Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 22

Chapter 22

Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sosai. Sayyid kuwa dadi ya ringa ji dan baima damu da rashin tsayuwarsa a rayuwa ba sbd tsananin son dayakewa Ummitah da duk abinda ya shafeta. Bai taba ganin ABDULAZIZ ba amma kaunarsa yake mai tsafta da karfin gaske sbd irin tsananin son da Ummitah ke masa dan haka shima yake shirye daya bisa yayi masa biyayya har inda karfinsa ya qare. Ahankali ahankali ciwon laulayi ya koma ciwo a jikin Ummitah, Ga karatu wanda dole ta dena zuwa ga sanyi daya shigeta sosai kwata kwata cikin baizo da saukiba ko kadan dan haka mama taxo ta dawo da ita hannunta tana kulawa da ita. *******Rashin jinsu kwata kwata tsawon lokaci me tsayin gaske ya saka ya shiga damuwar data taba aikinsa wanda ya saka masa dawowa da abinda yake yi baya dan kuwa lalacewa komai yayi sbd damuwa dan haka dole komai aka dawo farko kuma ba damar tafiya sbd aikine da zai sauya rayuwarsa gaba daya idan yayi nasara dan haka dole ya dage ya tsaya wanda hakan ne ya haddasa masa daukan tswon lokaci meyawa na shekaru bai dawo ba. A cikin nasara da yardar Allah ya kammala tareda samun zuwa na daya wanda ya janyo masa wata irin suna da daukaka. Murna da farin cikin mutanensa dasu alh saad suka shiga anata celebrating tareda tayasa murna hakama kamfaninsa take ya samu shiga jerin kamfanin da aka dan san dasu. A lokacin ne babu bata lokaci ya tattara ya koma Italy daga can ko sati biyu baiyiba ya sauka Nigeria. Bai kwana a abuja ba ya isa garinsu sbd daukosu kawai yakeda niyar yi su dawo abuja. Lafiyayyan gida me kyau da tsari dan girma ya mallaka a abujan wanda babu abunda baa sakaba na jin dadin rayuwa wanda tin bai dawoba qasar aka gama komai na gidan da tsarinsa. Da rana kwatsam ya sauka a garin wanda motarsa ta saka jamaa taruwa a kofar gidansu mama. Ummitah dake zaune mama da sayyid na gefen suna kokarin ganin taci abinci da lemu da abarban data saka sayyid siyo mata sbd shima gaba daya ya haukace da nema sbd kulawa da ita da Buqatunta gashi kusan ya tare gidan maman shima sbd ita. Mama na dagowa ta kallesa saida gabanta yayi mummunan faduwa sbd gabaki daya baiyi kama da ABDULAZIZ dintaba Hawayene suka fara gangarowa daga idanuwanta masu tsananin zafi da batasan ma na menene ba. Ummitah kuwa qamshinsa daya cike tsakar gidan ta shaqa da kyau har cikin cikinta taji wani irin sanyi na mamaye zuciyarta zuwa gangar jikin. Itama hawaye ne suka fara gangarowa daga idanuwanta tana kasa dauke idanuwanta daga kansa duk da kuwa tsananin kwarjinin dayake dashi na cikar haiba. Sayyid hannuwansa biyu ya saka suna rawa yafara goge mata hawaye yana jiyowa yayiwa ABDULAZIZ din kallo daya ya sauke idanuwansa. Kwata kwata bai lura da cikin dayake jikinta ba sbd abine da bazai taba kawowa akansa ba koda kuwa mafarki fararen idanuwansa masu wani irin kyau ya zuba mata zuciyarsa na samun abincin datai shekaru bata samuba ya ware mata hannuwansa ahankali tareda ambatar sunanta da wani irin sautin daya sakata fasa kuka tana miqewa da karfin da sayyid baitaba sanin ayanzu tanada shi ba sbd rashin lafiya ta tinkaresa da gudun gaske ta fada jikinsa yai wata kyakkywar runguma yana rintes idanuwansa wani irin farin cikim dayafi komai na rayuwarsa na rufesa. Mintina sukai ahakan yana sauke ajiyan zuciya ita kuma tana kuka sosai tana kankamesa tana ambatar sunansa kaman zata bude masa zuciyarta yaga irin abinda takeji na kewansa datai da tsananin Buqatansa datake. Mama ma kuka takeyi sosai wanda ya sakasa sassauta riqon da yayiwa Ummitah jin wani wani irin tudu ya dan tokaresa. Bude idanuwansa yayi ahankali tareda zubawa mama yana kasa sakin Ummita wadda itama ta sake qanqamesa. Wani irin ciwon kai yaji ya sara masa a tsakiyar gefen kansa ya lumshe idanuwansa da suka dan sauya ya bude yana zare Ummitah a jikinsa ahankali. A gabansa ya tsayar da ita ya zubawa fuskanta datake sunkuye tana kuka ido yana mata kallan daya saba mata duk yazo na karantar meye ya sauya a tattare da ita. Tin daga fuskanta yaji zuciyarsa na nauyi yafara gangaro da idanuwansa har zuwa cikinta daya fito qarami dashi. Kaman cikin haihuwa yake gani a jikinta wanda yasan imaginations nasa kawai dan haka ya dago ya zubawa fuskanta ido yana son ta kallesa amma ta kasa dagowa sai kuka tasake sakarwa. Mama data kasa dagowa ya mayarwa da kallansa sai lokacin ya lura da sayyid daya taho ya tsaya gefensu yana kallansu cikeda kauna da burgewa tareda rashin son kukan Ummitah. Mama ce tayi karfin halin dagowa tanai masa sannu da zuwa share hawayenta ta nufi daki dauko masa tabarmarsa da haryanxu bata taba fiddawa wani ya hauba sbd dan shi suka siyeta. Tana saka kafarta daya daki kafin ta saka dayar ya kasa shiru da muryansa me nutsuwa da taushi yace "Mama meye wannan a jikin Ummitah?? Cak ta tsaya agurin batareda tayi gababa ko baya tana sauke numfashi da ajiyar xuciya me sanyi kafinta juyowa ahankali kai tsaye tana daukan matsayinta na uwa ba shakka tace "Juna biyu ne a jikinta ga mijinta nan a tsaye ku gaisa bara na dauko maka gurin zama" Tana fadar hakan ta qarasa wucewa ciki tana sauke ajiyar zuciya da numfashi sbd ba amfanin boye boye da tashin hankalin abinda ya riga ya faru ba sauyi kaddararsu taxo ahakan. Shiru gurin yayi wani irin mummunan nauyi kansa yayi da maganar tareda wani irin nauyin kirji daya kusa taba ganinsa dan haka tabarman data shimfida ya qarasa baya gani sosai ya zauna yana kasa kallan maman sai Ummitah da rayuwarta ta riga ta lalace dan haka take idanuwansa sauya zuwa wani irin jajir kaman an zuba musu borkono. Maganan bayan rabuwa da barka da zuwa mama ke masa amma kwata kwata baya jinta jinsa gava daya ya dauke iska kawai yake ji kaman yana kada masa hakama ganinsa yara rawa dan haka bai fahimci komai sosai ba saida Ummitah ta gama kukanta ta dago ta kallesa ta fahimci kwata kwata baya hayyacinsa ma kuma maganar aure da cikin ne yake neman zarar dashi kuma tasani babu abinda zai hanasa raba auren dan haka cikin sanyin murya ta bude baki tace "HAMMA inasonsa zanci gaba da zama dashi" Rintse idanuwansa da suka kusa watse masa yakeji yayi da qarfi wani nauyin gaske na danne kirjinsa. Sayyid daya shiga damuwa da tsoro numfashi ya sauke me sanyi yana kallan Ummitah da shi gava daya ganin ABDULAZIZ din ya tsinkar dashi. Mama ma numfashi me sanyi ta sauke sbd a baya kam daya dawo da wuri yace zai raba auren bazata hanaba amma yanxu ga rabo ansamu kuma ace zaa raba auren bame yiyuwa bane. Mama ce ta karbi zancen kai tsaye da cewa "Sayyid yaron kirki ne kuma yana kaunar matarsa da abinda yake cikinta dan haka ba abin damuwa bane ga abinda Allah ya kaddaro, A matsayina na uwa gareku ina umartanka da kada kace komai ka karbi hukuncin Allah da hannu biyu" Bude idanuwansa yayi suna sake sauyawa kirjinsa na wani irin radadi me ciwon gaske sbd mata uku dayake so fiyeda komai a rayuwarsa da

