Chapter 74
Chapter 74
ba” Ya amsa masa yana saka Laptop din a mota, juyawa Jibril ya yi ya koma ciki gurin mutumen dazu. “Please ko kaji inda zata je? Ko kuma inda hadarin ya faru?” Mutumen da dan yi shiru sannan ya daga masa kai. “Ee na ji ta ambaci Specialist Hospital gaskiya ina jin ko can aka kai yaron ko kuma can hadarin ya faru” “Thank you” Ya juyo da sauri ya nufi gurin motarsa, driver seat ya nufa ya ce direban ya fita ya hau achaba shi akwai inda zai je, @360 ya fisgi motar kamar zai tashi sama, wani irin vibration jininsa yake yana jin kamar ya runtse ido ya gansa a cikin asibitin. “Dan ta...” Yana ta maimaita hakan ya iso Abuja road sai ya dauke hanyar da zata sada shi da Specialist, gudu yake sosai kamar dan shi aka yi titi ko kuma ance masa babu ababen hawa sai nasa kadai. Lokacin da zai kunna kai a gate din Specialist din sai da ya yi kamar zai buge wani magidanci da ke kokarin fitowa. Ko fakin din kirki be yi ba ya fito yana ta waiwagen inda zai shiga, tsabar rude daman can sau daya ya taba shigo asibitin loacin da yake farkofarkon zuwa sokoto sika yi wata mata tiyata. Da sauri ya nufi emergency wajen yan hatsari, har ciki ya karasa ya karasa inda Nurses suke ya muna masu id cart dinsa sannan ya soma tambayarsu ko an kawo wani. “Eh an kawo mutun daya yanzu” “Zai kai minti nawa?” “Ten haka yanzu yanzu” “Babba ne ko yaro?” “Gaskiya dattijo ne” “No wanda na ke nema karamin yaro ne yana tare da mamansa ina jin za ayi awa daya yanzu da kawo shi” “Eh an kawo wani yaro dazu, yana ciki bayan shi ma an kawo wani” Dayar Matar ta fada. “Bari na duba” Ya nufi ciki da sauri ya soma bin dakuna, sai gashi ya hadu da wani likita abokinsa. Shi ya rike Jibril dan hankalinsa gaba daya sama yake baya ganin kowa. “Jibril” “Dan Allah wani yaro na kr nema wanda aka kawo ya yi hatsari dazu” “Yaro ne sosai?” Ya dan yi shuru yana tunanin ta yadda zai amsa tunda ba sanin yaron ya yi ba. “Yeah yeah yaro ne” “Akwai wanda aka shiga tiyata da shi yanzu akwai kuma wanda ya rasu dazu, amman ba a fita da gawarsa ba saboda basu biya hospital bill ba” “Wait...” Ya fada sai ya fiddo wayarsa ya kira Nawwara duk da yasan ba zata bari ya karaso ba, ringing biyu aka daga da muryar Sakina tana masa sallama. “Ina Nawwara?” “Bata da lafiya” “Wacece ke?” “Ni kanwarta ce” “Kuna ina ne Nawwara tana ina” “Muna nan asibiti?” “Wani waje?” “Dakin Balaraba” Ya katse wayar yana kallon likitan. “Ina ne sashen balaraba?” “Ta can ne, ko shine yaron da ake neman jininsa aka zo diban na uwar ta suma?” Jibril ya rike. “Please zan iya ganin yaron” “Yes this way, amman an shiga tiyata da shi gaskiya ba zaka iya ganinsa yanzu ba sai dai a jira ya fito” Tare suka karasa sashen da ake yan tiyata, jikin Jibril sai rawa yake sosai ya so ya shiga amman likitan ya hanashi saboda tiyata ake masa kuma yasan irin matsalar da zai janyo matukar ya ce zai shiga yanzu. “Ka yi hakuri da sun fito zaka ganshi” Safa da marwa kawai jibril ya ke yana matsar hannunsa. “Jini ma ake nema garin bada jinin ne Mahaifiyar yaron ta yi ta amai daman da kuka ta zo, sai gashi ta sume mana dole muka kaita sashem Balaraba, kakarsa