Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 99

Chapter 99

Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

nake, muna haka naji tsayawar mota a kofar gidanmu wanda hakan ya tabbatar min da cewar Jibril ne kuma daman yana kusa da unguwar a lokacin da ya kira. “Ga Jibr.. Il nan... Yace tafiya zai yi da Noor” Na fada muryata na rawa. “Ki fita ki fada masa gaskiya dole ne ya sani” Inna ta umarceni, tashi na yi na fita ina hawaye, nasan Jibril ba zai yarda ba amman ya zama dole na fada masa, ko da na fito yana jingine jikin motarsa yana danna wayarsa da alama ni zai kira. Fitowata tasa ya dago kai ya kalleni yanayin yadda na ke tafiya na doso shi yasa ya kunna fitilar wayarsa ya haska fuskata. “Karki fara min complain ba gurinki na zo ba Wallahi, kawai zan dauki dana ne kuma nasan idan ban zo da kaina ba ba zaki bari taje ba, and i need to be with my son” “Jibril.... Noor ...... Noor” Na kasa magana saboda kukan da ya ci karfina. Ya sakar min ido sosai yana son jin abunda zai fito daga bakina. “Noor ya bata....” “What? How?” Na kasa magana sai kuka na ke. “Look Nawwara, idan ma kin shirya hakan ne dan ki samu nisanci da ni to wannan ba hanya ba ce, dan zan iya jure komai ban da rashin Noor, dan Allah ki canja tsari” “Wallahi ba wasa na ke ba Noor ya bata” Ya tsaya kallona dan tabbatar da zancen da nake gaskiya ne ko akasin haka. “Kamar ya Noor ya bata bata ya bata ya bata as how?” Ya tambaya yana mai daga murya tare da hannyensa sama, ni kuma sai kuka na ke ina ta kokarin rufe baki. “Ki daina wannan banzan kukan naki ki fada min yadda aka yi dana ya bata” Na razarana sosai saboda yadda ya katsa min tsawa da kuma irin bacin ran dake cikin muryarsa. “Da suka fita da Bilal shine suka tsaya Agg mall siyen chocolate sai ya nemi Noor ya rasa” Ya yi dariya marar sauti “Ki ce Bilal ya sace min yaro ya siyar ko kuma ya boyeshi ya nemi kudin fansa” “No Bilal ba zai yi haka ba, Wallahi Bilal ba zai taba cutar da Noor ba” “To wa zai cutar da shi waya batar da shi a yanzu?” Ya fada a tsawace. “Wallahi Bilal ba zai cutar da Noor...” Hannunsa ya daga zai mareni sai kuma ya kaiwa gilashin motarsa bugun yana wani irin huci. “Akan dana zan iya taba kowa Nawwara kuma kowa da kowan nan har da ke, idan kin san wani abu ne kula da Bilal tau ki gaggauta kanwace shi tun wuri” Yana fadar hakan ya bude motarsa ya shiga ya bar ni nan tsaye ina aikin kuka, sai ga Sakina ta fito da gudu ta nufi hanyar Babban gida, ni kuma na juya na koma, ko da na shiga Inna na ta buge bugen waya tana kuka kamar yadda Jidda take. Ko da tara na dare ya yi gidanmu ya cika da jama'a makota da kuma yan uwa, maza suna suka shiga gari inda ake sa ran za a ganshi har Agg mall din anje amman ba a ganshi ba, ko da Baba Sulaiman ya aika Sakina ta kira masa Bilal sai ta dawo ta fada mana cewar wai yana police station an tafi da shi tun dazu, kowa yayi mamakin wanda zai kulle Bilal a wannan lokacin sai da Baba Sulaiman da Inna suka fada cewar Jibril ne, a ranar duk wanda yake cikin gidan nan ya tabbatar da cewar Noor yana da Uba. Ni da Inna da Mama turai da Baba Sulaiman da Sakina da kuma Jidda muka kwasa muka je