Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 8

Chapter 8

Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

jima ko gobe” Cewar Jidda. “A'a Jidda tun da har Allah yayi mana mafita ƙara muje mu kai musu kuɗin, baki san halin da bawan Allah ya ke ciki ba” Na kalli Inna zuciyarta cike da tausayinta da kuma tausayin kaina da na Jidda, na san tun safe bata ci komai ba ga rashin kwanciyar hankali da ke damunta. Hijabinta da ke gabanta ta ɗauka ta saka ta miƙe jikinta har rawa yake ta saka talkaminta ta kama hanya. Na kalli ƙawata Jidda tare da yi mata godiya. “Na gode sosai Jidda” “Ba komai, ki yi magana da ƴar'uwarki Nawwara ki kwantar mata da hankali karta sake shiga wani hali, ni zanje gida kar Abbah ya dawo” “Na gode sosai Jidda” Tashi ta yi ta fita, ni kuma na tashi nayi alwala na yi sallah, shiru-shiru Inna bata dawo ba har bayan Isha'i, sai dai hakan be sani tsoro ba a tunani ko zasu ɓullo da wani abun ne na daban. Takwas da rabi Inna ta dawo ita kadai cikin yanayin damuwa. Sai dai ban tambayeta komai ba har sai da ta yi alwalah ta rama sallah magariba ta yi isha'i bayan ta sallame na matso kusa da ita na ce “Inna ya kuka yi da su” “Lamarin ƴan sanda nan yana ba ni tsoro Nawwara, basu bar mun ganshi ba, amman sun karɓi kuɗin wai zasu zo anjima su kawo shi da kansu, ni ban taɓa jin inda aka yi haka” “Ko dai ba zasu bada belin nasa ba ne?” “Ni ya zan sani, an ce dpo gurin ƙanen wacce aka yi satar ne, kin san kuwa sai yadda Allah yayi” “Baba Sulaiman be ce komai ba?” “Babu irin roƙon da ba mu musu ba Nawwara, Har Salisu da Dahiru duk sunje, amman sun ce ba zasu ba da shi ba sai dai su kawo shi da dare, shine su suka wuce gida ni kuma na dawo” “To ko wasu kuɗin zasu ce a ƙara musu kuma?” “Ban sani ba” Ta faɗa tana fashewa da kuka. Iya ƙoƙarin da nayi na danne kukana sai na kasa saboda ganin hawayen mahaifiyata yana zuba. Shiru-shiru har goma na dare babu wani labari, daga ni har Habiba da Inna muna cikin tashin hankali da zullumi, dukanmu hankalin sai ya tattara ya koma gurin ƙofa ko iska ya kaɗa sai muga kamar Baba ne za a shigo da shi. Sha ɗaya da rabi na dare na tashi zan rufe gida, izuwa yanzu kan mun sadaƙar ba zasu kawo shi. Ina kaiwa bakin ƙofa sai na hango motar ƴan sanda ta faka a ƙofar gidanmu ahankali, ta yadda ba za a ji ƙarar motar ba, fitar motar ma a kashe take. Ban ƙara tabbatar da ƴan sanda bane har sai da naga sun fara fito daga cikin motar. Da gudu na juya na koma cikin gida dan faɗawa Inna. “Inna Inna ga su can sun zo” Ba Inna kawai ba, har Sakina da Jamila da ke bachi sai da suka farka duk muka ɗunguma muka fito waje da gudu. Sai dai abunda muka yi karo da shi ya faɗar da gabanmu dukanmu. Baba ne suka aje gefen icce sai wasu ƴan sanda uku kusa da shi ɗayansu ya ƙaraso kusa da mu yana mana bayanin da ban gane kansa ba. “Zuciyarsa ce ta buga, ku kai shi asibiti da safe” Yana faɗar hakan ya juya da sauri suka fice daga gidan. Mu kuma muka ƙarasa gurin da Baba yake kwance, hannu na kai na girgiza shi be motsa ba, na kira sunansa be amsa ba, na jijjiga amman be yi wata alama ta mai rai ba. Firgice na nasa hannu na yaga rigar yadin da ke jikinsa, sai ga ƙirjinsa da dukan jikinsa da jini, tashin hankali ya mantar da ni cewar dare ban san lokacin da na kwala ihu ba, na yi tsalle na dire na faɗi ƙasa na mulmula na mulmulo ina kuka, Habiba kuma ta faɗo kaina sumammiya. YAWAN COMMENTS YAWAN TYPING. 