Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 115

Chapter 115

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

aure dakin mijina kawai zan ringa shiga karna sake shiga na kowane namiji sai nasa" Mama cikeda mamakin falaq din tace "To wannan nasihar datai miki wayace miki ana fada?baa fadawa kowa gaskia ta fada miki" Basusan da isowansa ba sai zancensa sukaji wanda ya sakasu yin tsit Fiddausi na hadiye hadiyarta da sauri tana kama kanta. "Wane mara hankalin ne ya sakata fadawa yarinya hakan? Fuskansa a daure take sosai bacin ransa na bayyana a cikin sautinsa dayake fita a natse ya kalli jannah din wadda ta kasa dagowa Yace "Wane kalan tarbiya ne kikazo dashi? So nawa zan fada miki tarbiyanku dana mutane ba daya bane, Kinsan inda maganganunki zasu kai tinaninta? Meya hadata da maganar zuwa dakin miji a wannan shekarun? Ke tin kina yarinya qarama aka nuna miki xuwa dakin mijin ne or wat?? Like seriously?? Mama ce ta katsesa da cewa "AZIZ me kake fada haka? Tana bata tinani me kyau ne ai sbd tintini ya kamata ta dena shiga dakinka anyhow, Ta girma ya kamata tafara sanin ta girma hakama tin a yanzu ne ya kamata tasan baa shiga dakin kowane namiji saina mijinta idan akai mata aure shima" Hawayen da jannah ta kasa barin su saukone ta hadiye su ta maqoshinta suka wuce mata da wani irin daci ta kasa dagowa. Shi kuwa maman ya kalla yace "Mama duka wannan zancen ba yanxu ne lokacin yinsu ba, Tana buqatan kiyaye kalan namu tarbiyan da dabiun dasu basuda shi banason zance kowane iri yana shiga kunnen Falaq din" Falaq jannah din ta zubawa ido itama nata idanuwan na cikowa da hawaye ta miqe ta koma gurinta tana rungumeta ta dago ta kalli daddyn nata tana bata fuska. Mama ma tausayin Jannah din taji duk ya rufeta amma bata ji zafin AZIZ din sosaiba sbd ganin take bai saba da kowa na saka masa hannu ko baki bane a tarbiyan yarsa bayan ita da sayd dasu kadai ne suke masa discipline nata. Fiddausi silalewa tai tabar palon jiki a mace Sayd ma dayake tare dashi shiru yayi sbd ba hurumin shigar kowa bane bayan maman sai kuma falaq da itama take iya sakasa da hanasa. Cikin karfin hali jannah ta dago tana hadiye damuwa da radadin zuciyanta tana nunawa mama ba komai bayan barinsa gurin. Falaq zuwa tai ta cire uniform dinta taqi sake fitowa dakinta har lokacin cin abinci yayi taqi fitowa karshema rufe dakinta tayi. Tin Fiddausi na daukan abin wasa har taga dai da gaske take take hadda su kuka sosai dan haka ta fito ta sanarwa su jannah da mama. Jannah ce ta nufi dakin ta ringa Knocking tana kiran sunanta cikin kulawa da rarrashi. Qin budewa tai wanda hankalinsu ya fara tashi sbd kuka takeyi sosai taqi magana. Jannah hankalinta mugun tashi yayi sbd tana gudun AZIZ din yaji ta sake wani laifin dan haka ta ringa rokon falaq din akan ta bude amma sam taqi. Mama tasan zaayi hakan daman Falaq din na wannan sakarcin har sai Daddyn yamata abinda takeso idan ba hakan ba haka zata qi fitowa ta dagawa kowa hankali. Basu san abinda yake faruwa ba sai da ya dawo kusan 10 na dare ya tararda Fiddausi da jannah din tsuru cikin damuwa. Ko kallan inda suke baiyiba ya wuce hanyarsa yana duba time. Sayd ne ya kalli Fiddausi yace "Lafiya dai?akwai abinda yake faruwa ne? Hanyar da AY yabi Fiddausi ta saci kalla tace "Falaq ce tin bayan magrib tana daki ta rufe tanata kuka sosai kuma tin dazu ma munji shir.......... Cak din da AZIZ din ya tsaya