Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 41

Chapter 41

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sosai ga gawar ta jima dan haka ba bata lokaci aka fara shirin janazarta wanda Mama da Sayyid ne sukai qarfin hali da dauriyar yi mata wankan gawa da shirinta wanda mama bata gani kwata kwata sosai daurewa kawai takeyi sbd yiwa Ummitah wankan karshe da kanta. Sayyid ma hakan ne daga garesa sedai qaramin dinkin dayake kirjinta ya zubawa ido yana goge mata shi sbd baisan yaushe taji rauni a gurinba sabo hakan, Fuskanta ya dawo da idanuwansa yana fasa kukan dayake riqewa yana kasa cigaba sbd numfashinsa dayake sarkewa da sauri aka fitar dashi matar Babansa da mama ma datake kasawa suka qarasa shiryata cikin suturarta ta karshe a wannan lokacin ne zuciyar mama ta gasa itama sedai aka fiddo da ita bayan an fice da gawar Ummitah din wanda Hankalin kowa yake qarasa tashi anata kuka da firgicin tareda tsananin tausayin Dan uwanta dako gawarta Allah bai basa ikon gani ba wanda sunsani har abada bazai taba dena fita daga radadin hakan ba, Mahaifinsa ya rasu batareda yayiwa gawarsa kallan karsheba sbd babu abinda ya rage a gawar mahaifin nasa wuta ta cinye, Mahaifiyarsa ta tafiyarta tin yanada kuruciya,tana taye ko a mace bai samu ganin gawartaba itama, A yanzu ya rasa rai mafi soyuwa a rayuwarsa amma bai samu ko sassaucin ganin gawartaba. Wannan tinanin kadai yake sake saka mama da duk masu kaunarsa shiga mummunan halin dayake hana zuciyarsu samun sauki. Sayyid ana saka gawar Ummitah kabarinta yaji wani irin Nauyin daya danne kirjinsa da har abada bayajin zai sauka, Ahankali hawayen idanuwansa sukai gangarowan dayake jin duminsu har a kirjinsa da tafin hannuwansa dasuka Ummitah a kabarinta. Rufeta aka fara yanaji yana gani har aka gama rufeta akai mata addua mahaifinsa ya kama hannunsa kaman makaho yana jansa suna barin makabartan yanajin duk taku daya yana rasa ruhinsa da ganinsa sbd dishi dishin dayake gani. Suna isowa gida suka tarar da Alh saad da iyalinsa sun taho gaisuwa wanda shima yayi iya kokarinsa ne ya tarar da jana'izar amma Allah baiyiba. Tashin hankalin dayake ciki da iyalinsa su kansu bamai faduwa bane sbd ABDULAZIZ din kawai suma suke kasa tinanin ma Halinda zai shiga din gashi suna hanya kira biyu yayi masa yana cewa a aika gidansa yanason magana dasu mama sbd kaf wayoyinsu basa shiga yanata kira tin dazu. Kasa fada masa Alh saad yayi sbd yasan Komai zai iya faruwa da ABDULAZIZ din a inda baya tareda yan uwansa dan haka ya zabi boye masa saiya dawo. Mama koda ake shigowa gaisuwa da magriba bata gane kowa da komai yanda ya kamata dan haka anty maryam ta sanar da Alh saad maman na buqatan ganin likita da gaggawa fa. Daman basuda gurin kwana a gurin dan haka kwanan zaune sukai a garin ana lallabawa da mama wadda take jin kamar itama mutuwar zatai. Yanda suka ga safe haka sukaga dare a zaune cikin qunci da damuwa da ciwon rayuka. Ana gama sallar asuba Alh saad yace su shiry karfe goma na safe ayiwa Ummitan addua su tafi sbd akai mama ga likita. Mama rikicewa tayi tana cewa bazata iya barin garinba har abada sbd Ummitah na garin. Wannan kalman nata ya daga hankalinsu aka fara rarrashinta amma sam batama san tanayi ba sbd duk ta rikice kaman ta samu juyewan kai. Baba alhassan ne da kansa ya shigo ya fara bata magana yana tinatar da ita a yanzu ABDULAZIZ ne wanda ya kamata ace duk sun duqufa roqarwa Allah ya basa dangana da ikon daukan kaddara ya samu sassaucin abinda zaiji tin kafin a fada masa, Shine wanda yake tsananin buqatarta