Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 153

Chapter 153

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ta nufi dakin me aikin ta bude taga babu komai nata ta kwashe sai tarkace kawai. Fitowa tayi ta nufi dakin Mimi ta duba taga duk an yamutsashi an kwace sarkoki da wasu abubuwan harma da sitirarta aka kwasa. Numfashi me dumi ta sauke ahankali tanajin jikinta na sanyi sbd ta fahimci abinda ya faru matar ta gudu kenan sbd kudin. Palo ta dawo kafafunta na sagewa ta zauna tana tallafe fuskanta da tafin hannuwanta. Batasan matar na son kudi ba da zata siyar da abubuwa da dama ta bata kudin sbd ta zauna da ita ta sabu da ita a yanzu kuma ta sake komawa ita kadai a rayuwarta me aikin ma datake tayata quntacciyar rayuwarta ta gudu ta barta. Ta dade a gurin zaune kafin ta miqe ta nufi daki ta sako hijab ta fito ta fita gidan a hanya taje ta siya abinci ta xauna cikin mota tana ci tana jin kaman zai shaqeta ta mutu sbd kwata kwata ba abinci ne a rayuwartaba kawai cikinta takeson abincin ya shiga sbd kada ta rasa karfin tsayuwa da kafafunta ta taimaki iyayenta. Wani abincin ta sake siyowa ta dawo dashi gida ta bawa me gadi kudi shima tace ya ringa cin abinci. ********Sati Biyu da tafiyar me aikinta tana kokarin fita da safe motocin jamian tsaro suka iso gidan tareda zungureriyar takardar karbe komai na Zaadens komai da komai hatta siritar sakawansu sbd zaa fara shariarsu dan haka ana buqatar dakatar da komai nasu har sai yanda shiriar ta kaya dan anason kaf rayukan da suka dauka sai anbiya diyyarsu me girma. Zamewa tayi jikin bango tana rintse idanuwanta da kuka ya qafe musu tana sauke numfashi tareda ambatar sunayen Allah a cikin rant. Da kansu suka shiga suka rufe koina ita kadai aka bari ta dauki kayan sakawarta a cikin yar qaramar jaka ta fito suka karbe keys na duka motocin gidan ana rubuce rubuce da daukan hotinan komai. Dakin me gadi da aka sallama take aka bata damar zaunawa har a gama komai ita duk bata damu da wannan ba nutsuwa taji tana samu na fito da iyayenta da zaayi a fara shariar sbd tasan a wannan lokacin Allah ne kadai yasan irin azabar da suke cikinta. Washe gari tinda safe ta shirya da dan sauran canjin dayake hannunta ta fito dakin me gadin tareda rufe kofar dakin ta fice gate ta rufesa shima tafara tafiya me dan tsayi sosai kafin ta samu abin hawan dazai kaita inda daga karshe aka sanar da ita suna can bama a cikin garin abuja bane fita akai dasu. Headquarters din da zaa taho dasu ta nufa tana isa sauka tayi ta nemi guri ta rakube ta zauna tana jiran a iso dasu. Tinda ta iso ake kyararta ana mata wasu tambayoyi masu ciwo da wulaqantawa bata cewa komai sbd jikinta rawa ma yakeyi na tsoro amma kuma zuciyarta ta riga ta bushe ta kafe akan ahalinta dan haka ta kasa bari tsoronta ya rinjayeta ta gudu daga gurin. Zaman awa daya tayi idanuwanta duk sun qanjame bakinta ya bushe zuciyarta harbawa takeyi sosai tana zubawa hanya ido., Kunnuwanta ne suka fara jiyo mata jiniya wadda ta saka yan media dake boye fitowa da yawansu suna cike kofar shiga gurin da yan kallo sosai harma da yawa daga cikin familyn wainda aka kashe nasu na nan Nigeria sbd an bayyanarda da sunayen wasu daga cikinsu sosai a yanda labarin ke yawo.. Miqewa tayi tsaye tana fitowa inda ta rakube kanta bugun zuciyarta na tsananta tana kafe motocin da idanuwanta har suka tsaya aka bude bayan motar prison din, Dr Ken ne wanda ya rasa kafarsa daya aka fara fitowa dashi