Chapter 44
Chapter 44
taru a gidan kowa ya keɓe wani ɓangare nasa ya kafa nasa iyalin. Lokatuta da dama takan keɓe ita kaɗai ko kuma da mu tayi ta kuka tana roƙon Allah ya bawa mahaifina wani aikin duk da bashi da wani karantun zamani a wacan lokacin, muna haka wani maƙocinmu Malam Buba kuma abokin Baba da yake yawan zuwa Abuja ya faɗa ma Mahaifimu cewar wani attajirin mai kuɗi a garin Abuja yana neman mai masa gadi kuma ya ce baya buƙatar kowa sai bahaushe ɗan'uwansa, Malam Buba ya kasance yana masa gadin wani babban kamfanin siyer da kayan alatu ne dake can garin Abuja. Muna zaune gida ranar wata talata, bayan mun gama cin kwaɗon ƙanzo, sai Baba ya shigo da far'arsa yana labarta mana abunda Malam Buba ya faɗa masa, Inna ta yi murna sosai kuma ta nuna jindaɗinta, a nan suka yanke shawarar ba zasu sanar da Yakumbo da Hajiya ba saboda sunsan ba zasu bari yaje ba, sai suka haɗa kai da Malam Buba ya faɗa musu Babanmu zaije Abuja ya kai fatune saboda ana bukatarsu a can, sun yi na'am suka masa addu'ah da fatan nasara, sai Baba ya karɓi fatun bashi da sunan idan yaje can zai aiko da kuɗin. Ranar da zai tafi munyi kuka sosai ni da Inna har ma da wasu mutanen gidan saboda muna ganin kamar ba zai dawo ba, tafiya nisa kuma har garin Abuja garin da a wacan lokacin muke ɗaukarsa kamar wata ƙasar dabam. Bayan wata ɗaya da tafiyar mahaifinmu sai gashi ya dawo cikin shigar mutunci da kamala, sai dai ya ɗanyi rama kaɗan ya kuma yi haske, ya labarta mana komai yake muna nan cikin ranshi wannan tunanin ne ya hanashi ƙiba, har ma yake faɗa mana cewar mai gidansa ya ware masa wani ɓangare na gidansa ya bashi ya ce ya ɗauko iyalansa su dawo nan kuma ya zo mana da kuɗi mai yawa. Ba ƙaramin yaƙi akayi ba kamin Hajiya ta yarda ta barmu aka tafi da mu, a nan ma sai da ya yi mata wata ƙaryar cewa ya canja sana'a yanzu yana siye da saida takalma ne na fatu har ma ya ce mata hayan gida ya kama a ƙauyen Abuja acan zai zauna da mu ya cigaba da sana'arsa. Amaina huɗu a mota kamin mu sauka zaria, aka siya min abinci da ruwa na cika cikina ni da Habiba sannan muka cigaba da tafiyar, ko da muka shiga garin Abuja ina bachi, sai da motar ta tsaya sannan Inna ta tasheni muka koma can wani ɓangare na tashar, Baban mu ya ari wayar wani ya kira Alhaji ya sanar masa mun iso domin ba a shiga da wani abun haya a unguwar. Dare ya yi sosai har Baba ya yanke shawarar zuwa gurin abokinsa Malam Buba mu kwana a can sai ga ƴan komisho sun zo suna neman Malam Musa Kafinta, a nan suka haɗa mu da mutumen yanayin yadda Baba ya gaisa da shi sai ya tabbatar da cewar ya sanshi, ashe direban Alhajin ne. Ni da Inna duk da tsoro muka shiga motar saboda ganin Babbar motar kamar wannan wacce ni dai zan iya rantsuwa hannuna ma be taɓa kaiwa akanta, amman yau zan shigeta. Ina ta rabon ido har muka iso wata kyakkyawar unguwa. Idona be ƙara buɗewa har sai da muka iso cikin ƙaton gidan dake cike da ababen more rayuwa. Iyalan mutumen ne da Alhajin shi kansa suka fito suna tarbonmu, har yake bawa Baba haƙuri akan rashin ɗaukoshi da wuri wai yaje meeting ne kuma sai ya manta sai da ya dawo gida sannan ya tuna. Cikin Falonsu muka shigo sai suka