Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 9

Chapter 9

Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

yaja baya, Baba Dahiru ya shiga duba Baba, Baba Sulaiman kuma ya fasa kuka yana faɗin “Sun kashe min ɗan'uwa ba bisa haƙƙi ba, Wallahi ɗan'uwana be yi sata ba, ya rantse min da Allah be ɗauka ba, sun ɗauki alhakin ɗan'uwana Allah ya isa Allah ya isa” Yasa taɓar rigarsa ya share hawayensa sai kuma ya faɗin a gurin yana kuka. Har sai dai sauran ƴan'uwansa suka riƙashi, sai ya fisge kansa ya nufi ƙofa yana faɗin. “Bayan sun karɓi dubu ashirin na beli sai kuma su kawo mana gawa, ba zata saɓuba” Baba Dahiru yayi saurin riƙeshi. “Sulaiman ina zaka je cikin dare nan?” Komawa yayi ya zauna yana rawar ƙafa alamun masifa na tare da shi. Inna A'i ce ta zo ta riƙa Inna ta tasheta daga gaban Gawar Baba ta maidata can gurin ƙofar ɗaki ta zaunar da ita. A nan suka shiga tambayar Sakina yaushe suka kawo shi, kasancewar itace mai wayo saman da Jamila, cikin in'innar kuka ta zayyana musu abunda ta sani. Ni kan ina zaune gurin kamar kayan wanki komai ina ganinsa kamar mafarki, har kuma lokacin babu hawaye a idona balle alamun kukan. Habiba na gefena tana rusar kuka. Can ƙasa-ƙasa na riƙa jiyo muryar Baba Sulaiman yana faɗin. “Sai da ya faɗa min suna ta dukansa akan sai ya karɓa laifinsa cewar yayi satar, shi kuma ya rantse min da Allah ba zai amsa ba sai dai su kashe shi, amman da naje na samu ƴan sanda nan na ce mu mun yarda yayi satar kuma za mu biya, daker suka yarda zasu ba da belinsa dubu ashiri, da yamman mu ka cika musu kuɗinsu sai kuma su kawo mana gawa? Shiyasa suka ƙi bamu shi, suka ce sai dai su kawo shi da kansu ashe sun san sun kashe shi, kuma suka karɓe kuɗin, Wallahi ba zamu bar wannan maganar ba, ba zamu barta ba” Faɗa yake cikin kuka kamar ba mace ba, sai yana buga ƙafarsa yake da ƙasa. Magana da shi ta ƙarshe a police station ne ya dawo min a rai. _“Mahaifinku be yi sata ba Nawwara, kuma be taɓa yi ba, ki gamsar da ƴan'uwanki da wannan”- A take na ji idona ya cika da ƙwalla, kan kace kwabo sai ga hawaye suna saukowa daga idona kamar ba gobe, ban san lokacin da na kwara wani uban ihu ina kiran sunansa ba. “Baba! Baba!! Baba!!!” Mama ladi ta zo da gudu ta rufe min baki, sai na faɗa hannunta ina kallon fuskarta da ke min gizo kamar ta mahaifina... *RAI BIYU...♥️🖤* Wattpad @Khadeeja_Candy 8⃣ Riƙani ta yi ta tayar ta maida can kusa da Inna ta zaunar tana bani haƙuri da kalaman da za su sanyayamin zuciya. Kuka muke ta yi ni da Habiba, yayinda Inna ta rafka uban tagumi tana kallon gawar Baba. Baba Dahiru ne yaja janena dake kan igiya ya rufa masa. Haka muka zauna har garin Allah ya waye babu wanda ya runtsa. Su Baba Dahiru ne suka yi alwala suka tafi masallaci yayinda mu muka yi namu sallah a gida, bayan na gama na ɗauko alƙur'ane ina karantawa, izuwa yanzu bana da buƙatar wani kuka bayan wanda na yi jiya ya haddasa min ciwon kai da kumburewar idanu, ina jin yadda maƙota na nesa da na kusa ke ta shigowa suna jajantama Inna, wasu na san gulma ce ta kawo su tun da gari ma be gama wayewa ba amman har labarin ya zaga unguwarmu da ma unguwanin da ke kusa da mu. Bayan fitowa