaa gina a local government na gyaran shinkafa me kudin dayafi tsaron shagon dan haka ya karba ya hada biyu yana yi sedai aikin gurin akwai hadari dan haka dole yake barin su ummita a gida amma saiya fada musu yafi so ashirin kada su fita koina. Sunji maganarsa basa fita dik ya tafi harya dawo baya cikin nutsuwa amma yana tarar dasu a gida basa fita koina sedai gidan zai tarar anyi masa kaca kaca hakama sunyi wata irin dauda hakanan zai tsaftacesu ya gyara gidan ya basu abinci suci su koshi suyi sallah wadda tasa ce kawai ta arziki su kam ture ture sukeyi a gurin sallan tsakanin umman da ummita yana jinsu zai kyalesu a gama a hakan. Akwai wata irin kauna da so me tsananin gaske tareda shaquwar datake basa tsoron da baisan na mene ba a tsakaninsa da Ummansa da Ummitansa haka suke sakasa wasa dasu dole wanda su kadai ne suke ganin dariyarsa da walwalwansa dan Allah ya sako masa wani irin kame kai tin yana yaronsa shiyasa ya taso hakan. Tin yana fargaban barinsu a gida yaje ya dawo harya dan rage fargaban yana aikinsa cikin dan nutsuwa amma bawai hankalinsa baya gidan bane dan baya kara ko minti daya yana tashi aiki yake komawa gidan dan ya dena zuwa makaranta exam kawai yake jiran ranar yinta yazo ta gamawa tinda suka shiga ss3 ya dena zuwan waec kawai yake jiran yi. A yau tinda ya kamo hanyar zuwa gida yakejin baida nutsuwa dan haka ya qara sauri yana jin kirjinsa na nauyi ya kuma saba da hakan a duk lokacinda bay taredasu jin yake zuciyarsa ta ringa shiga damuwa da nauyi kenan. Yamma ne sosai dan haka bai biya gidan mama sakina ba dan bata sabulu da omon daya siyo harda ita ba dan haka ya wuce gida saiya dubosu saika ya fito dasu yaje ya kai mata batareda ya shiga gidan ba san anjima da baba ila yai masa iyaka da shigar masa gida sedai ya tsaya daga waje gefen gidan mama sakinar ta fito ko kawai ya aika mata ummita ta shiga takai ta fito shikuma yana waje yana jiranta su koma. Yana doso gidan tin bai karasa ba ya hango Ummita tana fitowa daga hanyar bayan gidansu tana kuka hannuwanta da kafafunta qasa da jini. Wani irin abu ne ya daki kirjinsa da tsakiyar kansa dan haka da sauri ya qaraso ya tarbeta tareda ajiye kayan hannunsa ya jawota gaba daya jikinta yana kallan hannuwanta muryansa dayake da wahalar ji shima dan baya wani magana sosai sbd baida abokin firar yace "Ina ummah? Meya faru? Kuka takeyi sosai ta juya bayanta ta nuna masa hanyar data fito tana cewa "Umma ta tafi, Dodo ya bita da gudu ta tafi...... Wani mummunan yawu me dacin gaske ya hadiye yana daukan ummitan ya nufi hanyar data nuna batareda ya tsaya fahimtar me take fadaba yana jin kaman kansa zai zare. Duhun magriba yayi amma sam baya ma gani ya doshi hanya yana tafiya yana duba umman kaman zai zai haukace a take yaji yana ji dan haka ummitan dake jikinsa ya sake qamqamewa yana jefa kafarsa duk inda ya samu yana adduar Allah kada ya jarabcesa da wannan jarabawar me girman gaske akan mahaifiyarsa da ita da ummita sune rayuwarsa da hasken dayake gani a wannan rayuwar ko yaya ummansa ta koma yana tsananin buqatanta a hakan. Tafiya yakeyi harya isa wani kauye duhu yai sosai amma kwata kwata baya hayyacinsa. Kaf kauyen babu ummansa babu wanda ya ganda dan haka ya juyo ya dawo kauyensu lokacin tini akai ishai amma be zauna ba ya zagaye kauyen tas nanma babu umman ga ummita wahala da zazzabin raunikan jikinta sun saka tayi bacci a jikinsa jikinta zafi sosai. Bai taba shiga mafi munin tashin hankali da firgici irin daren ba na rashin umman amma bai damu da daren ba haka ya doshi wani kauyen a cikin tsananin duhun dare nemanta idanuwansa sunyi wani irin mummunan jajir. A cikin dare mafi tashin hankali a rayuwarsa kauyuka uku ya zagaye amma kwata kwata babu ummansa babu wanda ya ganta dan haka ya yanke jiki ya fadi qanqame da ummita zazzabi me mugun karfi ya gama gabalaitar da ita a jikinsa. Jamaar kauyen daya somen suka yo kansa sbd lokacin har anfito sallan asuba gari ya waye sosai suka yo kansa suna son cire ummita a hannunsa amma yai mata wani irin mugun riqo da dole tana jikinsa aka zuba musu ruwa a tare. A tare suka sauke ajiyar zuciya sedai kowannensu a galabaice musamman ummita shi kuwa ganin yayi kaman baya ganin komai sbd azaba da wahala tareda galabaita da tsananin tashin hankali. Tashi zaune yayi yana gyarawa ummita zama a jikinsa yana sake rungumeta da kyau wasu zafafan hawayen daya manta rabonsa daya zubo suka gangaro daga fararen idanuwansa da suka koma jajir ya ambaci sunan umman ahankali yana rokon ALLAH ya kawo masa kowacce irin jarabawa indai ummansa zata dawo garesa zai jure ya runguma kaddarar. Tausayinsa ne ya rufe jamaar gurin dan haka aka taimaka masa aka tayasa bincika neman umman tasa a kauyen amma har yamma babu labarinta kuma har dayan kauyen suka tayasa nemanta amma babuta. Kauyensu ya nufo ummita na jikinsa a some sbd ruwan saman da akeyi sosai duk ya qare akansu. Koda ya dawo kauyensu ana sallan ishai duhu yayi sosai, Kofar gidan ya shiga wanda ruwan sama ya cika gidan kai tsaye dakinsu ya nufa ya bude ya shiga Taku daya yayi zuwa biyu kafafunsa suka kasa daukansa ya zube a gurin yana fasa wani irin kuka me karfin gaske

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});