cak sbd maganarta tsaf a kunnensa ta saka ya saka Fiddausi kasa qarasawa tana sauke kanta qasa. Shi kansa Sayd din da sauri ya juya ya kalla ko AZIZ din ya shige ya gansa yana sauya hanya zuwa bedroom din Falaq wanda jannah ke can tsaye tin dazu idanuwanta duk sunyi ciki ita kanta tana cikin tsananin buqatan me kulawan da ita tai kalan tausayi jikin yayi tsananin sanyi sbd tasan itace zata hadiyi baqin cikin akan wannan lamarin. Jin qamshinsa da taku a bayanta ya sakata janyewa gefe tana juyowa taga shi dinne kuwa fuskansa babu sauki ko kadan. Tsayuwa yayi a bakin kofar ya ambaci sunan falaq da muryansa kai tsaye. Kafin ya sake kiran falaq din juyowa yayi cikin zafi ya kalli jannah din ransa na quna yace "Babu abinda kika daidai ne a rayuwanki ke?? Idan ta rufe kanta kusan awa biyar me amfaninki da bazaku nema mutane ku fada musuba? Cikin tsananin sanyi da mutuwan jikinta datake jin zazzabi sbd wahalar tsayuwa da buga kofa ta bude baki a sanyaye tace "I'm sorry" Kaman tafasashen ruwa haka yaji muryanta datake bayyanarda itama ciwone a jikinta na sauka a zuciyarsa, Da karfin gaske ya buga kofan yai wa falaq din kira daya daya saka falaq din mugun firgita sbd bata taba jinsa hakan ba. Ita kanta Jannah sarawa kanta yayi sbd faduwan gaba ta dafa bango. Acan ciki kuwa falaq ciwonta ne ma ya tashi jin tai kaman numfashi na gagara shiga cikinta, Bugun zuciyarta tsananta yayi sosai har tana jin azabarsa ta dafe kirjinta tana jin abinda bata taba jiba. Saukowa tai daga gadonta bata gani sosai jiri na dibanta tana son isa kofar sedai ko taku uku bataiba ta zube a tsakiyar dakin. Jin faduwanta a qasa ya sakasa juyawa da sauri yace Sayd ya kawo keys. Da gaggawa aka kawo keys ya bude dakin Ganinta zube qasa ya sakasa jin kansa gabaki daya ya dauki zafi da saurin gaske ya isa gareta ya dauketa cak yana sayd yayi sauri ya kira likita. Jannah ma tashi hankalinta yayi taji gaba daya ta rasa kuzarin jikinta ta rabe gefe tana kallan yanda falaq komai nata baya motsi. Sayd da sauri ya fidda wayarsa yana ficewa daga dakin ya saka kiran sabuwan dr din da suka samu anan din mace da namiji ta bangaren ciwon falaq kawai. Ganin ya rasa taimakon da zai bawa falaq din ya saka jannah zuwa bakin gadon tafara taimaka mata ganin numfashinta bai tsaya gaba dayaba sbd tayi karatun bada taimakon gaggawa a Greece sbd yanayin ciwonta hakama Ammar ya koyar da ita abubuwa da dama sbd koda wani abin zai sameta ba kowa dan basa wasa da lafiyanta sam. Yanda takeyiwa falaq dinne cikin taka tsantsan da kulawa ya sakasa kallanta yana jiran jin wani abu daga gareta sbd ganin falaq din tana dan kokarin daidaituwa a yanda kirjinta ke wani irin ja. Baa dauki lokaci irin sosai dinnanba dr Sameera ta iso tareda wata nurce. A lokacin mama data shige tini ta fito duk suna palo cikin damuwa Fiddausi idanuwanta sunyi jajir sbd Kauna ce me karfi da shakuwa kamar uwa da 'ya itama a tsakaninta da falaq sbd shayar da ita ne kadai bataiba amma duk wata dawainiyar falaq itace meyi tin falaq na zanin jariranta. Jannah ma a zaune take sanyaye zazzabi me karfi ne itama yake cinta na walaha. A gidan dr Sameera ta kwana Sai Falaq ta farka. Dr Sameera kwararriya akan aikinga kuma mace ce Kyakkyawa mai kyan jiki da tsari tareda ilimi sosai kuma tin ganin farko Allah itama ya jarabceta da kaunar AZIZ LIMBA wanda bai taba mata

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});