Chapter 113
Chapter 113
jinina kowa ni zai dorawa laifi, addu'ah nake hawaye suna min xuba, mafita kawai na ke nema a gurin Ubangijina, ina rokon ya sassauta min zuciyata ya bani ikon mantawa da komai. Bayan na gama na dawo saman kujera na zauna ina ta kallon fuskarsa tashin hankali da zullumi cike a zuciyata. Misalin bakwai da rabi Mahaifinsa ya shigo ina ganinsa na sauka daga kan kujerar na duka har kasa na gaisheshi amman abun mamaki sai ya ki kallon inda na ke balle ma ya amsawa. Ban tashi daga duken da nake ba likita ya shigo ya kara duba jikinsa ya yi musu bayanin cewar jikinsa da sauki kuma zai farka nan da wasu yan awoyi. Likitan na fita sai Step mother din Jibril ta shigo tare da wasu yan uwansa, su kan da na gaishesu sun amsa min har ma suka tambayeni mai jiki na ce da sauki. “Hajiya kuje waje likita ya ce a barshi ya samu isasshen bachi, kuma akwai maganar da nake son mu yi da matarsa” Shine Abbah ya fada abunda ya fadarmin da gaba, ba musu suka fice suna Allah ya sauwake, bayan fitarsu Abbah ya kalleni irin kallon nan na tsana ya ce. “Bari kiji na fada miki duk da na ya mutu sanadiyarki kema sai kin mutu, ko wane ango aka kai masa amarya farinciki yake yana zumudi balle ma Jibril da yake jin kamar ya hadiyeki, amman daren da aka kai shi daren aka kwasoshi zuwa asibiti yan biki ko watsewa ba su yi ba, Wace irin macece ke wani irin kallo kike so duniya ta miki? Jaruma ko hajirtacciya? Duniya zata miki kallo wawuya ne marar hankali wacce ilmimta be amfaneta da komai ba. Da kin san irin son da da na yake miki da ko ko da baki bari ya taba shi ba balle har ki bata masa rai, ban taba sanin cewar dana yana da heart attack ba sai yau, kuma na san saboda ke ne, idan kika kashe Jibril da wane ido zaki kalli Noor? Anya Nawwara akwai imani a zuciyarki kuwa?” Zubewa na yi kasan guiwoyina ina kukan da ban san ta ina yake fito min, kukan da ya hanani cewa komai har su Inna suka shigo sai Abbah ya juya ya fita bayan ya gaisa da su. Inna kamar jira take ya fita sai ta hau ni da masifa ranta a bace “Karkar kuka kike Nawwara, da kukan jini zaki yi, ba sakike kike so ba? Bari Allah ya bashi lafiya zan sa ya sakeki kije ki auri Bilal din mahaifiyarsa ta yi ta gasa miki garwashi a hannu ba ma gida ba, mutumiyar banza marar hankali wannan hakin naki ba haline na mutanen kirki ba, kuma duk mai irin rayuwarki ba zai taba jindadin zama duniya ba, ke baki ma Allah laifi ya yafe miki ne ko ke kin fi uban kowa ne, Jahila kawai ilminki ba shi da amfani Nawwara kin yi hasara jindadin zama da mutane indai haka zaki cigaba da rayuwa” Babu bakar maganar da Inna bata fada min ba, ita da Mama Turai mutuwa ce kawai ban yi a gurin saboda kuka, amman har numfashina kokarin fita ya rikayi. Hakan be sa Inna ta tausaya min ba sai ma haushina da take ina kokarin rike mata zane ta buge min hannu ta fice a fusace, babu wanda ya tsaya ya saurari ni. Kuka na yi a gurin har sai da na gode Allah sannan na tashi na koma saman kujerar na zauna ba dan hawaye sun daina min zuba ba. Wata yar uwar Jibril ce ta shigo da kayan abinci ta aje sai ta dafani “Adda Nawwara ki yi hakuri Yaya zai tashi Insha-Allah” Uffan ban ce mata ba har ta fice, sai na maida kaina na kwantar jikin gadon na lumshe ido kaina na mugun ciwo kamar zai tsage. JIBRIL POV. Misalin goma da rabi na safe ya bude idonsa, ya dade yana gani dishi² sannan ya soma gani dai dai har ya gane asibiti aka kawo shi. A hankali ya maida dubansa gurin Nawwara da kanta ke kwance saman gadon idanuwanta a lumshe da alama bachi take amman sai shesshekar kuka take. Hannu ya kai ya shafa saman kanta, ya lumshe ido. Sai kuma ya kai dayan hannunsa ya cire oxygen din da ke bakinsa ya unkura cike da karfi hali ya tashi zaune, yana jin zuciyarsa kamar zata rabe biyu. Hakan ne ya farkarda Nawwara daga bachin da take suna hada ido sai taga abun kamar mafarki saurin mikewa tsaye ta yi sai ta rumgume shi tsabar jindadin ya farka be mutu ba, sai ta fashe da kuka. “Ka yi hakuri Jibril ba zan sake ba, ban zata abun ya kai har haka ba” Rumgumeta ya yi tsantsan a kirjinta ya lumshe ido, rabon da yaji irin wannan sukunin da sakewa har ya manta, a take ya ji sanyi a zuciyarsa har wani kuzari yana rabarsa. Saurin sakinsa ta yi tana share hawayenta. “Bari na kira likita” Sai ya rike mata hannu ya bude ido a hankali yana kallonta da bakinsa da ya yi fari ya bushe. “Doctor be da abunda zai min Nawwara, ki ce likita na komai za a min a duniyar nan ba zan warkeba matukar babu kulawarki da sonki a kusa da ni, babu ciwon da zai rabeni matukar kina kusa da ni, na san ba nine wanda kika so but please stay with me ko da na dan lokaci ne, i feel like rayuwata ba zata tsawaita da har zan hanaki jindadin rayuwarki ta nan gaba i need you” Dawowa ta yi ta zauna bakin gadon da yake zaune, hannunta na cikin na shi fuskarta kuma na zubar da hawayen, dayan hannunta tasa ta jimke hannunsa a tsakiyar hannayenta. “Har yanzu akwai son Jibril a zuciyarki, ki rantse min da Allah baki son Jibril, ba zan iya aurenki ba saboda zuciyarki Jibril take so ko da na aureki gangar jikin kawai na aura. Haka Bilal ya fada ranar ganina na karshe da shi saboda ya ga son ka a idanuwana, karya na ke na ce bana son ka Jibril kawai na kasa manta abunda ka yi min ne, amman yanzu komai ya wuce i promise you ba zan sake yin wani abun da zai tashi hankalinka ba” Hawayene suka zubo masa hawayen da shi ma kansa be san na minene ba. Hannunsa ya dauka ya dora saman nata. “Fada min wani abu Nawwara, ina jin kamar ba ke bace, wata kila saboda na kusa mutane ne kike so na yanzu” “Daman can ina son ka nothing changed no one can take your place, da ace yau na rasa ba da na wayi gari cikin wata duniya mai rudani da rikitarwa, ban tabbatar da ina son ka ba sai da na ganka kwance a saman gadon nan, Jibril i love more than I did before” Ido ya tsura mata yana ta kallonta, gaskiyar zancenta yake karanta a idanuwanta, kawai ya kasa yarda cewar Nawwara din ce, abunda ya dade yana jiran jin daga bakinta yau ya jishi. Hannunshi ta daga ta kai gefen kunci ta lumshe ido. “Am sorry” Ta furta cikin kuka. Sai ya matsa kusa da ita ya sumbaci goshinta ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119