Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 7

Chapter 7

Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel 1,206 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

natsuwa a tare da ita idonta ya kumburo kamar ba nata ba. “Ina kika je Habiba?” A maimakon ta amsa ni sai kawai ta jefomin wata tambayar. “Inna na nan tsakar gida?” Kai na girgiza mata alamar a'a ina kallon yanyinta. Baya na yi hakan ya bata damar shigowa cikin gidan, hankalinta be kwanta ba sai kalle-kallen tsakar gidan take kamin da wuce ɗaki da sauri. Cikin rashin kuzari na rufa mata baya, ina shiga cikin ɗakin sai ta kama hannyena ta danƙa min sababin kuɗi ƴan dubu-dubu. “Nawwara ga dubu ashirin ɗin nan kije ki kai su saki Baba, daga baya sai a biyata kuɗinta” Wani jiri na ji ya kamani na kasa riƙe kuɗin, suka suɓuce daga hannuna suka watse ƙasa. Ita kanta ta tsorata da yanayi da sauri ta soma yin baya-baya tana fashewa da kuka. COMMENT AND SHARE *RAI BIYU...♥️🖤* Wattpad @Khadeeja_Candy 6⃣ Faɗuwa na yi saman guiwoyina na kai hannu na taɓa kuɗi, kamin na tada kai na kalleta. “Habiba ina kika samu wannan kuɗin?” “Tsinta na yi” Ta faɗa cikin kuka mai ƙarfi. Miƙewa na yi tsaye na matsa kusa da ita ina nunata da yatsa. “Karki raina min hankali Habiba, ta ya zaki tsince dubu ashiri a wannan halin?” Na faɗa ciki wata murya da ban san ina da ita ba. Sai ta rufe bakinta ta matsa baya. “Kyauta aka ba ni” Na watsa mata wani irin mahaukacin mari. “Ba ƙaramar yarinya ba ce ni, karki yi wasa da hankalina” “Mustapha ne ya ba ni” Ta sake faɗa tana dafe fuskarta saboda zafin marin da na yi mata. “Mustapha” Na maimaita sunan, tabbas Mustapha zai bata fiye da dubu ashiri, zai iya bata miliyan ma, amman idan ta ba shi mutuncinta. “Ya taya mutuncinki ne ya baki kuɗin ko kuma kin riga kin siyar masa ne?” Na tambaya gabana da dukan shida-shida, zuciyata kuma na ala-ala idan bata siyar ba. “Na siyar... Nawwara idan ba haka na yi babu inda wannan kuɗin zai fito, ki duba halin da Baba yake ciki, babu ruwan kowa da mu” Baya-baya na yi har sai da na jingina da ƙofar ɗakin. “Habiba kin kashe mu, ya kike tunanin Inna zata yi idan ta ji wannan abun? Kina tunanin wannan abun da kika aikata zai burge Baba? Da wane ido zaki kallesu” Da sauri ta ƙaraso kusa da ni ta riƙe hannuna tana kuka har muryarta na karkarwa. “Dan Allah karki faɗa musu, saboda su na yi wannan abun idan suka yi fushi da ni Wallahi mutuwa zan yi” “Kin san da wannan kika je kika siyar da mutuncinki? Allah da ya samu cikin wannan hali shi zai mana mafita, kina kunyar iyayenki amman baki kunyar Allah ki? yanzu ina kika son na ce mun samo wannan kuɗin?” Risinawa ta yi a gurin da cigaba da kuka mai taɓa zuciya. Sallamar Jidda ce ta razanar da mu daga ni har Habiba ɗin. Da sauri na fita waje domin na tareta karta shigo, na manta da hawayen da ke fuskata har sai da Jidda ta min magana. “Nawwara kuka kike yi?” Nasa hannu na share hawayen yayinda wasu suke ƙara zubo min, kuka ya zama biyu a yanzu. Hannu ta kama ta danka min dubu uku. “Ga dubu uku ku ƙara” “Ke kuma ina kika samu wannan kuɗin?” Na tambaya muryata na rawa. “Wayata na siyar vivo” A maimakon na yi mata godiya sai kawai na fashe da kuka, hakan ya karantar da ita ba wannan ne kawai damuwata