saka mai aikinsu ta kwashi kayanmu ta kai BQ, mu kuma suka kawo mana abinci da abin sha. Cikin sati ɗaya muka sake da ƴan gidan kasancewarsu mutane da suka san darajar ɗan'adam tun daga Hajiyar gidan har yaranta, Ƴaƴanta maza biyu manya sannan mata uku ɗayar tana aure sauran biyu kuma a lokacin suna karatune, sai ƴar ƙaramar ƴarta Salima, wacce ta kasance ta shida a cikin yaranta takwas. Shaƙuwa sosai da sosai ta shiga tsakanina da Salima, har ta kai zuwa makaranta ne boko ne kawai yake rabamu, kasancewar ni bana zuwa bokon sai dai islamiya Alhaji Dahiru wato mahaifinta ya sakani Islamiyarsu. Duk ƙarshen wata Baba yake zuwa gida duba Hajiya, wani lokacin kuma sai dai ya yi mata aike a haka muka kwashe shakara ɗaya a gidan Tsohon ambasadan nigeria a ƙasar London, muka zama kamar ƴan gida, shaƙuwa sosai ke ƙara shiga tsakanina da Salima, da kuma Babban yayanta Jamal, shi yake koya min karatu duk da ba a sani makaranta ba a lokacin, Jamal mutum ne mai son jama'a da far'a, har ta kai idan be ganni ba sai ya aika an kirani, bayan ya gama koya min karatu sai ya ce na yi masa gatana, ba laifi a lokacin na iya zuba gatana har da wacce ba'a taɓa yi ba, haka zai zauna ya yi ta saureren shirme na wani lokacin har da Hajiyarsu. Shi ya fara yaba ƙwazo na sai ya yi ma mahaifinsu magana aka sakani a makarantarsu Salima, na kashe kuɗi sosai gurin samo transfer dake nuna daga wata makarantar na ke, sannan aka samu sa'a aka sakani aji ɗaya da Salima, Habiba kuma aka sakata wata maƙarantar wacce ƙannen Salima suke yi. Tare muke zuwa mu dawo, mu tafi islamiya tare, wasa-wasa sai na tattara kayana suka na koma ɗakinta da zama, a lokacin Inna na da cikin Sakina, komai a iri ɗaya muke da Salima bana da ƙawa sai ita itama bata da ƙawa sai ni, idan ba a ganta ba sai an tambayeni haka itama. Ta ɓangaren Jamal kuma soyayyace mai ƙarfi ta shiga tsakaninsu duk a lokacin ban san miye so ba, na kan samu kaina da tunaninsa da kuma rashin jindaɗi a duk lokacin da baya gida. Muna daf da ƙare makarantar secondary school ni da Salima Hajiya ta samu labarin cewa Baba gadi yake a wani gida, babu irin bala'in da bata mushi ba cikin har da zance zata tsine masa gidan be dawo ba, wai Inna zata kaishi ta baro yana biye zancen mace. A dole tasa Baba ya tattara ya koma gida sai dai be zauna gidan ba sai ya kama haya kusa da su inda muke zaune har yanzu. Ni kuma a aka barni nan da sunan idan na gama zana jarabarwar za a maidani gida, bayan mun gama jarabarwa ta fito ta yi kyau, a lokacin ne ɗan wani mai kuɗi ya fito neman auren Salima, Alhaji Dahiru ya yi na'am ya sallama masa bisa sharaɗin zai jirata ta yi karatu na gaba, a lokacin shi kansa yaron be kammala karatunsa da yake ba. Bayan sati ɗaya da faruwar haka sai Ya Jamal ya fara min zancen aure, ni kuma ina ta tsoro saboda ina ganin kamar iyayensa ba zasu yarda ba, sai na nuna masa bana son shi, duk abunda muke a tsakaninmu ne iyayensa basu sani ba, har Salima ma tada zame min jinin jiki ban taɓa labarta mata ba, shi ma kuma be taɓa nunawa kowa ba. Bayan takadun mu sun fito sai Alhaji Dahiru wanda muke kira da Daddy
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119