Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 158

Chapter 158

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

salo wanda yake farin ciki da baqin ciki tareda tashin hankali sbd samun nasarar su Dad na nufin Saleem Zad ya sadaukar da rayuwarsa ga limbas. Wannan tinanin ya saka jannah shiga firgici da sabuwar damuwa me tsananin gaske gashi sunfara kaiwa maqura a rashin komai, Abincinta da zai dade bata nemaba sbd yawan kudinta a gurin me abinci ya rage yawa ne sosai sbd yanzu ba ita kadai bace dan haka tafara zuwa aiki gurin me abincin data nuna mata zata dauketa aiki. Itada Ummah suke zuwa aikin wanke wanken kayan abincin da aikin su fere dankali da doya haka da wanke kayan miya dasu cabbage. Ajiye Ummah takeyi gefe ta hanata komai itace me aikin wanda idan suka wuni suka dawo da dare bata iya bacci sbd azabar ciwon jiki sai ahankali Ummah ta gane abinda yake hanata bacci dan haka kullum suka dawo zata kwantar da ita ta ringa mata tausa cikeda kulawa da kauna ahakan Jannah ke samun dan bacci ya dauketa Ummah xata zauna ta ringa kulawa da ita tana fita har safe tukuna ita kuma idan sukaje gurin aikin ta kwanta tai nata baccin da bata samu da dare ba Jannah na aiki. *******Ayau da zaa shiga tinda safe taje tai aikin da zatai sauran ta sanarwa Madam dinsu zuwanta kotu dan haka ba musu ta bata damar zuwa. Suna gamawa sharp sharp ta fito itada Ummah suka kama hanyar kotu tana jin kirjinta na wani irin nauyi hakama hannuwanta har wani rawa sukeyi. Ummah ce ta kalleta a natse taga yanda duk take fita hayyacinta sbd fargaba kaman koyaushe idan zasu shiga kotun haka take sbd tsananin tsoron koyaushe zaa iya cewa yau an yankewa ahalinta hukuncin kisa. Wannan tinanin kadai rabata da nutsuwarta yake yana sakata shiga mummunan yanayin datake neman zarewa. Ahankali Ummah ta kwantar mata da kanta a jikinta tana shafa bayanta ahankali tana cewa "Zamu dawo dasu gida, Zasu biyomu gida" Koyaushe Ummah ta fada mata hakan jin takeyi tana samun yar nutsuwa da qwarin gwiwa duk da abu ne me wuyar gaske amma bata dena fadawa Allah ba itada Ummah koyaushe Adduarsu kenan. Koda suka isa kotun guri sika nema kaman koyaushe suka zauna jiran isowan su Dad daga gidan yari kafin judges. Zaman kusan awa daya sukai kafin aka iso dasu Dad din kowannensu ba kyan gani musamman Ammar da gabaki daya ya fita hayyacinsa, Ya koma kamar me ciwon sida ya bushe ya qanjame ya koma kamar wanda aka ciro daga rami, Maheer komawa yayi kamar mahaukacin dayake cikin tsananin qazanta, Dad kuwa ganinsa kwata kwata sai ahankali har wannan lokacin gashi su Maheer sun fisa jikin kuruciyar jure azaba da wahala. Dr ken kuwa yana gap da rasa ransa gava daya sbd kafarsa dai ta rube taimakon gaggawa yake buqata idan ba hakan ba zai iya rasa ransa. Anny ma kwata kwata batada kyan gani gashi mahaifinta shima case din ya biyo ta kansa tinda duka akwaisa a ciki wanted ake nemansa ido rufe amma ya boye baasan wace qasar yake ba. Miqewa Jannah tayi tsaye itada Ummah suna kallansu Dad din cikeda kauna da kewansu dake kasheta kowace daqiqa. Zuba musu idanuwanta dake cikowa da hawaye tayi tana musu kallan dayake kasheta sbd yanayinsu abune dayake yankar zuciyarta. Matsowa tayi tanason ta kama hannun mahaifinta ko zai samu sassaucin abinda yakeji itama ta samu sassaucin quncin dayake cin ranta amma aka dakatar da ita ahankali ta ambaci sunansa sautin ya shiga kunnensa ya dago yana kallan inda take baya iya ganinta sosai amma dai ya zuba mata idanuwansa yanajin