a yanzu fiyeda kowa daya rasa Ummitah sbd ita kadaice zata iya kulawa da shi idan wannan mummunan labarin ya samesa. Ambatar ABDULAZIZ kadai idan akai saitaji tana neman sake zarewa sbd kunyarsa da shakkar yanda ma zata sanar dashi Ummitah tabarsa har abada ba dawowa sedai a mafarki ko hoto amma tabbas ABDULAZIZ na buqatanta a kusa sbd duniyarsa ce zata rushe da wannan mummunan labarin. Addua sosai itama Mama da sayyid akai musu ta dangana aka basu suka sha kafin aka samu Maman aka tafi da ita tareda Sayyid wanda shima Saida akai musu nasiha sosai akan zamansu anan bazai taba dawo da Ummitah ba wadda babu kaunar da zasu saka mata dashi bayan Su kaunaci ABDULAZIZ su tsaya akansa batareda sun bari duniyarsa da rayuwarsa ta mutu gabaki daya akan rashintaba. Wannan tinin da Mahaifinsa yayi masa ya sakasa jin duk wani asalin tsananin so da kaunar dayakewa Ummitah suna komawa akan Hammanta wanda zata iya bada rayuwarta akansa idan tana raye. Babu zaman gaisuwan da zaayi dan haka Alh saad na barin garin dasu aka watse cikeda radadi da ciwon rashin Ummitah tareda tausayin yanda rayuwa zataiwa ABDULAZIZ a yanxu da babu ta baida jininsa ko daya a duniya sai abinda Ummitah tabar masa. Tinda aka haifi babyn daga Mama har Sayyid haryanxu babu wanda yasan yanda take sbd kwata kwata sunma manta da ita matar mahaifin sayyid dince take kulawa da ita tinda suka isa . A hanyar komawan nasu Anty maryam ce take dauke da babyn wadda sai alokacin itama ta budeta ahankali ta zuba mata idanuwanta tana kalla. Sanyi jikinta yake dauka cikin tsananin tausayi da mutuwar jiki tana kallan kamannin Ummitah da ABDULAZIZ dake shimfide akan fuskan babyn wadda tin a yanzu da kammaninsu ta shigo duniyar wadda babu komai a cikinta sai son kai da son zuciya da gwagwarmaya tareda kaddarori masu kyau da marasa kyau. Ahankali ta sauke numfashi tana kai hannunta cikin sanyin jikinta daya tsananta ta rufe fuskan babyn sbd sanyin Ac dayake motar duk da an ragesa sosai sbd Babyn. Yamma sosai suka iso Abuja suka fara sauka gidan ABDULAZIZ din Alh saad yayiwa Mama da sayyid yar nasihar hakuri da dangana kafin suka wuce bayan Anty maryam ta nanatawa fiddausi kulawa da komai na babyn dasu maman da basa cikin walwala da nutsuwarsu. Suna ficewa Sayyid yashige yayi alwala ya fita sallan magrib bai dawo ba acan ya tsaya yana karatun Alqurani yana kuka kaman zaciyarsa zata fito kozai samu sassaucin abinda yakeji a kirjinsa. Yana ishai ya dawo gidan ya shige dakinsa bai sake fitowaba saida safe. Mama ma da daddare bayan Fiddausi ta gama bawa babyn madara ta sauya mata kaya da pamper sbd batai mata sabon wanka ba tinda bata iya wankan jariraiba, Dakin maman taxo tayi sallama ta bude tashigo rungume da babyn dake bacci cikin nutsuwar maraici da batasaniba. Dago idanuwanta da sukai laushi sosai mama tayi ta zubawa hannuwan Fiddausin datake tinkarota da babyn ta miqa mata. Hannuwanta rawa suka fara ta dagosu tana jin rawar zuciya ta karbeta tana dorawa akan kafafunta tareda bude fuskanta dake rufe, Tana saukar da idanuwanta akan fuskan babyn bata san lokacinda kuka me qarfin gaske ya kufce mataba tana qanqame babyn wanda take sak mahaifiyarta da tana jinjira. Fiddausi ma hawaye ne suka fara gangaro mata wainda taketa riqewa rashin Ummitah da tausayin megidan da baya nan dana sayyid sai kuma na babyn. Kuka sosai mama takeyi wanda ya saka Sayyid fitowa sbd yana jiyo kukan sbd kofar dakin a bude suka barta dan haka ahankali ya tako ya nufo dakin. A kofar dakin

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});