Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 145

Chapter 145

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

wasu hawaye masu tsananin zafi da tashin hankali suna gangaro masa jikinsa na daukan rawa gabaki daya wanda ya saka kowa dayake gurin tsit kafin kukan daya kasa riqewa ya kubce masa sbd kaman ana fada masa ne Falaq tafiya zatai ta barsa kenan.. Sautin kukansa ne ya tayarda tsikar jikin dukkanin wanda yake gurin yana ratsa zuciyoyinsu, Jijjiga jikinsa keyi sosai fuskansa na tafin hannuwan mama datake hawayen tausayinsa har cikin ranta, Sayd ma silalewa yayi ya zauna a qasa hawaye masu tsananin zafi da radadi na tsinke masa sbd kai tsaye kaman dama ce aka sanar dasu ta kwanakin dasuka ragewa Falaq a duniya. Mama ma ganin kukan Sayd sai ta kasa riqe sautin kukanta ta rintse idanuwanta tana sake jin saukan hawayen AZIZ masu zafi a tafin hannunta. Dr Ashir da suke saka hawaye taruwa a idanuwansa barin gurin yayi yana jin tausayin familyn gabaki daya sbd shi kansa yasan samun donor abu ne me wuyar gaske da ahaka suna ji suna gani lokacinta zaiyi tabar duniya. Daqyar mama ta iya kama hannunsa ta dagar dashi ta kama hannun Sayd shima dayake kuka rasa 'yarsa da har yau batasan matsayinsa na mahaifintaba, 'Yar dayake kallo a lokutan quncinsa ya samu sassauci da sanyi, 'Yar dayake wa kallan mahaifiyarta daya rasa, 'Yar da har yau bata taba kallansa a uba ba bare ambatarsa da sunan uba ko so daya ba... Dakin falaq din mama ta shiga dasu ta isa dasu har bakin gadonta ta saki hannuwansu suna kallan yanda Allah ya Maidata a lokaci daya ba kyan gani, Oxygen ne da wasu abubuwan a fuskanta da bakinta harma da kirjinta, Tayi haske a lokaci daya tai wani irin jemewa idanuwanta a rufe, Kallo daya zakai mata kasan ciwo me girma ne a tattare da ita wanda Allah ne kadai yasan ko zata tashi kokuwa tafiyarta zatai itama ta huta da wannan duniyar me wahalar zama. Silalewa AZIZ yayi ya zauna a gefe yana kallanta sbd yanayinta dake nuni da azababben ciwone take cikinsa duk da bata hayyacinta.. Sayd ma sunkuyar da kansa yayi yana zuba mata dukkanin idanuwansa jikinsa a mace. Shiru dakin yayi babu me motsi, Ayau falaq datake da gatan da dayawa basada gata a kwance numfashin datake shaqa ma na Oxygen ne zuciyar da zata rayu take buqata, Kudi da gatanta ba zasu iya bata hakan ba, Soyayyar mahaifinta bazata iya bata hakan ba sai abinda Allah yaga damar yi da ita. Tsawon Lokaci ahakan har aka fara kiran asuba suka fito AZIZ na gaba Sayd na gefensa kowannensu idanuwansu sunyi nauyi sosai. Masallaci suka nufa sukai sallah suka zauna suna adhkar har gari yai haske kafin AZIZ ya dago idanuwansa ya kalli Sayd tsawon seconds kafin ya bude baki Ahankali ya furta "Ka sanar da Dr Nico komai da ake ciki a sakamu na list din gaggawar neman donor" Gyada kai Sayd yayi yana sauke numfashi. A kusan qasashe 6 Sayd ya buga da neman zuciyar cikin lokacin daya ragewa Falaq din wadda take qara wani irin sauyawa daga kwancen tana rasa duka albarkar jikinta. Duk yanda suke tinanin zasu iya riqe abin sun kasa su kansu a cikin budadden qunci suke daya nauyaya zuciyoyinsu. Gida suka dawo aka baro Fiddausi dataje can, Tsit gidan yayi ga dining an jere abinci amma babu wanda ya iya fitowa a cikinsu kowa na daki. Wanka yayi ya sauya kaya ya zauna yana buga wayoyi a wayarsa kansa na zarewa ahankali ahankali gurin neman ta inda zai samu zuciyar dasawa 'yarsa. Acan asibitin Zaadens kuwa Saleem ne ya fara dawowa daidai kafin jannah wadda ta zubawa mahaifinta dake zaune gabanta idanuwanta da sukai tsananin laushi. Mahaifinta