Table of Contents

Chapters

163 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
  120. 120 Chapter 120
  121. 121 Chapter 121
  122. 122 Chapter 122
  123. 123 Chapter 123
  124. 124 Chapter 124
  125. 125 Chapter 125
  126. 126 Chapter 126
  127. 127 Chapter 127
  128. 128 Chapter 128
  129. 129 Chapter 129
  130. 130 Chapter 130
  131. 131 Chapter 131
  132. 132 Chapter 132
  133. 133 Chapter 133
  134. 134 Chapter 134
  135. 135 Chapter 135
  136. 136 Chapter 136
  137. 137 Chapter 137
  138. 138 Chapter 138
  139. 139 Chapter 139
  140. 140 Chapter 140
  141. 141 Chapter 141
  142. 142 Chapter 142
  143. 143 Chapter 143
  144. 144 Chapter 144
  145. 145 Chapter 145
  146. 146 Chapter 146
  147. 147 Chapter 147
  148. 148 Chapter 148
  149. 149 Chapter 149
  150. 150 Chapter 150
  151. 151 Chapter 151
  152. 152 Chapter 152
  153. 153 Chapter 153
  154. 154 Chapter 154
  155. 155 Chapter 155
  156. 156 Chapter 156
  157. 157 Chapter 157
  158. 158 Chapter 158
  159. 159 Chapter 159
  160. 160 Chapter 160
  161. 161 Chapter 161
  162. 162 Chapter 162
  163. 163 Chapter 163
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});