sanyi yana dan ratsa ransa da ruhinsa. Ammar ma kallanta yayi yana jin baqin cikin da radadin halin da suka sanyata, Maheer ne kadai ya iya bude bakinsa ya sakar mata wani murmushin wahala daya sakata sunkuyar da kanta tana tsiyayo hawaye masu zafi. Ciki suka isa suka zauna Ummah na gefenta riqe da hannunta cikin nata tana share mata hawaye kaman zata ciro ciwon da Jannah din ke ji ta dawo dashi kirjinta. Shariar yau itace wadda ake saka ran zaa yanke hukunci dan haka dukkaninsu kowa jikinsa yake a mace babu iya dago kai ya kalli dan uwansa jimami da ciwo me radadi ne yake cike kirjin kowannesu, Kowannensu halinda Jannah zata shiga a rashinsu ne yake cin ransu da kuma rashin sanin me zasuje su tarar a gaban ubangijinsu akan abinda suka aikata sbd sun riga sun saddakar ga hukuncin kisan da zai iya hawa kansu. Bayan gama gabatar da sauran jawabai da manyan lawyers sukai da duka abinda aka hada dana fili da wanda akai bayan fage kotun tayi tsit a lokacinda babban alkali yake gabatar da hukuncin karshe na case din. "Bisa bayanai da dukkanin shedu na fili dana rubuce tareda kundun bincike da tabbaci da komai akan case din kotu ta yankewa dukkanin likitoci da Nurse da sukai aikin hukuncin kisa ta hanyar rataya banda Dr Ammar Zad wanda dukkanin bayanai da likitocin da aka saka suka dubasa sun tabbatarda baida cikakkiyar lafiyar kwakwalwa maana baida hankali dan haka Dzad,Maheer zad da Ammar Zad Zasuyi zaman shekara Daya gidan yari tareda aikin wahala me tsanani na horo a gidan yarin hakama kotu ta karbe dukkanin abinda suka mallaka na koina dan biyan diya ga rayukan da aka salwantar da hanyarsu hakama har abada kotu ta soke lasisin karatun Ammar zad na likitanci harma da sauran...." Jannah da zuciyarta ta dena bugawa a farkon maganarsa ta yanke hukuncin kisa ga likitocin jin banda Ammar zubewa qasa tai tana fasa wani irin kuka mai tsananin gaske ma samun dawowan rayuwarta daidai sbd saura kadan ta rasa ranta daga wannan hukuncin wanda ya sumar da dukkaninsu su Dad din suma sbd jin hukuncin da suka dauka hadda Ammar wanda bazasu iyaba zasu gwammaci a rataye su su dukan. Jin badashi ba Maheer ya fasa wani irin kuka mai tsuma zuciya daya saka Dad rungume Ammar jikinsa na tsananin rawa take ma yaji zuciyarsa ta kasa daukan mummunan shock din da suka shiga na dan lokaci ya dafe kirjinsa jikinsa na neman sakewa daga na Ammar din wanda ya kwata kwata baima cikin hankalinsa shi. Rungume jannah Ummah tayi da sauri tana fasa kuka itama ganin yanda jannah ke kukan tsananin ciwon daya danne kirjinta wanda ta tabbatarda Saleem Zad yabarsu tinda aka yankewa Ahalinsu wannan hukuncin me sassaucin da sun tabbatarda akwai abinda akai. Kukan farin ciki da tsananin ciwon zuci ne takeyi lokaci daya tareda tinanin tayaya zata iya fadawa su Dad Sun rasa saleem shima wanda har abada bazai dawoba sun rasasa kaman Mimi. Anny kuwa yanke jiki tai ta fadi a gurin hakama dr ken wanda take yafara shure shure zuciyarsa na neman bugawa, Hakama dr Abraham a rana daya zaa ratayesu dashi da 'dansa acan tasu qasar suma wanda ahalinsu ke cikin tsananin tashin hankali mai girma. Ammar zuri yayi baima da abin fada ko yi sbd ba komai yake ganewa ba ko fahimta wasu lokutan. Tattarosu akai zaa fita kotun dasu jannah ta miqe da sauri har tana faduwa ta nufesu da gudu ta kamo hannun Dad dinta da ake riqe dashi baya iya tsayuwa sbd hawan jininsa da yayi mummunan tashi. Da hannuwanta biyu dake tsananin

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});