gabaki daya kammaninsa sun sauya ya koma kamar mahaukaci idonsa daya ya tsiyaye. Dauke idaniwanta tayi akansa sbd bashi take buqatan gani ba, Ammar ne na biyu wanda yanda ya koma ya sakata yin baya tana neman faduwa zuciyarta na kasa dauka sedai kafin ta ja wani numfashin aka fito da Dad dinta wanda ta ambaci sunansa da karfin gaske tana yi kansa da tsananin gudu wanda ya saka duka jamian tsaro da yan media dawa da kallansu akanta hakama kafin jamian tsaro suyi yunqurin tareta da sauri tini ta isa kan mahaifinta ta fada jikinsa da karfin gaske sukai baya zasu zube sbd baida karfi ko kadan Ammar dayake tsayuwa da qyar da sauri ya tsaya bayan Dad din yana taresu ta qamqame dad da wani irin karfin gaske wanda shima duk da baya gani sosai sbd azabar dasuke cikinta wata irin runguma yayi mata me karfin gaske yana cewa "Jannah kece????? Qanqamesa ta sake yi da karfin gaske tana ambatar sunansa kawai zuciyarta kaman zata tarwatse a gurin ta fasa wani irin kuka me tsanani karfin gaske tana kiran sunansa kawai bata iya cewa komai tana jin kaman Allah ya dauki ranta a gurin a jikin mahaifinta. Shi kansa da baya ganinta sosai qanqameta yakeyi yana ambatar sunanta hannuwansa na tsananin rawa bakinsa ma na rawa.. Ammar ma juyawa yayi yana kasa kallanta kuka me karfin gaske yana zuwar masa kaman yanda Maheer ma kasa kallanta yayi kansa n qasa idanuwansa sunyi jajir. Securities mata aka kira da sauri suka fito aka fara banbareta daga jikin dad dinta ta sake qanqamesa tana qin sakinsa tana tsananta kukanta tana kiran sunansa. Kasa cireta daga jikinsa akai zuwa lokacin shima kukan yakeyi sosai sbd gabaki daya zuciyarsa matacciya ce akan 'yarsa.. Dukanta Securities din suka farayi tana qin sakinsa dan haka suka fara tsanantawa Ammar ya juyo da saurin yana rufeta jikinsa hakama Maheer dad ya rufe wanda shima ake dukansa sbd rufesu da duka akai ana kokarin rabasu jannah na sake riqe dad din wanda yake banbareta da jikinsa shima sbd a dena dukanta. Ba tausayi aka rufesu da duka gabaki dayansu dan haka Dad ya saka karfinsa ya cinketa daga jikinsa akai saurin riqeta tana zubewa qasa cikin tsananin kukan dayake neman qare mata tana rintse idanuwanta bakinta na fidda jini. Jansu akai zuwa ciki da karfi kowannensu bakinsa da hancinsu na fidda jinin dayake kona zuciyarta yana kasheta ahankali. Sai alokacin aka fito da Anny da dr Abraham wanda zaa miqa kasarsu acan xai karba nasa hukuncin sbd acanma sun kashe rayuka akai ciki dasu Anny bata iya ko tsayuwa sbd daurin dayake hannuwa da kafafunta. Ana shigewa dasu aka saketa tareda barinta zaune a gurin tana kukan da babu sauti sai numfashi kawai. Duk yanda taso sake ganinsu baa bata damaba dan haka a gurin ta wuni sai dare ta koma gida zazzabi me karfi na cinta. Kwantawa tai kawai bata iya komai sai jikinta dake rawar zazzabi har wani azababben bacci ya dauketa a gurin. Tsakiyar dare cikin bacci taji motsi a kofa ta bude idanuwanta ahankali daqyar sbd nauyinsu ta motsa tareda dafawa ta tashi zaune ta miqe tsaye tareda nufar window datake jin motsi kullum tinda ta dawo kwana dakin kullum tana jin motsi kaman akwai wanda yake kwana kofar dakin dan haka yau bude window tayi kai tsaye. "SALEEM" ta furta cikin tsananin sanyi da mutuwar jiki tareda kasa yadda da abinda idanuwanta suke nuna mata. #MAMUH ZAFAFA BIYAR KALBIM 500 mamuhgee A DUNIYATA 500 Huguma AJIYA A DUHU 500 Billyn Abdul

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});