Chapter 104
Chapter 104
babu wanda ya zauna, Jibril ya matsowa kusa da shi sai Dsp din ya shiga tsakani. “Ba sai ka taba shi, ai hukunci za a yanke masa dai dai da abunda ya aikata, abun jindadi ma ya amsa laifinsa da kansa, kuma mutane da muka kama a gidan da aka aje Noor sun fadi cewar shi ya saka su kuma be karyata ba” “Ba komai zan masa ba tambayarsa kawai zan yi” Jibril ya fada yana jin kamar ya kama wuyan Siraj ya shake. “Mina hana maka Siraj? Mina maka ka aikata min haka? Me ka nema na hanaka? Mi Rabi ta maka? Me Noor ya maka?” Ya dago kansa da idanuwansa da suka kumbure saboda duka, har baya iya gani da idon sosai gaba daya an canja masa kamani kamar ba shi ba. “Baka min komai ba Jibril sai alheri, ni kaina ina jin rashin kyautawa a abunda na aikata, sai dai babu yadda zan yi saboda zuciya ta dibeni tun farko, abun da na ke ta kokarinyi da gani na fika Jibril, saboda ina bakincikin ace ni ne a karkashinka ba kai ne a karkashina ba, irin rufin asirin da Allah ya baka na so na samu da karfi sai ya gagara, na sa an kashe Rabi ne saboda ta tona min asiri ta ci amanata kuma na san nima kasheni za ayi, a a yayinda ita kuma za a yafe mata kuma za a yaba mata, Noor ya ganni lokacin da na yi kokarin kasheshi shiyasa na sace shi nasa a kashe shi saboda kar wata rana ya fadi sai gashi Rabi ta lalata komai” “Hassadace ta cuce ka Siraj ka ci amanar kanka kuma daman hassada ga mai rabo taki ce, mun dauki amana mun baka sai ka cuce mu Allah ya waddaranka Siraj” Cewar Abbah cike da bacin rai. Jibril ya matso kusa da shi ya chakumi wuyansa ya matse game yana kokarin aikashi lahira, daker aka kwaci Siraj a hannun Jibril har aka wuce da shi Nawwara kawai yake harara idonshi na kanta. “Ka kwantar da hankalinka Jibril kotu za ta yi komai, litanin din nan muke son fara zaman kotu alkali zai yanke masa hukuncin ai” Cewar Dsp yana rike da Jibril ta dake ta faman huci. Daga gidan maza station suka wuce saboda wasu statement din Nawwara da za a dauka. Sun yi awa daya a gurin sannan suka baro gurin tare da tawagar yan sanda zuwa rinjin sambo gidan wani dan'uwan Rabi da take zaune a gidansa. Ko da suka je sun tararda jama'a anyi dandazo a gurin duk kuwa da kasancewar an rufe gidan gaba daya kuma sun bar police uku da zasu yi gadin gurin. Suna isa police din suka bude musu gidan, Nawwara ce a baya tare da Jibril, ya yinda Dsp yake can gaba tare da su Abbah da kuma wasu police din. “Are you sure zaki iya kallon gawar Rabi? Ance fa dadsatsata suka yi” Tsayawa ta yi cak sai ya kalleshi. “Idan kin san zai daga miki karki kalla” Sai kawai ta fashe da kuka. “Duk laifina ne” “Ba laifinki ba ne, haka Allah ya tsara” Kamin ta kara cewa wani abu sai ga wayarta tana ringing, Baba Sulaiman ya kira ya ji inda suke ya zo, da kanta ta tsaya tana masa kwatanci sai Jibril ya shiga ciki ya bar nan waje tsaye. Shi kansa da yaga gawar Rabi sai da hankalinsa ya tashi domin datsata aka yi aka mata guntu-guntu ko ina ya bace da jini, suna cikin gurin su Baba Sulaiman da wasu kanenn mahaifin Nawwara suka iso, isowarsu ta yi daidai da isowar yan uwan Rabi kana kallonsu zaka gane ba hausawa ba ne dukansu yanayin shigarsu da kuma tsagen da ke fuskarsu, da kuka suka shiga cikin gidan maza uku mata biyu a nan suka yi ta ihu har da mai faduwa tana tashi tana buga kasa. Daker suka tsagaita kuka har aka dauko gawarta aka fito da ita zuwa motar police. NAWWARA POV. Ana fitowa da gawarta hankalina ya tashi sosai lallai mai rai ba komai ba ne, duk kyau rabi da far'arta sun tafi kenan, a gurin na raina kaina saboda ina ganin kamar sakacina ne yasa hakan ta faru, amman Jibril ya yi kokarin dorawa kansa laifin ko kuma ya ce min haka Allah ya tsara zai faru, mahaifin Jibril ne yaso a tsaya a yi mata jina'iza a nan amman yan uwanta suka ki, a dole tasa ya hakura ya bawa police kudin mai dan su rakasu har can kogi inda iyayenta suke, a ranar yan uwanta suka juya suka koma a mota tare da gawarta da kuma rakiyar yan sanda. Mahaifin Jibril kuma muka dawo asibiti tare da shi ya duba Noor ya yi masa addu'a tare da step mother dinsa, sannan ya yi mana bankwana akan cewar zai koma abuja a yau gobe tun da safe zai hau wani jirgin yaje kogi saboda ayi jana'iza a tare da shi, sosai ya so Jibril ya bishi amman Jibril ya ki wai sai yaga idon dansa, Abbah ya sashi gaba yana ta masa nasiha sosai akan rayuwa da kuma abubuwan da suka faru. Da yamma lis Abbah ya yi mana sallama ya bar asibitin kasancewar an kira an fada masa jirginsa ya kusa tashi. Mutane na ta zuwa ganin Noor makota da kuma yan'uwa da abokan arziki ciki har da wasu familyn Jibril da suke garin nan da kuma abokansa. Gurare takwas da rabi na dare Jibril ya bar asibitin saboda kiranshi da aka yi, ko minti goma ba ayi ba sai ga Jidda ta shigo tare da Mustapha i was very surprised dana gansu tare saboda ni na ma dauka Mustapha baya kasar nan dan tun lokacin da nayi magana da shi ban sake hada hanya da shi ba, hankalin Jidda ya tashi sosai har da kukanta Mustapha kan yana tsaye kan Noor yana masa kallon da ban san na minene ba. “Ya aka yi aka barku kuka shigo?” Na tambaya bayan Jidda ta zauna har yana kokarin bude abincin da ta zo da shi. Sai Mustapha ya kanne min ido daya yana murmushi “Cin hanci na bayar” Na sauke kaina kasa, sai ya yi yar dariya kadan ya ce. “Allah ya kara sauki ya tsare gaba, kai gaskiya an yi arziki da mun rasa yaro mai kyau, ni da nake son na hada surukuta da ke, dan gaskiya idan na haifi ya mace sai ta auri Noor ko kuma da na ya auri yarki” Ya fada yana dariya kamar babu abunda ya dame shi, ni dai bance masa komai ba, Jidda kuma ta kasa daga kai ta kalleni duk tabi ta tsargu. “Ba ganin danki kawai na zo ba Nawwara, na zo na fada miki cewar na samu matar da na ke so” Sai Jidda ta yi saurin kallonshi. “Haba Mustapha wannan wane irin magana ne, baka ga halin da take ciki ba? Ko ma minene ai ni ya kamata na fada mata” “Na ga kamar ba zaka iya fada mata ba ne, shiyasa ni na zabi fada mata da kaina” “Amman dai ba a yanzu ya dace ka yi wannan maganar ba” “Fine ba zan kara ba” Ya fada yana daga hannunsa sama
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119