Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 142

Chapter 142

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

masu aiki gabaki daya kowa jikinsa a sanyaye yake. Daman kwana zaune akai gidan likitoci na kan Falaq din. ***acan asibiti suma kwanan zaune sukai sbd Ammar daya rikice hakama Dad ba sauki ko kadan ga Mimi zuciyarta ta fara kasa dauka, Maheer na ya zaunar da ita ya sanar da ita qasar zasu bari gabaki dayansu. Shiru tayi zuciyarta na wani irin sanyi da ciwo duk a lokaci daya wanda a wannan karan batajin soyayya zata hanata bude idaniwanta ta tsaya tareda familynta da sukai sacrificing komai akanta, Numfashi me zafi ta sauke ahankali tana hadiye wani irin daci da ciwo ta kalli Maheer tace "Na Amince zan biku mu tafi bazan sake waiwayan baya ba" Dad ne ya sauke numfashi ahankali cikin ciwo na jin dadin abinda ta fada, Maheer ma numfashin ya sauke yana jin samun sanyi da saukin nauyin kirjinsa. Hudu na yamma likitoci da nurses din mahaukatan daya gayyato daga lagos jirginsu ya sauka daga airport kai tsaye motocin asibitin Mahaukatan nan abuja ce tazo ta daukesu tareda motar jamian Drugs da babu me alamar yasan imani a acikinsu suka isa asibitin Zaadens. Suna isa dakin da Ammar yake kwance an dauresa a gado abi na farko wani mahaukacin mari Wani Dan drug ya fara kashesa dashi wanda ya saka haukarsa daukewa ta wucen gadi. Motocin police ne kusan guda biyar suka iso asibitin take guri ya cika aka hargitse. Wani mummunan daurin azaba akaiwa Ammar kamar goro yana ihun tsananin azabar da bai taba ji ba aka fito dashi tareda takardar asibitin mahaukata zaa kaisa ta lagos. Duk tsananin ciwon dad saida ya tashi daqyar suka fito dukkanin familyn suna roko da neman taimako cikin mummunan tashin hankali da fita hayyaci. Maheer ayau kuka yakeyi kaman mace a gaban tarin mutane amma wani ball da akai dashi saida ya fasa goshi. Dad ma kuka yakeyi sosai kirjinsa na tsananta ciwo. Mimi kuwa yanke jiki tai ta fadi saleem yayi kanta. Jannah kan maheer tayi tana goge masa goshinsa daya fashe da hannun rigarta idanuwanta jajir. A dakin da dad yake aka kwantar Mimi dan haka dukkaninsu sunyi shiri zuciyoyinsa na ciwo da tarin baqin cikin daya rufesu, A rayuwarta soyayyar AZIZ LIMBA itace mummunan kaddarar data afkowa rayuwarta harta tarwatsa mata family ayau sike cikin mummunan halin dasuke buqatan dauki. Tayi danasani da baqin Kamuwa da soyayyar wanda bai taba sonta ba qarshen iyayenta kawai yakeso batareda laifin komaiba, A yau tayiwa kanta alkawarin ta hakura da rabuwa da aurensa, Idan ita yar halak ce zata cire soyayyarsa har abada bata buqatansa... Miqewa tayi ahankali ta fice daga dakin taba jan kafafunta daqyar. Gate ta nufa idanuwanta jajir ko gani sosai batayi ta tari mota ta shiga ahankali tana rufe idanuwanta bayan ta sanar dashi idan zai kaita. Ahankali ta miqa hannunta ta dora akan zuciyarta dake bugawa da tsananin ciwo da quncin datake jin yana sake ciketa tako ina. ko data iso gidan security da sauri suka bude mata gate ta shigo tana tafiya cikin quncin daya rufe idanuwanta. Ciki ta shigo babu kowa a main palo sai Fiddausi data ganta ta qaraso cikin tsananin sanyi tana mata sannu da zuwa amma sam Jannah batajinta sbd nisan datai a cikik matsanancin qunci da tinani me ciwo. Kai tsaye dakin Falaq ta isa ta taddata kwance kamar wadda tai shekaru a kwance. Silalewa tai ahankali bakin gadonta tana fasa wani irin me tsuma zuciya da tsananin ciwo da radadin rabuwar da zatai da ita har abada batason su sake haduwa sbd haduwansu ba alkhairi bane garesu su dukan gwara kowa yayi rayuwarsa. Kukane tayi sosai