Chapter 3
Chapter 3
da tsohon rediyonsa. “Allah gamu gareka, ka iya mana” Cewar Inna tana sauke ajiyar zuciya. Ni kuma na miƙe tsaye ina faɗin “Bari naje na shirya na koma can na gani dan jiya sun ce min na dawo da safe” Baba ya ce. “Sun ce zaki samu aikin ne?” “Inshallah zan samu, saboda gurin Babansu naje kuma yana da mutuncin sosai” “Wai aikin me ne?” Inna ta tambaya tana daga kwance. “Sharar ti'ti ne kuma kullum ake biya” Ta yi saurin tashi zaune. “Wane irin sharar ti-ti kuma Nawwara? Wannan sam ba mutuncin ki ba ne, Wallahi zaginki za a fara daman sun saba” “Dukan masu zaginmu Inna babu wanda ya taɓa ɗauko Naira ɗari ya bamu ya ce mu siye wani abu, kuma na muku alƙawarin kare mutuncinna, Hijab zan saka idan har na samu aikin nan” “Ba irin wannan aikin ya dace da ke ba Nawwara, ni nafi kowa dacewa da na yi shi” “Baba ka san kana da Asma ba zai yiyu ka yi irin wannan aikin ba, kuma na maka alƙawari da zarar ka samu wani aikin zan daina wannan” Ya girgiza min. “Ba zaki yi ba Nawwara, sai dai ba zan hana ki bincikar wani aikin na daban ba, shi ma kuma kamin na samu wani abun yi” Na ɗaga masa kai cike da ladabi. “Tau Baba zan koma Candy Restaurant ko Allah zai sa a dace, amman Baba dan Allah ban da turin baron nan da ka taɓa yi kasan yadda zuciyarka yake idan ka ɗauki abu mai nauyi, ni Wallahi bana son kana dakon nan” Na faɗa kamar na yi kuka, dan har ga Allah nafi tsanar dako fiye da komai a duniyar nan. Baba yayi murmushi irin nasu na manya sannan ya ce “Nawwara kenan, ni dai ina jan hankalinki kan tsare mutuncinki da kuma na mu gaba ɗaya, Nawwara ke rai biyu ce mai maka da rai dubu a gurin mu, dukan abunda zai zubar da mutuncin ɗan ki da ni Mahaifinki karki kuskura aikata shi, ki riƙa tuna ke uwace, kuma ɗiyar wani wacce idan kika yi abun assha za a zagi Ubanki, ɗan ki kuma ayi masa jawabi, ni dai na san irin tarbiyar da na baku Wallahi ko cikin maza dubu zaki shiga matuƙar baki watsar da tarbiyar gidan nan ba, nasan zaki fito lafiya. Ni da kan ɗan ki rai biyu ne a gareki Nawwara, abu kaɗan kika aikata zai iya saka zuciyata ta buga, ɗan kuma zai tsanake ni ya riƙa nadamar da kika kasance uwarsa, saboda haka ki riƙe mutuncin ki, Allah ya muku albarka” Ni da Inna muka amsa da Amin. Haka yake min a duk lokacin da zan fita neman aiki ko wani abu makamancin wannan, waɗannan nasihohin suna tasiri a gareni matuƙa, sukan katangeni daga duk wani tayi da wasu suke min na siyar da mutuncina, ko kuma musanya mutuncina da takarɗun aiki. Comment on every single line. *RAI BIYU...♥️🖤* Wattpad @Khadeeja_Candy 3⃣ Bayan na baro ɗakin Inna na ɗibi ruwa a shiga ban ɗaki na yi wanka. Atamfata ta sallar bara na ɗauko na saka, akwai da son saka gyale duk da kasancewar Baba baya son haka, daman ba ko waɗanne uwane suke son ƴarsu ta saka gyale ba, sai dai nawa gyalen ba irin na barbarɗaɗɗin ƴan mata nan ne ba, me zai kai ni saka ƙaramin gyale bayan ina da ɗa kuma ba budurwa ba ce ni, duk da yake wani lokacin Jidda da Habiba har da mutanen waje kan faɗa min babu wanda zai kalleni ya ce ni bazawara ce har sai idan ni na faɗa, wani lokacin ko da na faɗa ba a yarda har sai idan waɗanda