Chapter 53
Chapter 53
ɗaya ba shi da kyau Ya Mustapha domin idan mace da Namiji suka kasance su kaɗai suka kaɗaice to sheɗan ne na ukunsu, amman wannan be taɓa zuwa a ran Momy ba balle kuma kai da ace hankali ko kuma sha'awarka ta kwaɗaita maka ni da yanzu ka gama da ni kuma ba za ayi komai ba saboda kai ɗan gata ne. Ka misalta kanka Ya Mustapha da ace kana aikata zina da wannan yarinyar ne Allah ya karɓi ranka mai zaka faɗawa Ubangijinka? Kamar kaina da bawa ka ce karya aikata abu kaza wata rana sai ka sameshi da tsabama Umarninka har ma ya yi maka sata kuma ka kamashi dumu-dumi wane irin hukunci zaka yanke masa?” Tun da ta fara maganar jikinsa ya yi sanyi hankalinsa ya tashi tun da yake a rayuwarsa babu wanda ya taɓa tsayawa ya faɗa masa gaskiya kamar Ikram, yana sauraren wa'azi amman be taɓa natsuwa ya yi aiki da shi ba. Hawaye yake hawayen da ke nuna nadama da tashin hankalin da ke fuskarsa. “Miyasa baki faɗa min wannan ba tuntuni? Da kin tunatar da ni da yanzu ban faɗa wannan halin ba” “Ko da na faɗa maka zaka faɗa saboda ƙaddaraka ce a haka, kuma a lokacin na san ba zaka saurareni ba saboda ba zaka taɓa ganin munin abunda kake aikatawa ba, ban ga sha'awa ga abincin da zan wanke hannu na ci ba wani yazo hannunsa da datti ya ci wani ma yazo hannunsa da datti yasa ya ci ni kuma na zo na sake saka hannu na ci, sam babu kishi kuma babu imani ga duk mutumen da yake aikata Zina, ban san miye daɗinta ba balle kuma ribarta, saboda yawan mata da kuma yawan wasu ɗabi'u na ɗan adam Allah ya halattawa maza auri mace sama da ɗaya amman kai kaba ma yi auren ba ka faɗa a zina kana neman hallaka kanka, a wannan halin da ka shiga a yanzu ina tunanin shiriyarka ne yazo, dan haka ka yi ta istigifari kana neman Allah ya yafe maka abunda ka aikaka kuma ka yi ma Allah alƙwarin ba zaka taɓa komawa a cikin wacan ƙazamin halin ba, ka yi ta aikata dik wani abin da ka san zai kusantar da kai ga Ubangijinka” Ya gyaɗa mata kai alamar gamsuwa. “Amman Nawwara ba zata yafe min ba ko?” “Zata yafe maka matuƙar kana kyautata mata, kuma kan tuba tuban gaske sai Allah ya dafa maka ta yafe maka har ma ta so ka idan ƙaddarar sonka yana cikin ƙaddararta” “Idan kuma so na baya cikin ƙaddararta fa?” A hankali ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce. “Zai iya zama son ka yana cikin tawa ƙaddarar...!” Da sauri ya miƙe tsaye ya share hawayensa daman tun ba yau ya lura da take-taken Ikram da ke nuna alamar tana son shi. “Ki ɗauki abincin idan na fita waje zan ci, na gode sosai Sis” Yana faɗar hakan ya nufi banɗakinsa dake cikin ɗakin, murmushi ta yi murmushin da ke nuna rashin jindaɗinta sannan ta kwashe kayan ta fice. bayan ya fito wankan ya ɗauki wayarsa ya nemo number Jidda bugu uku ta ɗaga muryar a sake har wani zaƙi take ƙara mata. “Hello Mustapha” “Ya kike?” “Lafiya ƙalau” “Kina gida?” “Ee ina gida lafiya?” “Lafiya ƙalau, kawai ina son ganinki ne akwai wata magana mai muhimmanci da na ke son mu yi da ke idan babu takurawa kuma idan kina free” “Aiko bana free dole zan samu time dominka, faɗa min yaushe zaka zo i mean time?” “Yanzu nan gani nan har na yi wanka” “Okay sai ka shigo” Yana