Chapter 105
Chapter 105
tare da yin murmushi. Ina tunanin Mustapha ya yi min haka ne saboda bakinciki ya yi min yawa a tunaninsa zan ji zafi idan ya ce ya samu wacce yake so duk da nasan ba zata wuce Jidda ba domin alamu sun nuna hakan, ko rantsuwa na yi bana kaffara Mustapha ya so Jidda ne kuma zai aureta ne saboda na ji bakinciki tun da aminiyata ce, kuma yana son bakinciki da nake ciki na rashin lafiyar Noor ya karu akan kishi ne saboda na ki shi, ni kuma na kasa damuwa saboda daman can bana son shi kuma ina ganin sonshi a idanuwan Jidda dan haka sun fi dacewa da juna duk kuwa da kasancesar ta kasa fada min ne saboda karna zargeta ko kuma na yi tunanin wani abu. Basu wani dade sosai ba Mustapha yasa hannunsa aljihu ya dauko kudi mai dan dama ya aje mana saman gado tare da yi mana addu'ar Allah kara lafiya, sannan ya yi gaba sai na kamo hannun Jidda ya riketa har sai da ya wuce sannan na kalleta na ce “Amintakarmu ta fi karfi mu boyewa juna abu” “Nawwara ban yi nufin boye miki ba, kawai ban san yadda zaki kalli abun ba ne” “Ta fuska mai kyau zan kalleshi Jidda, na san ke aminiyata ce kuma ba zaki taba cin amanata ba, Wallahi ko da Mustapha be furta da kansa yana sonki ba zan hada soyayyarku saboda dacewar da kuka yi da juna, kuma ina ta tabbacin idan har ya aureki ba zai sake wata rayuwa marar kyau ba” “Ba a yanxurya kamata mu yi maganar nan ba Nawwara, ki kula da Noor please” Ta fada tana dafa kafadata sannan ta wuce. Ni kuma na dawo na zauna na saka Noor a gaba ina ta kallonsa zuciyata cike da tausayinsa. Misalin goma na dare Jibril ya dawo, yana shigowa dakin Noor na farkawa da kuka yana kiran sunana. “Momy Momy” “Gani nan” Na yi saurin kama hannunsa. “Momy sun yanka ni wasu sun ce zasu kashe ni” Sai Jibril ya yi saurin karasowa ya kama dayan hannunsa kuma ya shafa kansa. “Shiiiiiiiiiii you're safe kana kusa da Momy da Daddy babu wanda zai taba ka” “Daddy sun ce sai sun yanka ni sun yanka min ciki ma, kuma sun buga min kai” Sai kawai yasa dariya. “Ashe Noor dina ba jarumi ba ne, kadan fa suka yanka ka, kuma na sa police sun kama su” Matsawa ya yi sosai ya kwanta gefen Noor ya rumgumeshi ya matse hannunsa cikin nasa. “Allah ya baka lafiya ya raya min kai Noor kai kadai ka rage min sai Abbah na” Tashi na yi na fita wajen kiran likita saboda ya ce idan Noor ya farka a kirashi. _________________________________ Ku yi hakuri da wannan 🙏🙏🙏. [11/14, 4:00 PM] Farar Mace...: *RAI BIYU...♥🖤* Wattpad @KhadeejaCandy 5⃣6⃣ A GURGUJE.... Bana tunanin Bilal yana da wata hujja ko dalili na yin fushi da ni, duk kuwa da kasancesar Jibril ya sa an daureshi kuma an masa kai wulakanci da kasa guguwa a fuskar yan uwansu, amman idan har zai min adalci babu hannu a ciki balle kafata, sai dai shi ya kasa fahimtar hakan domin tun lokacin da abun ya faru zuwa yau be taba daga waya ya kirani ba, idan kuma na kirashi sai ya dinga min magana cikiciki kamar baya son magana da ni, sau uku Baba Sulaiman yana daukar mutane suna dubashi bayan sallamoshi daga asibiti, ni kan ban jeba domin Inna taje ba bata dawo da farin rai ba duk da bata fada min abunda suka mata ko suka ce