Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 100

Chapter 100

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

fitowa saiyaji ya dan samu sassaucin tsananin dacin dayake ransa. Bude baki yayi cikin kulawa da nutsuwa yace "Karkiyita murna da yawa tareda tsalle tsallen nan banason wasa da lafiyanki kin sani so ki kula sosai okay? Gyada kai tayi tana cewa "Zanyi amma daddy pls when zata taho? Bai amsa tambayarba ya wuce palonsa yana jin mama na kiranta. Yana shigewa cire babban rigan jikinsa yayi tareda zame kayan duka sbd ya samu sakewa. Wani wankan ya sake yi ya sauya kaya zuwa qananun kayan D&G bai fitoba ya kashe wayoyinsa dan hutawa. Su mama kuwa bikinsu sukeyi cikeda farin ciki da kwnaciyar hankali sbd su anty maryam duka da iyalan Alh Saad din dana Alh Ahmed duka suka gidan anata taya mama murna. Sayd ma shigewa yayi dan hutawar sbd Uban gidansa na hutawa ba wani aiki. Dayake Fahad ma a mansion din ya sauka shi kam yana cikinsu mama da mutuniyarsa falaq kafin daga baya ya fita zuwa wani guri. ***Karfe 4 da mintina Ammar ya farka yana fara motsawa Mimi da jannah dake dakin har lokacin sukai saurin yi kansa mama na ambatar sunansa tareda kamasa ya tashi zaune ta rungumesa da sauri hawaye na gangaro mata na tsananin kaunarsa me karfi da tausayinsa. Jannah ma hawayen ne suke gangaro mata tana kasa dagowa ta kallesa tana jin tsananin tsanar zuciyarta data kasa riqe amanar shekara da shekaru, Ammar bai cancanci hakan daga gareta ba, Taci Amanarsa taci amanar kanta sbd ta sani har abada wanda aka aura mata din bazai taba sonta kamar Ammar ba wanda zai iya vada rayuwarsa akanta. Kansa da yayi masa tsananin nauyi da zafi ya dan dafe kafin ahankali ya bude idanuwansa da sukai jajir alamar baccin dolen da aka sakasa zuciyarsa bata hutaba ko kadan. Akan jannah ya saukar da idanuwansa ya kafesu akanta yana mata wani irin kallo zuciyarsa na karban wani azababben yanayi me tsananin ciwo da radadi, Tinda Allah ya saka masa tsananin son jannah tin tana cikin mahaifiyarta har isowanta duniya da gwagwarmayar neman lafiyarta zuwa yanzu bai taba kawowa ko a mafarki ko tinanin Jannah zata iya zamowa matar wani ba duk duniya bayansa, Da ransa da lafiyarsa da hankalinsa da tinaninsa aka daura auren jannah da wani yana kwance yana baccin Asara da baqin cikin da aka sakasa sbd cimma buri batareda an dubi nasa halinda zai shiga ba a rashinta.... Rintse idanuwansa yayi sbd wani irin radadin daya yanki zuciyarsa da kirjinsa yana kasa riqe radadin ya rintse idanuwan. Mimi jin saukan hawayensa masu wani irin tsananin zafi taji a bayanta wanda tajisu tamkar sun sauka a zuciyarta ne dan haka bata san lokacinda ta fasa qaramin kuka me sautiba dan tasan babu a duniya abinda zaa fadawa Ammar din akan wannan lamarin ya sassauta radadinsa, Anyi masa illar da har abada bazai warke ba sedai samun sasssauci, Jannah ganin hawayensa zubewa tayi qasa tana fasa kuka itama tana son ambatar sunansa amma baqin cikin kanta datakeji ya hanata fada. Gangarowa hawayensa keyi ahankali akan bayan Mimi datake rungume dashi kafin jikinsa ya fara rawa ahankali yana kakkarwa ta sake qanqamesa da karfi tana girgiza masa kai tana cewa "Ammar no pls, No pls, karka bari ka shiga wani hali zuciyana bazata iya daukaba" Dad ne ya bude kofar dakin ya shigo Maheer na bayansa suna ganin ya farka suka qaraso kowannensu idanuwansu na kansa. Yanayinsa ya saka Maheer saurin isa garesa ya janyosa jikinsa ya qanqame yana kokarin hana jikinsa jijjigan dayake yana