🙌 *RAI BIYU...♥️🖤* Wattpad @Khadeeja_Candy 7⃣ Cikin tashin hankali na kwantar da Habiba da ta faɗo kaina, na nufi Inna da ke baya-baya tana nuna Baba da yatsa. Ina riƙata sai ta cafki hannayena jikinta na karkarwa. “Gawa suka kawo mana Nawwara, sun kasheshi, miya musu? Basu yarda zamu biya kuɗin ba? Ko dan sun maida mu talakawa? Saboda ba mu da galihu? Akan ƴan kunnen zinari da wayoyi suka ɗauki rai? Miyasa za su kawo mana shi? Saboda muma mu taru mu mutu ko? Sun maida mu mahaukata...” Daga kalaman da take na fahimcin ƙoƙarin fita hayyacinta take. Riƙata na yi na zaunar, Sakina da Jamila da ke kuka na tura su ɗaki. Sai kuma na dawo tsakar gidan na yi tsaye ina kallon Baba, kana na kalli Habiba da ke sume, sai kuma Inna da ke zaune tana kallona, neman kukana na yi na rasa ashe akwai ranar da zaka buƙaci kukan ya ƙi zuwa maka, idona gaba ɗaya na ƙafe kamar hawaye be taɓa taruwa a ciki ba, yawun bakina na bushe kaina kuma yayi mugun nauyi kamar an ɗora min dala. Ban damu da rashin mayafi da babu a jikina ba da kuma takalmi na fita da gudu zuwa babban gida. Gudu na ke amman gani nake kamar ƙara maida ni baya ake, tsakaninmu da su babu nisa amman yau sai ya koma min kamar gari da gari. “Keeeeeeee” Na ji an kirani sai dai hakan be sani tsayawa ba, har sai da na ji an harba bindigar mahalba. A firgice na juyo ina ɗaga hannuna sama yayinda su kuma suka tunkaroni suna nuna ni da bindigar, ɗaya daga cikinta da dalla min fitila mai tsananin haske da kashe ido. “Nawwara miya fito da ke cikin daren nan?” Jin muryar Baban su ƙawata Ruƙaiya yasa na gane cewar ƴan sitirine masu yawo da zarar dare yayi domin kama ɓarayi. “Babanmu ne aka kawo shi ne zan je na faɗawa Baban Sulaiman, Babban gida zani” Na faɗa cikin wani irin mugun haƙƙi da sarƙewar murya. “Tah koma gida zanje na faɗa musu, Ibrahim rakata” Ya ƙarasa yana kallon ɗaya daga cikin yaransa. Wanda aka kira da Ibrahim ɗin ya saka ni gaba shi ya rakani har ƙofar gida sannan ya koma. Ko da na shiga na samu Inna zaune gaban Baba ta zuba masa bokiti biyu na ruwa sai fifita take masa da ɗankwalinta, atunaninta ko ya yi doguwar suma ne wata ƙila idan ta yi masa haka zai farko. Ƙarasa na yi ƙusa da ita na ɗauki ragowar ruwan da ke bokitin na juyewa Habiba sai gata ta farka a firgice tana haƙi kamar na fitar rai. A nan Inna ta juyo ta kalleni fuskarta a taɓe tana shirin fasa kuka. “Shi wannan ya mutu kenan?” Wani irin uhu Habiba ta saka iya ƙarfinta tana shurin ƙafafunta, tana danƙar ƙasar tana watsarwa. Ni kuma na yi zaune a gurin bana kuka kuma bana iya bawa ɗayansu haƙuri daga ita har Inna da ke kuka, ƙaɗan-ƙaɗan juri yake ɗibata ina jin sautin kukansu kamar a cikin bachi. Kan kace kwabo maƙota sun cika gidanmu kamar ba dare ba, masu taya Inna kuka na yi wasu kuma na girgiza kai, shigowar su Baban Sulaiman ne yasa kowa

Table of Contents

Chapters

119 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});