mata ba, na fahimcin hakan ne a fuskarta da kuma yanayinta. Al-hamdulillah sauki yana ta zuwa ma Noor ta ko ina domin a farko ya firgita sosai har na dauka ko kwakwalwarsa ta tabu ne, sai dai kulawar da likitocin Uduth da kuma addu'o'in da muke sai komai ya daidaita, tiyatar da aka masa ma cikin sati biyu ya samu sauki su kansu sun yaba da irin kyau fatar Noor, yana samun kula sosai da sosai wani abun da Jibril yake masa har mamaki yake bani kamar zai dauke sa ya cinye, a dan zaman da muka yi na asibitin Noor har ya sagarce abu kadan zai fara kuka yana kiran Daddynsa. A zaman da mukayi asibiti sau biyu Jibril na aman jini a gabana abun har sai da ya bani tsoro domin na dauka zuciyarsa ko kuma hanjin cikinsa zai amayar gaba daya, sai dai shi sai ya nuna kamar be damu ba, da alama abun ya zame masa jiki. Ana gobe za a sallamemu daga asibiti muka yi zaman kotu na karshe akan case din Baba a ranar na sha mamaki ashe matar da ta lakawa babanmu sata yayar Siraj ce daamn ina ganin alamaun haka sai dai ban tabbatar da sai yau da aka yanke hukunci na karshe, saboda yan uwan Siraj da suka zo sune wadanda aka tsaya masa a lokacin da aka yi shigar kotu ta farko case dinsa. Hukunci kazafi alkalin ya yanke mata su kuma aka yanke musu hukuncin kisa bisa ga shaidu da hujjoji kwarara da aka gabatar gaban kotu. Na yi farincikin sosai da sosai a wannan ranar daga ni har Inna da duk wani mai son ganin na kwatowa Baba hakkinsa, na yaba ma dpo daya tsaya kai da fata wajen ganin ya bi mana kadin mu. Abunda ya faru abun mamaki ne kuma abun a yabawa masa ne domin ba ko wane dan sanda bane zai kashe mutum kuma an hukunta shi kamar yadda doka ta ce, a ranar na ji kamar na zuba ruwa kasa na sha saboda farinciki mutane na ta zuwa har gida suna mana murna. Washe garin ranar aka sallamo Noor daga asibiti, a abun mamaki sai ga Zinatu ta zo ganinsa wani sukuku da ita kamar ba ita ba, na yi mamakin ganin ta zo gida dubashi bayan bata taba zuwa asibiti ganinsa ba. Da fari jajanta mana ta farayi akan abunda ya faru sannan ta dora da bayaninta. “Na san zaki yi mamakin rashin zuwa ganin Noor asibiti ko? Wallahi Jibril ne ya hanani, saboda na kirashi ina jajanta masa abunda ya faru sai ya gargade akan karna yarda na kusanci dansa, saboda yana ganin akwai aminci da shakuwa sosai a tsakanina da Siraj wata kila yana zargin zan masa wani abun ne” “Ayyah kin san dole ne ya tsorata kuma ya yi taka tsantsan saboda abubuwan da suka faru” “Amman ai ba halina daya da Siraj ba, miyasa zai yi tunanin haka” “Ban da abinki Zinatu ai shi hali ba a fuska akae ganeshi ba, shi ma Siraj din ai bamu dauka cewar zai yi haka ba, ni kaina a yanxu ba kowa zan yarda da shi ba balle kuma shi” “Haka ne, ni kaina da be koremu daga kamfanin ba, na kudiri aniyar aje aikin domin ba zan iya aiki inda ake ɗari ɗari da ni ba” “Ya sa kun aje aikin ne?” “Eh kwana biyu da faruwar hakan duka ya canja ma'aikatan kamfanin, yanxu kuma yana nan yana daukar wasu” “Ayya abun be yi dadi ba sorry” “Ba komai Allah kara lafiya, amman gaskiya Siraj ya bata mana suna Allah ya isar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119