ba, lallai da akwai wani abun a ƙasa. “Nawwara ko dai wani abun ya faru ne?” Ɗurƙushewa na yi a gurin na fashe da wani sabon kuka, har su Sakina suka yo kaina. Hakan yasa na katse kukan na miƙe tsaye na kama hannun Jidda muka shiga ɗaki. “Jidda Habiba ta siyar da mutuncinta ta kawo dubu ashirin” Na faɗa ina nuna mata kuɗin. Ita kuma ta ɗora hannu saman kai tana faɗin “Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Inna ta ji? ” “Bata sani ba, amman yanzu dole zata sani idan ta ga wannan kuɗin” “Habiba miyasa kika yi haka?” Jidda ta tambaya hawaye na bin fuskarta. Habiba kan aikin kuka kawai take, ta ma kasa ɗaga ido ta kalli Jidda. “Ina zaku ce kun samo wannan kuɗin Nawwara?” “Nima ban sani ba” “Karki faɗawa Inna, bari na je da kuɗin ni nasan yadda zan yi” Duƙawa ta yi ƙasa ta tsince kuɗin ta fita. Har na cira ƙafa zan bita sai Habiba ta kirani cikin muryar kuka. “Nawwara” Juyowa na yi na dawo. Sai ta tashi zaune “Dan Allah karki faɗawa Inna” “Ba zan faɗa ba” “Idan na yi tafiya ba zata ga ne ba?” “Ba zaki ita tafiya ba ne ba?” “Gurin zafi ya ke min sosai, bana iya haɗe ƙafafuna da kyau” Wani ƙololon bakin ciƙi na ji ya ratsa zuciyata. Cikin rashin ƙwarin jiki na fita waje na kunna wuta na ɗora mata ruwan zafi, Sakina kuma na ce su je su siye wani abu su ci da kuɗin da Baba Sulaiman ya basu. Sai da na cika mata roba da ruwan zafi sannan na zuba mata wasu a bota, da kaina na kai mata banɗaki, naje na riƙo ta kaita banɗakin. Tana gurin wankan Inna na ta dawo, fuskarta da alamun damuwa tun daga yanayin sallamarta na lura da hakan balle ma lokacin da ta zauna kusa da ni. “Kin dawo” Na tambaya ina ƙoƙarin ɓoye hawayena. “Eh mun kai musu kuɗin amman sun ce sai an cika sauran, ba su bar mu mun ganshi ba” “Allah yayi mana mafita” Na faɗa ina sauƙe ajiyar zuciya. Yayinda idona ke kallon Habiba ta tsaya tana leƙon. Na san tsoronta ɗaya kar Inna ta gane halin da take ciki, ina baƙin cikin halin da Habiba ta faɗa da ƙananan shekarunta ni kaina mai shekara ashirin da huɗu mutane kan kirani da ƙaramar yarinya balle ita mai sheƙaru goma sha bakwai. Tunanin dabarar da zan yi ma Inna ya ɗaukr hankalinta har Habiba ta samu ta wuce na ke, sai ga Jidda ta shigo kamar ta san ina nemanta. Saman tabarma ta zauna tana gaishe da Inna, ko da wasa Jidda bata kalli inda na ke ba, sai kawai ta fara jerawa Inna irin ƙaryar da data tsara. “Inna ga dubu ashirin na kawo, na siyar da kayan Kitchen ɗina ne, Maman Nura ma bata sani ba kuma idan ta ji zata min faɗa, dan Allah karku faɗa mata, inyaso idan Allah ya kawo sai ku biyani” Ya ƙarasa tana danƙawa Inna dubu ashirin ɗin, Inna ta saki baki. “Haba Jidda ayi haka?” “Zan iya muku komai Inna ni dai ki rufa min asiri karki faɗawa Maman Nura” “Ba zan faɗa ba, Allah ya saka miki da alheri ya biyaki da aljanna, ya baki miji na ƙwarai” Da ido na yi ma Habiba magana akan ta zo ta wuce saboda hankalin Inna ya ɗauko kan kuɗin, sannan na amsa da “Amin Jidda mun gode Allah ya bar zaman tare” “Ba komai ai yi ma kaine” Inna ta kalleni. “Ai ban ga ta zama ba ni kan, bari na je na samu Sulaiman mu kai musu cikon kuɗin ko?” “Inna ana kiran magariba kuma? Da dai kin haƙura har a

Table of Contents

Chapters

119 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});