Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 156

Chapter 156

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,206 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

biya 09033181070 Or mtn vtu at 09032345899*_KALBIM_* _Mamuhgee_ 94 *SHOP WITH ME by RANO* 08030811300 Best children's clothing shop💯 https://chat.whatsapp.com/Gk4H76TlRgyAAWIWgx3Jo7 Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema. Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta. *********** Hanyar gida suka nufa Jannah na sake bude fuskan matar da kyau daga hijabin dayake rufe fuskanta sbd ko akwai wanda zai ganta daya santa ya tafi da ita gida sbd tana tsoron tafiya da mahaifiyar wasu gurinta azo ana nema karshema aga laifinta da daukanta. Tafiya suke sakeyi me tsayi matar na sake riqe hannun Jannah cikin nata sosai kamar itace karamar yarinya jannah kuma uwarta, Yanda take qanqame hannun jannah din cikeda tsananin kauna da kasa iya barinta ya saka jannah juyowa da jajayen idanuwanta ta kalleta tana jin inama hannun tata mahaifiyarne take riqe dashi a hakan da tabbas dukkanin quncinta da baqin cikinta ya yaye. Gap da magrib suka isa gidan zuwa lokacin dukkaninsu sun tsananin gajiya dan haka zaunawa jannah tayi a tsakiyar dakin bayan ta shiga toilet ta debo musu ruwa a fanfo tafara bawa matar wadda tasha sosai itama sha tai ta xauna tana hutawa ahankali kafafunta na wani irin radadin gajiya. Sallah akai har aka fito masallaci tukuna ta iya tashi ta nufi toilet ta shige tayo Alwala ta kama matar itama takaita toilet da taimakonta tayi komai suka fito tare suka tada sallah sai yazamana kamar itace take jagorantar matar sallah sbd yanda ta ringa binta. Suna gamawa abincin data bari na cin darenta kafin ta fita ta janyo ta ajiye musu a gabansu ta kama hannun matar ahankali ta saka mata a ciki tana bude baki Ahankali tace "Kici abinci" Zuba mata idanuwanta masu tsananin kama dana 'yayanta matar tai cikeda kaunar jannah din da batasan ta inda take kwararo mata ta bude baki da muryanta me bayyanarda batada cikakkiyar lafiyar kai tace "Umminah kici, Umma tace kici" Dagowa jannah tai da idanuwanta dake sauyawa sbd yanda tai maganar kaman Mimintata take taji kewar uwarta idanuwanta suka ciko da hawaye suna gangarowa ahankali. Hannuwan Umman rawa suka dauka ta dorasu akan fuskan jannah tana goge mata tana cewa "Umminah bata kuka" Tsananta gudu hawayen jannah sukai tana rife idanuwanta ahankali tana tana share mata hawayen hankalinta na tashi jikinta na rawa sosai. Rikicewa Umman ke neman yi kanta na juyewa wanda ya saka Jannah bude idanuwanta tana dago hannunta ahankali ta dora akan na Umman dayake kan fuskanta tanata goge mata hawayen ta bude baki Ahankali tace "Jannah ce,jannah ce ba ummi ba, Ummi bata nan........ Bata qarasa ba Umman tayi baya da sauri tana kama kanta da hannuwanta biyu tana buga sosai tana girgiza kai da karfi koina jikinta na rawa tana cewa "Umminah zata kaini gurin hamma, Idan ba Umminah bace ki kaini gurin hamma, Gurin hamma nakeson zuwa, Ina hamma Abdul dinmu nida Umminah, Hamma yana can yana fada kullum mun fita yawo, Ya hanamu yawo, Ki kaini gurin hamma na fada masa Umminah batanan..." Yanda take buga kanta da karfi tana ambatar koma waye hamman da ummin ya saka Jannah tasowa da sauri tayi kanta tana kokarin riqota ta ture Jannah din da karfin gaske wanda ya sakata buguwa da bango har saida goshinta ya fasa kadan ta rintse idanuwanta cikin tsananin azaba amma