wanda baida sauti ko kadan zuciyarta na tsananin ciwo tsawon lokaci kafin ta miqe ko gani batayi sosai ta fice daga dakin sedai batasaniba Falaq din ta bude idanuwanta itama Hawaye takeyi sosai batareda ta motsa ba sbd tsananin qunci da azabar ciwo take ji itama wanda yake sakata jin tsoron kamar mutuwa zatai. Tana fitowa kai tsaye palonsa ta nufa ta bude kofar ta shiga daidai fitowansa idaniwansa sun fada sosai a lokaci daya sbd tsananin damuwa da tsoron dayake bayyane a yanayinsa na tsoron rasa 'yarsa da itace rayuwarsa. Tsayawa sukai suna kallan juna ahankali tsana na tasowa ahankali tana rufe zazzzafar soyayyar dake qasan zuciyoyinsu, Ahankali ta tako ta tsaya gabansa ta bude baki tana kallan cikin idaniwansa tace "Meyasa? Why? Mun cancanta hakan daga gareka ne? Sbd zuciyana ta mutu akan soyayyarka ne ka zabi hukunta iyayena da yan uwana akan laifin daba nasu ba? Duka soyayyar danake maka ne ta jawo wannan? Wasu hawayen tsananin radadin zuciya ta hadiye ahankali tana cewa "AZIZ LIMBA kaje nayi freeing dinka daga Soyayyar da kake cutatar da ahalina akanta, Na cireka daga zuciyata bazan qara sonka har abada, Sadakata aka baka ayau ina rokonka ka jefar da sadakar da bakaso ka bani yancina na maka alkawarin har abada bazaka sake sakani a idaniwanka ba zan tabbatarda hakan sbd ni kaina bazan taba son sake saka ka idaniwanaba....... Jajir idaniwansa sukai tiririn dayake cin zuciyarsa na tafasowa ya jefa mata mummunan kallo tana ficewa daga rayuwarsa gabaki daya ya dago file din dayake hannunsa nata wanda zai bawa Sayd ayau a saki duniya tasan su waye zaadens ya jefa mata a fuskanta takardun duka watse gabaki daya a qasa. Cikin tsananin tsanar familynta datake juyewa harda ita yace "Yaushe kika samu bakin tambayar why? A zaadens babu me darajar da zai tambayeni na amsa harke din, Ki dena tambayar auren dayake kanki sbd tin farko ban daukeki mata ba kuma bazaki taba zama matar dani AZIZ LIMBA zan ambata da matataba, Amsa kikeso na abinda familynki sukai? Kije ki tambayesu zuciyar waye a kirjinki take harbawa? Ki duba ga takardu nan rai nawa suka kashe kisan gilla kafin su kashe mace me tsohon cikin da zuciyarta take bugawa yanzu haka a kirjinki, UMMITAH ABDULAZIZ LIMBA shine sunan, Shine sunan mahaifiyar data haifi Falaq, Shine sunan Qanwa kuma jinin AZIZ LIMBA daya dayake da ita a duniya da bustards dincan suka kashe sbd a raya waye????? Ke sarauniyar Zaadens da ranta yafi na kowa, Ummitah data raye da yarta da mijinta Sayd a cikin Aminci badan ke ba, Badan keba da yanzu Falaq tana raye tareda mahaifiyarta, Da yanzu yaya na yana tareda qanwarsa daya taso baida kowa sai ita, Itace rayuwata,itace gabaki dayan AZIZ LIMBA amma suka farka kirjinta suka rabata da zuciyarta sbd son zuciya and kin samu daman tambayar me sukai? Sarewa kafafun Jannah sukai cikin matsanancin tashin hankalin daya saka zuciyarta bugawa ta durqushe tana dafe kirjinta sbd tsananin azabar gaske takeji idanuwanta na neman rage gani. Falaq datake tsaye bakin kofar cikin rashin karfin jiki kunnuwanta suka ji mata kalaman da suka juya duniyarta lokaci daya jini ya fara biyowa ta hancinta ahankali kafin tausayi wani motsin harta bakinta yafara fitowa.... Mama ma data biyi bayan falaq din dataga wutowarta mutuwar tsaye tayi da abinda kunnuwanta suka ji mata amma ganin yanda jini yake fita baki da hancin Falaq tana yanke jiki ta fadi ya sakata ambatar sunan Falaq din cikin amon daya saka AZIZ kallan kofar yana yi kan falaq cikin mummunan halin dabai taba samun kansa a ciki ba. #MAMUH #THE STORY

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});