Chapter 97
Chapter 97
yi masa na yi ne saboda Noor idan ya gyaru Noor zai amfana idan kuma ya lalace Noor ne zai tagaiyara miyasa ka kasa fahimtata ne?” “Saboda Noor ko? Komai ma ai saboda Noor ne Nawwara i understand” Yana fadar hakan ya saka hannayensa aljihu ya wucewarsa ya barni nan tsaye ina faman hawaye. JIBRIL POV. Daker yake numfashi saboda nauyin da zuciyarsa ta yi masa, daman yanzu abun ya zame masa kamar jiki idan yau be yi ba gobe sai ya yi, sai dai duk wannan abun be taba yarda ya yi gaban Nawwara ba, idan har suna tare abun ya taso masa sai ya kulle office dinsa ko kuma ya bar kamfanin ya dawo gida. Daker ya unkura ya tashi ya nufi bathroom yana shiga sai aman jini yau kan be yi shi da yawa ba kamar yadda ya saba, sai da ya wanke bakinsa sannan ya bude cabinet ya dauko wasu kwayoyi ya hade tare da ruwa sai ya juyo ya fito daga bathroom ya zauna saman kujera ya lumshe ido yana sauke numfashi a hankali. Nawwara ce kadai macen da yake gani idan ya rumtse idonsa, duk da a yanzu ya sadakar ba zata taba zama tashi ba, yana ji a jikinsa kamar ba zata sake rabarsa, but he's happy da ta yi aiki da shi ta maida da shi cikakken namiji, dukan wani canji daya samu a rayuwarsa yasan ta dalilin Nawwara ne, domin be yi zaton zai iya daina shan cocaine ba amman gashi yanzu komai ya zama tarihi, and now he can read Quran duj da be yi nisa sosai a ciki ba amman ya san bakin domin kullum Malaminsa yana zuwa yana koya masa har ma da wasu littafan na daban da kuma bayani akan sallah da wasu abubuwan na addini, shi kansa a yanzu yana jin dadin rayuwarsa Saboda yana jin ya kara kusanci da Ubangijinsa hakan yasa ba janye dokan hana saka hijabi a kamfaninsa domin a yanzu ya fahimce babu komai a cikin addininsa sai rahama da jinka ga gata da addinin musuluncin yake ma ko wane musulmi, bashi da wata matsala ta rayuwa a yanzu sai tunanin Nawwara da ya zame masa kamar abinci, idan suna office har baya son su rabu saboda kewarta da yake komai ya zo masa kamar a mafarki ace Nawwara ce ta sake jiki da shi suna aiki haka, but a duk lokacin da ya tuna zancen aurenta da Bilal sai yaji kamar ya hade zuciya ya mutu, wannan tunanin ya yi tasiri a zuciyarsa da har ya zurfafa masa ciwon dake damunsa, a iya yanzu ya sadakar kuma ya yarda rayuwarsa ba mai tsawo ba ce a duniya, saboda matsala da cocaine ya haifar masa da kuma yawan tunanin da yake a baya ga kuma wanda yake a yanzu, wannan yasa shi yin saku saku da rayuwa. Wani lokacin yana kan kamar ya samu Nawwara ya fada mata hakan sai dai yasan ba zata fahimta ba kuma zata zargeshi da cewar saboda yana son bata alakarsu da Bilal ne, wannan yasa ya danne komai ya barwa zuciyarsa sai kuma mahaifinsa da Siraj da suka san da matsalar. Kalaman da ta yi masa yau a office na cewar zata aje aikinta a wannan satin mai zuwa ne suka haddasa masa ciwon kai har ya abun ya sauko a zuciyarsa, kullum sai ya kirga kwanakin da suka rage na aurenta da Bilal kamar da shi za a daura auren. Ji yayi yana da bukatar ganin dansa domin a yanzu shine kawai farincikisa, a duk lokacin da Noor yake kusa da