station din, daidaikun mutanen unguwa suka bimu saboda gulma. Mun tararda Jibril a can sai mahaifin Bilal da mahaifiyarsa tana ta kuka, sai wani kanensa daya. “Ina Bilal din yake?” Inna ta tambayi Mahaifinsa sai ya amsa mata cikin rashin dadin rai. “Yana can ciki sun ce ba zasu fito da shi ba, tun dazu muke a nan tsaye babu irin rokon da ba mu musu ba” “Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un” Cewar Inna, ni kuma na doshi gurin Jibril sai yayi saurin tashi ya fice daga station din, da gudu na bishi ina kiran sunansa daker ya juyo ya kalleni fuskarsa babu annuri. “Minene” “Wallahi ba Bilal ba ne ya sace shi” “Ke kika sace shi” “Wallahi ba Bilal ba ne, dan Allah ka kyale kasan yan sandan nan basa da mutunci zasu iya ji masa fa” “Ke ta Bilal kike ni kuma ta da na nake, babu ruwana da alakarku ya fito min da da na ya zauna lafiya” Yana fadar hakan ya bude motarsa ya shiga ya barni nan tsaye. Wasa wasa aka kwashe kwana uku ana abu daya, Jibril ya ki bari a saki Bilal saboda yana zargin shi ya batar masa da da, ita kuma mahaifiyar Bilal da yan uwansa suna dora laifin akaina, a ganinsu ko da da gaske Bilal ya batar da Noor ai be cancanci a ayi masa irin wannan wulakancin ba, har fade take wai danta be taba zuwa cell ba sai dalilina, babu irin magiyar da bana ma Jibril amman kullum maganarsa daya Bilal ya fito masa da da, ni da shi baka iya tantance waye ya fi shiga damuwa, sai dai Jibril ya fini shiga tashin hankalin sosai saboda haukacewa yake kokarin yia kan neman dansa, har mahaifinsa sai da ya zo har sokoto saboda wannan maganar Noor, kullum mafarki na Noor sai dai har yanzu zuciyata bata zargin Bilal. Ranar talata ranar da mahaifin Jibril wato Alhaji Baahir ya yasa a kashe maganar gurin yan sanda muna station mu dukanmu Jibril ya saka Bilal gaba yana masa magiya har da kukansa. “Dan Allah dan Annabi Bilal ka fada min inda da na yake? Idan kudi kake so ka fada min zan baka ko nawa ne, kuma Wallahi na maka alkawari ba zan bari a ama ka komai ba, amman Noor shi kadai ya rage min ka tausaya min Bilal dan girman Allah” Bilal ya kasa magana sai hawaye yake, gaba daya kamaninsa sun canja. “Wallahi Bilal be dauki Noor ba” Na fada cikin kuka, sai mahaifiyar Bilal ta kwatse ni. “Ke dan Allah can rufewa mutane baki, baki fada tuntuni ba sai yanzu tsohuwar munafuka, ko da yake Allah ya kara ai kai ka ce ka ji ka gani” Ban kara mata magana ba, har muka fito station din, muna dawowa gida sai ga Jibril ya iskoni har gida be tsaya a waje ba ya shigo cikin gidanmu da sallama ba tare da ya nemi uzinin shiga ba, ban tabbatar da irin ramar da yayi ba sai a wannan lokacin idanuwansa sun fada sosai. Gaban Inna ya je ya risina yana hawaye kamar karamin yaro “Inna na rokeki ki saka Nawwara ta fada min wani abu akan batan da na, shi kadai ya rage min a duniyar nan, yau kwana hudu kenan ba a ga Noor ba, duk wanda ya dauke ke Noor rayuwarsa yake so ba kudi na ba, da kudi nane da yanzu an kira an ce na bayar, babu inda ban duba ba, babu irin binciken da ban sa anyi ba amman an kasa ganin Noor”

Table of Contents

Chapters

119 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});