aje wayar ya nufi gurin da tufafinsa suke ya buɗe, cikin ƙanƙanen lokaci ya shirya cikin manyan tufafi riga da wando na shadda, sannan ya fito ya nufi gurin motarsa ya shiga sai ƙofar gidansu Jidda. Waya ya buga mata sai gata ta fito ba ɓata lokaci fuskarta ɗauke da kwalliya sai ƙamshin turare take kamar sabuwar amarya, motar ta buɗe ta shiga kasancewar be fito ba ne yana daga ciki zaune. Front seat ta zauna tana ƙara miƙa masa gaisuwa ciki kashe murya fuskarta ɗauke da murmushi, bayan sun gaisa ya koro mata da bayanin da ke tafe da shi. “Jidda ko kin san wanda yake da gidansu Nawwara da suke haya?” “Ee Malam Haruna ne yana nan gaba da su kaɗan, ya aka yi?” “Na je gurinta ne sai take zargin ko nine na siye gida na saboda ance an siye gidan” “Haka nima na ji amman ban san waya siye ba” “Ai nasan Malam Haruna zan masa magana na ji wanda ya siya sai ya fansar min. Am Jidda ina son ki faɗa min duk wani abu da Nawwara take so da wanda bata so da kuma taimaka min akan duk wani abu da zai ƙara kusancina da ita na san ke zaki iya daboda kinfi kowa saninta” Ta kalleshi Jiki a sanyaye. “Saboda me?” “Saboda ina ƙaunarta son ta na ke Jidda wannan dalilin yasa na ƙulla abota da ke” Tafiyar daƙiƙu biyar zuwa shida numfashinta ya yi sannan ya dawo jikinta har ta iya jiyo bayanin da Mustapha yake koro mata. Be ɓoye mata komai ba daga irin son da yake yi ma Nawwara da kuma abunda ya aikatawa Habiba, ko da ya ƙarasa bata labarin kuka yake sosai kamar ƙaramin yaro. Lumshe ido ta yi ta haɗeye yawu sai hawaye suka sauko mata, hawayen da ita kanta ba san na minene ba na tausayin Habiba ko Nawwara ko kuma kanta ko Mustapha, wani baƙon al'amari ya ziyarceta labarin ya zo mata banbaragwai domin Nawwara bata taɓa labarta mata wannan ba, sai dai yanzu ne ta gano dalilin tsanar da Nawwara take yi ma Mustapha. “Please help me...” Ya faɗa cikin muryar kuka. Sai ta kalleshi tana kukan kamar yadda shi ma yake yi. “Zan yi tunani akwai, ina da buƙatar natsuwa bana iya banbance komai a yanzu” Tana faɗar hakan ta buɗe motar ta fita ta shiga gida da sauri tana kuka. Ya kusan minti talatin sannan ya bar ƙofar gidan zuciyarsa na mugun ƙona ya nufi gidan Malam Haruna. *** *** *** Anya zan iya aiki tare da Jibril kuwa? Mutumen da ya wulaƙanta ni zan iya bashi wannan damar ta kusanci da ni? Yes zaki iya, ga dukan alamu ya gane kuskurensa yanzu kan ya san ƙimarki tun da har zaki maresa a gaban jama'a ya ƙyaleki, yanzu ne ya fi dacewa ki nuna ko wacece ke, yana da kyau yasan ba wacan Nawwarar ba ce this is the time da zaki rana abunda ya yi miki kuma the same time da zaki nunawa Bilal son gaskiya kike masa, kuma idan har ban yi aiki da shi ba na gallaza masa hakan zai bashi damar da zai riƙa bibiya ni da familyna. Da wannan tunanin na tashi yau ina ta son tsayarda matsaya ɗaya akan na yi ko kar na yi. Su Sakina sun kama hanyar makaranta Inna kuma na bachinta kamar yadda ta fara dabuwa kanta a yanzu da bachin rana, ni kuma na fito na gyara tsakar gidan na yi wanka sai na shirya cikin koriyar atamfata ta roba, jin na yi bana ƙaunar zama gidan dan haka na saka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119