shi yana jin dadi sai ya dinga jin kamar Nawwara ce a kusa da shi. Unkurawa ya yi ya tashi cikin karfin hali ya koma bathroom ya yi wanka ya fito ya shirya cikin kananan kaya ya feshe jikinsa da turare sannan ya dauki wayarsa da car keys ya fice daga dakin. Har ya fito harabar gidan be daina jin zafin da zuciyarsa take masa ba. Haka ya shiga motar ya dauki hanyar da zata kaishi gidansu Nawwara. A kofar gidan ya yi parking sannan ya dauki wayarsa ya kira Nawwara, bata dauka ba har ta katse sai ya sake kira haka ya jera mata kira hudu ba tayi picking sai ya fita daga motar ya je kofar gidan ya buga, sai gata ta fito hawaye shabe shabe a fuskarta. “Dan Allah dan girman Allah karka sake zuwa kofar gidan nan Jibril da sunan ganina, yanzu yanzu Bilal ya bar gurin nan da ya tararda kai ai ba zai ji dadi ba, saboda kai yau na fada min magana marar dadi, kuma na fada maka cewar komai ya kare a yanzu, tun da zaka iya komai da kanka shiyasa nima zan aje aikin saboda na samu damar kula da Bilal da kuma kaina” “Ina son ganin Noor ne shiyasa na zo” “Idan kana son ganinsa ka sanar da ni zan sa a kawo maka shi har gidanka, amman a i zuwa yanzu ka daina zuwa nan sai na yi aure” “Okay Nawwara ba zan sake ba, and ki bawa Bilal hakuri akan abubuwan da suka faru, na san mun shiga hakkinsa but yanzu komai ya wuce” Ba tare da ta sake cewa komai ba ta juya ta koma ciki, shi kuma ya cikama bakinsa iska ya busar sai ga Noor ya zo da gudu, sai Jibril ya risina kasa ya shafa fuskar dansa sai kuma ya rumgume shi ya lumshe ido. ‘Ni na jawa kaina komai saboda haka dole na yarda da rashinki’ Ya fada a ransa, a fili kuma sai ya dago fuskar dansa ya kalleshi ya ce. “Dukan abunda Nawwara ta yi da wanda na yi mun yi ne saboda kai Noor, ina son ko da bana raye ka kasance mai alfahari da ni a matsayin ubanka” “Ni ban gane abunda kake cewa ba” “Zaka gane wata rana, ina son ka zama mai biyayya ga Mahaifiyarka ita ce zata rayu da kai har ka girma, na yi farincikin da na rayu da kai Noor ina son ka sosai” Ya rumgume shi idanuwansa cike da kwalla, sosai da sosai yake shakar kamshin jikin Noor, domin haka na masa dadi yana jin kusan da dansa sosai. “Noor zamu je yau ka yi weekend gidana ko?” “Ee amman Uncle Bilal ya ce zai je da ni yawo gobe Saturday” “Yaushe ya zo?” “Dazu” “Okay, idan kun dawo sai na aiko a dauko min kai ka ji” “Okay Daddy Momy har da cake ta yi ma Uncle Bilal” Wani irin daga kai ya yi ya sauke numfashi saboda yadda maganar ta sokeshi. “Okay je cikin gida ni zanje gida kar dare ya yi” Ya sumbanci goshinsa. “Goodnight” “Goodnight” Noor ya fada yana daga masa hannu sannan ya shige cikin gida, shi kuma ga mike tsaye ya jingina da motarsa ya lumshe ido yana sauke ajiyar zuciya. Ya samu thirty minutes a gurin sannan ya bude motaraa ya shiga cikin rashin dadin rai. *** *** *** NAWWARA POV. Na farka yau cikin rashin dadi rai saboda abunda ya faru jiya, sam ban jidadin yadda Bilal ya kasa fahimta ta ba, duk da nasan kowa waye dole ya zargi wani abu a tsakaninmu, amman komai ya kare a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119