bata taba gurin ba sbd Umman ta fara jiwa kanta rauni sbd yanda take yakushin fuskanta tana kiran Hamman da tsananin so da kaunar datake saka jannah fara hawaye tana sake komawa kanta da sauri batai wata wata ba ta rungumeta sbd dukkaninsu suna cikin qunci daya ne na rashin mutane mafi soyuwa a rayuwarsu. Yanda ta rungumeta da karfi ya saka duk yanda umman take tureta tana dukanta amma bata saketaba har saida Umman ta fasa wani irin kuka me tsananin karfi da radadin dayake cin zuciya da ruhinta tsawon shekarun gararanbar neman Hammanta da umminta datake yi batareda cikakken hankalinta haryanxu ya dawo jikinta ba duk da kuma ba tuburan take haukarba, Tayi yawo states da dama gurin nemansu, Ta kasa tina komai na rayuwarta bayan Hamma Abdul dinsu itada Ummi, Ta kasa tina ita kanta wace, Ta kasa tina ita wace,daga ina ta fito, Ina ne gidansu, Inane garinsu, Tayi yawon gidajen abinci tana aiki amma daga lokacinda aka fahimci ba cikakken hankali ne da ita ba haukanta yi takeyi tana tashi korarta akeyi, Idan abin ya kwanta baka taba sanin tanada juyewan hankali lafiya kalau zata samu aiki amma da zarar angane shikenan zaa sallameta, A wani kauye tayi rayuwa me tsayi sosai inda maigarin kauyen ya aureta duk da batada hankalin shi dai tai masa ta kwanta masa yana kaunarta, Bai taba komai da ita sbd magani da aketa nemar mata tsawon shekaru har Allah ya dauki ransa yabar duniya bata warke ba dan haka yayansa da matansa suka koreta ta sake shiga duniya wanda duk tsawon wannan lokacin bata taba dena ambatar sunan 'yayantaba. Jannah sake qanqameta tayi tana jin nutsuwa itama ayau ta samu wanda ta runguma tana sauke hawayen samun sassaucin abinda yake cin rayuwarta na tsananin kadaici da qunci. Ahankali Umman tafara rage kukanta yanayin qasa tana ambatar sunan Ummi wanda ya saka jannah amsawa dole sbd bata damar dawowa hayyacinta har ta dena kukan tayi shiru a jikin Jannah wanda itama tayi shiru babu me motsi a cikinsu har akai ishai suna hakan. Ahankali jannah ta janye jikinta ta miqe ta kamata suka koma suka sake alwala suka dawo sukai sallah Suna idarwa abincin ta sake janyowa ta kama hannunta ta saka mata a cikin abincin suka fara ci Ahankali kowannensu jikinsa a sanyaye har suka gama. Tattara gurin jannah tai ta shiga toilet tayi wanka ko data fito Umman tai bacci daga inda take zaune cikin tsananin gajia da zazzabi. Cikin tausayi jannah ta gyara mata kwanciyarta kafin itama ta saka doguwarta har qasa ta bacci taxo ta kwanta gefenta suka rufe da abin rufa guda duk da ya musu kadan. Kaman yanda akace mutum rahama ne hakan ne ya faru ga jannah sbd ayau datake tareda da wani ba ita kadaiba kaman yanda ta saba bacci ta samu yau din ya dauketa har safe wanda rabonta da hakan ta manta. Da asuba sallah sukai suka sake kwantawa Umma ta ringa baccinta hankali kwance Jannah ta zuba mata idanuwanta ahankali tana kallan fuskanta kafin ta gangaro da idanuwanta akan hancinta da gurbin idonta datake samun Kammanin wanda yake maqale a zuciyarta a lungu ta boyesa boyo na har abada da bazata fidda ba kuma bazata farfado ba. Numfashi ta sauke ahankali wasu hawaye masu dumi na gangaro mata na Saleem da har abada bazata yafewa limbas ba idan suka raya tasu yar ta hanyar rabasa da tasa rayuwar. Meyasa saleem zai mata hakan? Meyasa ya zabi barinta a lokacinda tafi komai da kowa buqatarsa, Rashinsa ya sakata jin rashin tsoro da shakkar janyo matarda

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});