Masallci sauran ƴan'uwan Babana suka shigo maza da mata cikin har da Yakumbo. masu kuka na yi masu faɗa na yi, Baba Ayuba ne ya bada shawarar a ɗauki gawar Baba aje da ita police station a mayar musu, Baba Sulaiman kuma ya hana wai ba za a tagayar masa da gawar ɗan'uwa ba, idan aka yi haka ɗan'uwansa aka wulaƙanta. Daga ƙarshe suka yanke shawarar zuwa station ɗin ba tare da gawar Baba ba, a ɗakin mu aka saka shi sai aka rufe ɗakin duk muka kwaso muka dawo ɗakin Inna. Noor ya zo kusa da ni ya zauna, Jamila da Sakina kuma suka zauna gurin ƙofa suna ta aikin kuka kamar yadda Habiba ke yi. Ni kuma ɓa noce kaina ƙasa bana kuka kuma bana tunani kaina kamar fanko na ke jinsa, shigowar Jidda da Mahaifiyarta ce ta ɗaga hankalin kowa, saboda kuka da take kamar ita akayi ma mutuwar, sai gida ya ɗauki kuka muryarta muryar Habiba da Inna sai kuma Jamila da Sakina. Yakumbo ce ta katsa musu tsawa tana faɗa kan kuka da suke, musamman Inna da take ganin ita ya kamata ace ta rarrashe mu amman ita take kukan ma. “Mamaci addu'a yake so ba kuka ba, bawan Allah nan fa yana cikin gidan nan amman kuna ta masa kuka, kuka ai ba zai dawo da shi ba, ba zai muku maganin komai ba, amman addu'a zata iya sanyaya muku zuciya kuma ta canja lamarinku, sannan shi kuma Allah ya karɓa yayi masa rahama. Yanzu ke Hajara ke da ya kamata ace kin bawa yaran nan haƙuri, sai ki zauna kina kukan tare da su, Allah be yi wani dan wani ba, be yi Musa dan ku ba kuma be yi ku dan Musa ba, shi ya hallita abunda yasa masa rai yanzu kuma ya karɓi abunsa, gode masa ma ya kamata ku yi kuma ku yi haƙuri sai kuga Allah ya yi muku wata mafitar” Ba laifi kalamanta sun yi tasiri gurin Inna da har tasa hannu ta share hawayenta tana ta kokuwar tsayar da kukanta, Habiba kan kunne uwar shegu ta yi sai abunda ya cigaba, kusa da ni Jidda ta dawo ta zauna ta kama hannuna ta riƙe sai hawaye take, ni kan kallonta kawai na ke ina jin kaina kamar babu komai a ciki. Tun da suka ta fi basu dawo ba sai ƙarfe goma na safe har da ƴan mintuna, mutane da suka je tun hasken alfijir ba gama yayewa ba. Tare da tawagar ƴan sanda suka zo wanda hakan ya haddasa mana dandazo jama'a a ƙofar gida. Dpo ne ya shiga da kansa ya duba gawar baba tare da wani ƙaramin ɗan sanda mai ɗaukar hoton jikin Baba, bayan ya gama dubawa ne ya dawo gurinmu, a bakin ƙofa ya tsaya yana ba mu haƙuri tare da faɗar za a ɗauki mataki da ya dace. “Wacan ƴarsa ce?” Ya tambaya ganin ni kaɗaice na kasa ɗago kai na kalleshi tun da ya soma maganar har ya gama. Inna A'i ta nuna Habiba da Jamila da kuma Sakina “Eh da wannan da wacan da wacan, su kaɗai Allah ya bashi” “Allah sarki ku yi haƙuri zamu ɗauki mataki, yanzu haka mun sa an kama ƴan sandan da suka yi wannan aika-aikar kuma za a gabatar da su a gaban kotu In'sha Allahu” Ya ƙarasa yana ciro duba goma da uku ya miƙawa Jamila da ke kusa da shi, kana ya miƙe tsaye yana mana sallama. “Mu za mu tafi Allah ya sanyaya zuciyarku” Na yi zaton ya tafi hakan yasa na ɗago idona da ke cike da hawaye na kalli ƙofa, karaf idona sai cikin nasa, sauke na sa idon yayi ya wuce ƴan

Table of Contents

Chapters

119 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});