kaunarsa a jininta take da duk laifin da zai aikata a duniyarnan bazata taba dena so da kaunarsa ba, Bazata taba gudunsa ko qyamarsa ba,bazata taba jin tsanarsaba, Kaunarsa ce take sake rufesa da tausayinsa sbd duka wannan mummunan lamarin daya faru ya farune sbd kaunarta da shedan daya shiga zuciyarsu ya gurbata tawakkalinsu. Ahankali wasu hawayen baqin ciki da dana sani tareda kunyar yarsa suka gangarowa Dad ya dago ya kalleta itama shi din take kalla idanuwanta na tsiyayar hawaye. Saukar hawayensa Kan tafin hannunsa dayake bude ne ya sakata rintse idanuwanta da karfi tana jin zuciyarta na tsananta ciwon ganinsa ahakan... Bude bakinsa yayi Ahankali cikin sanyi yace "Akwai son zuciya da rinjayar shedan a lamarin da muka aikata, Nayi dana sanin nema miki zuciyar datake jirjinki bata hanya halastacciyaba sbd kema kin shiga matsalar da mune muka janyota, Jannah ni mahaifi ne da idanuwana sika rufe akan kaunar danakewa 'yata a baya, Kuma a yanzu ma na shirya zama uba da idanuwansa zasu rufe akan kaunar dayakewa 'yarsa na aminta na shirya karban da fuskantar sharia sbd hana rayuwarki shiga quncin da babu fita, Bakida masaniya dan haka zan miqa kaina da kaina sbd na kasa baki farin ciki daga karshe sai kuka da qunci...... Wani irin kuka me tsima zuciya ta fasa tana fadawa jikinsa ta rungumesa da karfi tana girgiza kai quncinta da radadin zuciyanta na tsananta. Rungumeta yayi shima yanajin kasawarsa da lalata rayuwar duka 'yayansa a matsayinsa na uba. Maheer dake gefensu kuka yakeyi sosai shima har yana jijjiga zuciyarsa na radadi shima yana jin zai iya bin mahaifinsa a duk matakin da zai dauka a wannan rayuwar me kyau da mara kyau dan haka idan mahaifinsa ya aminta dasu miqa kansu su karbi hukuncin daya kamata ya aminta da hakan ya shirya binsa har lokacinda da zaa kashesu kaman yanda suka kashe. Kuka sukeyi gabaki dayansu a dakin cikeda tsananin so da kaunar junansu da haryanzu babu abinda ya sauya daga cikinta, Saleem ma mahaifiyarsa da likita ya sanar dashi ta samu paralys ya rungume yana wani irin kuka mai tsima zuciya. Jannah dagowa tayi ta kalli mahaifinta kafin ta maida kallanta kan Maheer dayake gefenta riqe da hannunta daya ta bude baki cikin sanyi tace "Neman tuba da yafiya a gurin Allah shine farko kafin komai, Insha Allah zamu cinye wannan jarabar Dad" Dakin Mimi suka nufa dukkaninsu idanuwa a jeme a can suka tararda mugun labarin daya qarasa collapsing duniyarsu gabaki dayanta. Sabon zama suka dora na jimami har dare. Tsakar dare Mimi ta farka ta bude idanuwanta ahankali daqyar cikin wani irin sanyi tanajin dukkanin quncin zuciyarta ya yaye ganin ahalin dai daga karshe kansu ya sake hadewa basu rabu ba duk da munin aikin dasu Dad suka aikata. Akan Saleem ta tsayar da idanuwansa tai masa kallan mintina ya saka hannunsa cikin nata yana hango kewan Ammar a cikeda idaniwanta wanda babu bakin furtawa, Maida idanuwanta akan Maheer tayi tana jin tsananin tausayin kaddarar data hau kansu wadda batasan hukuncin da zasu fuskanta ba amma koma menene tana masa fatar samun sassauci da rayuwa me kyau a gaba idan yanada rabon tsallakewa. Maida idaniwanta tai kan jannah da itama ita take kallo idaniwanta sun bushe sunyi jajir babu abinda yake cikinsu sai qunci da damuwa. Hawayene suka gangaro daga gefen idanuwan Mimin tana jin tausayin rayuwar jannah da batasan yaya zata kasance ba idan ta wayi gari batareda gata da dukkanin ahalinta... Maida kallanta kan Dad tai wanda kallo daya tai masa idanuwanta suka rufe ahankali. Maheer ne yafara

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});