suka san ni ne. Ina da kyau jiki dai-dai gwargwado wannan yasa mutane basa yarda idan har na faɗa cewar ni Bazawara ce har da ɗa, wannan baya rasa nasaba da auren wuri da aka min, a lokacin da nake ganin kamar ban isa auren ba, auren da ya gurɓata min rayuwa ya canja ƙaddarata daga mai kyau zuwa mummuna. Atamfata miyan goro ce mai ratsin ja, hakan yasa na saka jan gyale saboda atamfar ta ƙara fita, talkamin Habiba na ɗauka na saka masu launin ja. Fes na fito sam baza kalleni kace ina da wata damuwa a wannan lokacin ba, idan ba ka birkice atamfata gaka ta roba bace sai ka ɗauka ni ƴar wani shegen mai kuɗi ce, ba laifi ni kaina ina sarawa kaina indai babin kwaliyana ne na iƴa fito kamar matar minister. “Inna zan tafi” Na faɗa ina tsaye daga jikin ƙofa, kai na jingine da ƙofar ina kallon Baba da ke unƙurin tashi. “Tau Allah ya kiyaye” Inna ta faɗa, Baba kuma sai ya ce “Ni ma bari na shiga kasuwa na ga abunda Allah zai yi” Salamar Maniru muka ji wato almajirin Hajiya Murja, maƙociyarmu masu babban gida, matar babban soja wacce bata taimako sai idan da dalili. Ni da Inna muka haɗa baki gurin amsa masa, Baban kan ya amsa masa da. “Bata nan taje makaranta” Domin yasan Jamila take nema, takan aiko kiranta a duk lokacin da wani aiki ya sha gabanta, domin kawai ta taya ta aikin sai ta sammata wani abu daga abincin rana ko dare da aka yi a gidan. Bayan Maniru ya fita Baba ya haɗe fuskarsa saboda mu ɗauki zancensa da muhimmanci, ya saba mana a duk lokacin da yake hanin mu kan aikata wani abu ko kuma ba mu umarni. “Bana son zuwan da Jamila take a gidan Manjo Faruku, kowa ya tsaya inda Allah ya aje shi” “Ni kaima bana son zuwanta a gidan domin yaron gidan nan ba shi da tarbiya, sannan yunwa babu abunda bata sawa musamman ga waɗannan da suke yara” Na faɗa cike da jin zafin tuna irin satar da ta taɓa ɗorawa Sakina a kwanakin baya. Inna dai bata ce komai ba bayan ajiyar zuciya da ta sauke. “Na tafi nidai ayi min addu'ah” “Tau Allah ya bada sa'a karki daɗe dai, kuma ki kula.da irin mutanen da zaki yi hulɗa da su” Cewar Inna ni kuma na amsa da tau na kama hanya ina addu'ar fita daga gida wato. _Bismillaahi, tawakkaltu 'alallaahi, wa laa hawla wa laa quwwata ‘ illaa billaah._ _بِسْمِ اللَّهِ تَوَكَّلْـتُ عَلَى اللَّهِ، وَلاَ حَوْلَ وَلاَ قُـوَّةَ إِلاَّ بِاللَّهِ_ Babu ko ƙwandala a hannuna ƙasa na kama hanya duk kuwa da kasancewar unguwar akwai ɗan nisa da ta mu. A bakin ti-ti na haɗu da Bilal wato abokina ko kuma na ce mutumen da muke mutunci da shi sosai har mutane suke raɗin-raɗin wai akwai soyayya a tsakanin mu. “Nawancy” “Bilal ya gida?” “Lafiya ƙalau Wallahi Ina zaki je haka?” Bana son faɗa masa ainahin inda zanje, ba kasafai nake son mutane su san ina zuwa aiki ba nafi son aji na samu aikin kawai, musamman Bilal da yake yawan nuna min baya son neman aikin da na ke. “Nan zan je gawon nama gidansu wata ƙawata Zinatu” Ya matso da mashin ɗinsa Honda “Hau na sauke ki” “A'a na gode” Na faɗa ba dan bana son hawan ba sai dai bana son yasan gurin da zanje. “Dan Allah ki hau mana, t-t ne balle ki ce kina jin kunya an mun fito
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119