taje ta siyo” “Please Doc Ismail muje ka gwada nawa idan zai yi” “Okay yaron ya ji ciwo sosai gaskiya ya zubar da jini, amman yaron ka ne ko naga kuna da kaman sosai kuma yadda ka tashi hankalinka haka...” Be gama maganar ba Jibril ya rike shi “Da gaske muna da kama? Da gaske?” Ya gyada masa kai cike da mamaki, ko da suka karasa lab Jibril be sani ba saboda hankalinsa yana can gurin tunani. Sai da aka dibi jininsa kadan aka gwada ya bada result iri daya da na Noor sannan Doc Ismail ya kawo masa, Jibril na ganin takardar hawaye suka fara masa zuba jikinsa ya yi mugun sanye, sai da ya karantar result din ya fi a kirga sannan ya yarda da duniya yake, fashewa ya yi da kuka sai kuma ya yi saurin guntse bakinsa tunawa da inda yake, saman table ya aje takardar ya nufi wani bangare na lab din hannayensa a baya yana jin wani irin abu marar misaltuwa. “Doc Jibril ko ka fasa bada jinin ne?” Sai ya juyo da sauri ya dawo yana share hawaye abunda ya bawa kowa mamaki, sai dai su abunda suke dauka saboda yaron ya ji rauni sosai ne yake hawayen, har wasu na cewa wai kamar ba namiji ba namijin ma kuma likita wanda be kamata aga yana kuka saboda sun saba ganin tashin hankali. Dakin da ake dibar jiki ya shiga ya kwanta a saman kujerar nan mai kamar gado, aka saka masa abun diban jinin aka tasti leda biyu sannan ya tashi yana fadin. “Doc Ismail muje yanzu ko sun fito” “No Doc kai kansa kasan dole ka dan zauna yanzu na ga kamar a hankalinka a tashe yake” Tashi tsaye Jibril ya yi da zimmar tafiya, ganin hakan yasa Doc Ismail ya bishi suka koma gurin tare sai suka tarar ba a fito da shi ba har yanzu. Sai kawai suka zarce inda Nawwara take domin itama yana da bukatar ganinta, basu sha wahala wajen nemanta ba saboda farko farko take. Irin dakinnan ne da ake jera masara lafiya dama da hadu, tana kwance saman gadon asibiti idanuwanta a rufe kamar tana bachi ga drip an daura mata a hannu, Sakina na zaune a kujerar da ke kusa da ita tana ta hawaye. Kallonta yake sosai cike da tausayinta a nan Sakina ita ta samu damar kallonsa a take ta raya a zuciyarta cewar tabbas wannan baban Noor ne domin kamar har ta ba ce. Zaunawa ya yi gefen gado yana ta kallon fuskar Nawwara kamar yau ya fara ganinta, can kuma ya dago ya kalli Doc Ismail dake ta faman kallonsa da mamaki ya ce “A sama mata daki inda zata zauna ita kadai ta samu kulawa, if babu zan so ka mata transfer zuwa asibitina” “No nan din ma akwai” Gurin Nurses din ya nufa ya yi magana da su sai suka zo suka canja mata daki zuwa wanda take ita kadai sai dai shi kudinsa da daban ne. A nan ma ya dade yana kallonta sannan ya cire rigarsa yar sama kasancewar suit ne a jikinsa ya lulluba mata saman jiki. “Ki kula da ita please” Ya ce da Sakina sai kace ita Nawwara wata karamar yarinya ce. Tare suka fito da Doc Ismail har suka hadu da wani likitan Jibril dai be bi ta kansa ba dan hankalinsa yana can gurin dan da aka ce na Nawwara ne. Sun yi sa'a suna isa ana fitowa da shi dakin tiyata, Sai Doc Ismail ya tsayar da su saboda abokinsa ya samu ganin yaron, mutuwar tsaye Jibril ya yi a gurin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119