jin zuciyarsa na karyewa. Dad ma qarasowa yayi daidai lokacinda Ammar din ya rikice gabaki dayansa komai na jikinsa rawa yake idanuwansa a rintse yana sake qanqame Mimi maheer kuma na sake qanqamesa. Cikin sauri Dad ya kalli saleem daya shigo dakin yace ya kira dr. Da sauri saleem ya ciro wayarsa yana kokarin saka kiran. Daddy mahmoud ma qarasowa yayi dakin cikin damuwa da kulawa yana kallan Ammar din yace Maheer ya cire masa Cardigan din dake jikinsa. Mimi da maheer dinne suka cire masa a lokacinne jikinsa ya sake gaba daya. Maheer cak ya daukesa tareda nufar toilet da sauri Dad ne ya kunna masa ruwan dumi aka zaunar da Ammar din har lokacin maheer na riqe dashi dan haka ruwan su biyu yake jiqawa shima dad din kusan ya jiqe amma dai basason Ammar yana passing out sbd likitarsa data bada umarnin hakan a dena barin yana suma. Cikin ruwan Daddy mahmoud ne da jannah suka shiga ruwan lokaci daya suna girgizasa tareda kiran sunansa cikin tsananin kulawa da son ganin idanuwansa sun bude. Qara gudun ruwan Dad yayi sosai Maheer na sake riqesa da kyau. A cikin qanqanin lokaci gabaki dayansu suke neman zarewa da tashin hankali da firgici sbd Idan aka cire son ran da sukai masa wannan karan to kaf familyn bayan jannah babu wanda ake tsananin so irin Ammar din sbd jinin Zeynab ne da basu hadata a duniyarsu da komaiba, Su kansu a yanzu sun rasa gane wace kaddarar ce takaisu ga wannan lamarin wanda basusan Abinda Allah ya boyeba a cikinsa sai kuma Allah ya kaddara jannah din saita fara auren wani wanda ba Ammar ba. Koda Dr ya iso Ammar din bude idanuwansa daqyar jajir wainda bama ya ganin komai dishi dishi yake gani hakama sama sama kunnuwansa kejin sautin sunansa dasuke ta ihun kira. Akan jannah ya tsayar idanuwansa baya ganinta sosai amma yanajin sautin kukanta da yanda take kiran sunansa. Sake rufewa idanuwansa sukai aka cirosa Maheer ne ya sauya masa kaya bayan kowa ya fice ya kwantar dashi a gadonsa da Jannah ta gyara da sauri hannuwanta na rawa tukuna dr yafara dubasa. Palonsa suka koma suna jiran fitowan likita da Maheer dayake ciki shika suna jin kaman su tattaro likitocin abujan kaf suzo su dubasa. Dr ya dade sosai a ciki kafin komai ya daidaita ya fito yana musu bayanin yanda zaa kula da kiyaye Ammar din kafin ya wuce. Dukkaninsu kaman masu zaman makoki haka suka koma tareda manta hidimar bikin da ake gashi dare ma yayi baqi duka sun watse batareda anma tina da maganar kai amarya ba hakama ta bangaren AZIZ din babu wanda yai maganar zuwa daukan Amaryan. Sallan magrib suka fice yi aka bar Ammar din ya huta sbd yanzu baccin nutsuwa ya samu. Mimi ma sai lokacin ta koma dakinta tayi wanka da ruwan zafi sosai jikinta ya sake tai sallah tukuna aka kawo mata abinci da tea me zafi wanda tea din kawai tasha. Jannah ma bedroom dinta ta koma ta kwabe kayan jikinta tai wanka ta sauya kayan zuwa riga da wando masu fadi sosai da kauri tai sallah ta zauna tana adduar Allah ya kawo musu sassaucin wannan kadaddarorin dasuke afko musu daya bayan daya ya maidasu rayuwarsu ta baya. Kowama bayan dawowa sallah wanka sukai suka sauya kaya zuwa na shan iska basu fitoba sai lokacin ishai suna dawowa sallan angyara dining amma basu wani ci abinci ba kowa yawanci tea da snacks yaci sai Saleem ne ma sai Anny sukaci abinci me nauyi. A lokacin ne Ammar ya tashi Mimi da jannah ne sukai feeding dinsa abincin da bai wani ciba amma dai yasha tea sosai shima. Sallah Mimi ta taimaka masa yayi

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});