Chapter 72
Chapter 72
saba'in. “Ka sake ni ko na maka ihu” “Ko kin yi ihu babu wanda zai zo” Ya fada idonsa a lumshe yana kara kwamtar da kaina a kirjinsa. “Kina jin yadda zuciyata take bugawa ko Naj saboda ke” “Idan baka sake ni ba zan sake zuwa aikin nan ba, daman saboda ka rika min haka ka tirsasani yin aiki a tare da kai ko?” Ya dora kansa saman kaina. “Ina ma zamu dawwama a haka” “Ba zan sake zuwa aikin nan ba” Ya yi saurin saki na. “Ina son ki sosai Naj ina miki irin son da wani da namiji be taba miki ba” “Ni kuma bana son..” Na kasa karasa saboda hannunsa da yasa ya rufe min baki, sai kuma ya duka kasan guiwoyinsa ya hade hannayensa. “Dan Allah dan Annabi Naj ki yafe min abunda na yi miki, dan Allah ki manta da komai” “Na manta da komai saboda ka san ka zalince ni ko? Mugu bakin azzalumi” “Ki kirani da ko wane irin suna zan karba miki, ki ayyanani a duk kalar mutumen da kike gani zan dauka, ki ci mutunci a gaban kowa zan jure matukar hakan zaisa ki yafe min” “Ba zai taba sa na yafe maka ba” “Fada min abunda zan yi ki yafe min Naj, ni kadai na san irin abunda na ke ji a zuciyana, na kan tsani kaina idan a duk lokacin da na tuna abunda na aikata miki, tunaninki ya haddasa min ciwo da damuwa, rashin kulawar nan taki ina jin kamar yana kokarin rabani da rayuwata ne, i will die soon Naj mai yuyuwa a wannan lokacin zaki tausaya min ki zo gaban gawata ki yafe min” Hawaye yake irin hawayen nan dake nuna tsantsar abunda ke zuciyarsa, ga nadama da damuwa nan ƙarara a fuskarsa. “Lokaci meeting yana wuce” Na fada tare da daukar takardun na nufi kofar fita. A ranar meeting hudu muka yi uku a cikin kamfanin daya kuma a wani kamfanin da muka je tare, sai dai sam babu walwala da sakewa a fuskar Jibril da ma yadda yake maganarsa da mu'alama da mutane, dukan abunda zan yi hankalinsa yana kaina, da muka dawo na yi sallah shi kuma ya dora alwala ya fita zuwa sallah a masallacin da ke kamfanin ni kaina ban taba sanin akwai masallaci a kamfanin ba sai yau, bayan na dawo ya cilasta min zuwa cin abincin rana kamar jiya, da muka shigo office ya dauko wasu takardu ya aje min wai na yi typing dinsu a computer shi kuma ya nemi wata kujera ya aje gaban teburina yana kallona har na yi aikin na gama. Tare da shi muka shiga mota, ya kawoni a inda ya aje jiya sannan ya mika min wata sabuwar laptop, wai da ita zan dinga zuwa office kuma na je gida ta aiki ce sai kuma na bukaci na kwashe duk abunda ke cikin wacan computer ta office na saka a laptop din, ni dai ban ce masa na gode ba balle sai anjima na fito na yi tafiyata. Ko da na isa gida yamma ta yi lis saboda yau na dade sosai a gurin aikin, na darar da gidanmu cike da mutane suna ta mana murna wai Sakina ta ci gasa an bata gida kuma wanda yasa gasar ya dauki nauyin karatunta sannan ya yi mata kyautar dubu dari biyu da hansin, ita kanta kamar zata hade kanta dan murya. Jibril kawai zuciyata ke raya min ya saka gasar nan, sai kuma daga baya na soma tunanin Mustapha domin shine a unguwar ya fi kowa sanin inda Sakina take karatu, har dare mutane nata shigo mana, Inna ta siye minti ta yi sadaka, bayan sallah isha'i Bilal ya kirani a waya na ki na daga sai ya aiko min da sako wai yana kofar gida, nan ma ban mayar masa da amsa ba jim kadan sai ga yaro ya shigo wai ana sallama da Nawwara, sai na yi karaf na ce “Je ka ce ba zata zo ba” Inna ta saki baki. “Ba zaki zo ba? Ba kyau wulakanta dan adam fa, Wallahi ki kama kanki, ni bana son yawan zuwan da ake ama miki sallama, wallahi ko aikin nan da kike zuwa hankalina be kwance yake ba, bani da kwanciyar hankali idan ba aure kika yi ba” “Inna Bilal ne fa” “To dan me ba zaki je ba?” “Wai birthday yayi yau shi da Zinatu suka yanka cake din kuma a gurin aikinmu wai har da kirana dan na gani” “Kishi kike kenan, ashe ana kishin abunda ba a so?” “Ni ina son shi” “Kina son shi kike nuna baki son shi? Kina son shi miya hana ki aure shi? Yanzu ke kina ganin zaki samu namijin da zai so ki kamar yadda Bilal yake son ki? Babu abunda ba a fada masa ba a kanki amman ya toshe kunne ya ce yaji ya gani shi dai son ki yake, kuma kina da ɗa shi yana saurayi kuma a haka yake son ki, babu irin kulawar ta cusa kai da be nuna miki ba amman kiki bashi dama, sai yanzu dan ya kula wata zaki ji haushi har ki zo kina kishi? Wane iriin zama kike son ku yi da shi? Shi dai aure yake son ki idan baki bashi dama ba ai dole yaje inda wacce zata bashi dama, Idan har son Bilal kike da gaske tau ki bashi dama ya ga magabatanki, sai ki yi kishi mai dalili, amman yanzu ai cin amanarsa zaki yi ki hana shi aurenki kuma ki ce ba zai kula wata ba?” “Amman Inna ai kin san yan gidansu basa so na, ni bana son na yi aure inda zan wahala ni da Noor” Na fada ina kuka, sai ta ce “Zaki wahala dai ke, Noor kan ai ba zai zauna tare da ku ba, duk son da Bilal yake nunuwa Noor ana daura miki aure dole a gida zaki barsa sai dai ya rika zuwa yana ganinki, saboda Bilal Saurayi ba mai mata ba, da ma ace yana da mata da zakiniya zuwa da danki ya rika shi, amman wannan kan ai sai ya kara kiyayyar ki ga yan uwansa kuma jama'a ma sai su zageni ace na bari aka je da yaro ya takura masa, ina tunanin ba a gidansu zai aje ki ba ko da ya aureki, dan haka yan uwansa su daina damunki ba akansu zaki zauna ba, indai mijinki na son ki babu wanda ya isa ya taka ki, sai dai ki shiryar fuskantar kalubale daga garesu” Na kara fashewa da kuka, ni dai har ga Allah ina son Bilal dina, kuma bana jin zan iya auren wani namiji bayan shi. *** *** *** Washe kamar marar lafiya haka na tashi jiki babu dadi zuciya ma babu dadi, bayan mun gama karyawa suka tafi makaranta ni kuma na gyara gida sannan na shiga na yi wanka ina fitowa na shirya cikin wata bakar abaya, da mayafinta, sannan na dauki laptop din da jakata na nufi dakin Inna ina mata sallama. “Amman dai ina tsoron ki rika wannan abun a hannu, kin san garin ne ko maza ya suka kare balle mata” “Ai kin ga a ciki jaka take ba wanda
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119