Chapter 108
Chapter 108
ya yi. “Oucccc am such a fool taya Nawwara zata kirani yanzu ba bayan fushi take da ni” Bude idonsa ya yi ya danna picking ya kara a kunne. “Hello Abbah” “Jibril kana lafiya?” “Lafiya kalau Abbah ya Abuja” “Al-hamdulillah ya Noor yaushe zaka shigo” “Da dai cikin satin nan ne amman yanzu ban sani ba gaskiya” “Ya dai kamata kasa lokaci ka zo” “Wani abun ne?” “Akwai maganar da ya kamata mu yi” “Ba zamu iya yi ta waya ba?” “Magana ce mai muhimmanci zai fi kyau idan kana nan zaka fi fahimtar abun” “Idan magana mai muhimmanci ce ka fada min a waya dan bana tunanin zuwa yanzu” “Magana ce akan aurenka Jibril be kamata kana zaune haka nan ba, yarinyar nan da keke so aure zata yi, zama haka ba ba zai maka ba, na sha baka dama ka fitar da wacce kake so sai ka ce sai Nawwara kuma yanzu gashi yarinyar nan aure zata yi, dole ne idan ta yi aure zaka karbo dan ka dan ba zamu barshi can ba, babu yadda zaka yi ta gujeka kuma ta zauna da danka, na san ka yi kuskure kuma ka zalinceta amman ai an bata hakuri so dole ne ka nemi matar aure wacce zata rike maka yaronka” “Haka ne Abbah amman har yanzu ba a daura mata aure ba ba lallai ne ta auri yaron da yake son ta ba” “Wai kai ba zaka cire ranka a gareta? Yanzu dai mun yi magana da Hajiya (Step Mother din shi) akwai wata yarsa margayi Alhaji Dahiru wato Salima wacce ta fito sai kaje ka gani idan kana sonta ba zamu cilasta maka ba, amman fa bazawara ce yaranta hudu sai dai duka yaran suna hannun Babansu” “No Abbah wanda zai auri Nawwara ya fasa aurenta saboda mahaifiyarsa ta hana just saboda abubuwan da suka faru tsakanin mu, shine sai Nawwara ta bada damar na tura nawa magabatan” Abbah ya dan yi shiru kamin ya ce “Jibril ka tabbata?” “Yes Abba, jiya take fada min haka kuma kasan yadda na ke son ta Abbah, ni yanzu abunda na ke so da kai kasa rana cikin satin nan ka zo ku ga iyayenta” “Jibril ka tabbata” “Yes Abbah” “Shikenan zan samu iyayenka na nan mu yi magana” “Thank You” Daga haka Abbah ya kashe wayar, sai Jibril ya yi murmushi. “Idan ma karya ne Bilal yake ai idan Abbah ya zo dole familynta zasu fada masa gaskiya” Ya fada kana na nufi kitchen dan hada kansa tea. NAWWARA POV. Na ci kuka sosai a daren nan, na kasa yarda da abunda Bilal ya fada min na san yana so na dan me mahaifiyarsa zata shiga tsakaninmu? Miyasa idanuwan wasu suke rufewa su kasa fahimtar komai sai kansu. Washe gari da asuba bayan na gama sallah na dauki qur'ane na karanta Yasin wato zuciyar qur'ane, Suratul Yasin tana da fa'idodi da yawa ga musamman ga mutumen da yake cikin matsala da damuwa ta matsalar mijin matukar ka karanta sau goma sha biyar zama daya idan ya gama ya roke Allah bukatarsa idan da hali sai mutum ya yi sadaka, ba ni da halin karanta Yasin sha biyar hakan yasa na karanta ta sau daya na karanta Ayatul Kursiyo dari domin ita ma tana da nata fa'idan sosai kuma idan Allah ya amsa maka kamar yankan wuka yake, bayan na gama na roki Allah ya zaba min abunda duk yafi zama alheri a rayuwata, sannan na aika Jamila ta siyo min kosai na yi sadaka, a lokacin Sakina har ta shirya mana abun kari sun yi breakfast ni ce kawai ban ci komai ba tun tashina. Dakin Inna na shiga na gaishe ta a lokacin Sakina ta gama shiryawa ita da Jamila suka kama hanyar makaranta, bayan sun fice Inna ta kalleni ta ce. “Nawwara ki yi hakuri da yadda rayuwa ta zo miki, kuma ki yarda duk abunda Allah ya zaba miki shi yafi zama alheri a gareki, ni dai ina nan ina ta yi miki addu'a, dan haka ki daina sa kanki a damuwa, tashi kije ki zuba abinci ki ci” Na tada kai na kalleta idanuwa cike da hawaye. “Amman Inna kina ganin wannan dalilin kawai ya isa yasa Mahaifiyarsa ta hana shi aurena?” “Ya isa mana, idan kika duba daman can ai ba sonki take ba, kuma tana ganin an wulakanta mata da, ni kaina babu irin maganar da bata fada a gabana ba lokacin da na ke zuwa duba shi, amman idan har Allah ya rubuto ke matarsa ce Wallahi bata isa ta hana ba, ki sawa kanki wannan” Na gyada mata kai na share hawayena sannan na mike tsaye ina amsa sallamar da naji wani namiji na yi a waje, bakin kofar na nufa babu mayafi a jikina hakan yasa na leka da kai na yayinda jikina yake cikin gidan, wani saurayi saman babur hannunsa rike da ledoji sai ya miko min. “Ga sako daga Candy Restaurant Jibril ya ce a kawo ma Noor” Kamar ba zan karba ba, sai kuma na mika hannu na karba ba tare da na ce masa komai ba, dakin Inna na dawo na aje ledodin tare da fadin. “Wai Jibril ya aiko a kawo ma Noor, ni ban gane masa ba ya raina abincin gidan nan ko mai?” “Ba raini ba ne, yana ganin dacewar hakan ne kawai” “Ina Noor din?” “Yana bandaki tun dazu ya shiga” Cewar Inna sai gashi ya shigo dakin yana tafiya a hankali. “Momy gurin kaikayi yake min” “Karka sosa dai ciwon zai iya tashi” Na fada masa, sannan na juya na koma dakinmu jin wayata na ringing. Jibril ne yake kirana katse kiran sai ya sake bugowa cikin fushi na dauka “Wai ba zaka daina kirana ba ne?” “Amman kin san ba ke na kira ba Noor na kira dan me zaki dauka? Na ce ina son magana da ke ne? Da na na kira kuma kin sani na ce zan siya masa waya saboda na rika kira ta nan kin hana ya kike so na yi” “Akan me zaka aiko masa da abinci bayan kuma kasan muna da shi” “Ta nan kika bullo kuma? Na aiko masa ne saboda na san ya saba da abincin ba zai iya cin wani abinci bayan wannan ba a yanzu, kuma ina da hakki na ciyar da dana bana son wata dogowar magana da ke dan Allah ki bashi waya na tambayi lafiyarsa ko kuma na zo gida yanzu na duba shi” Kashe wayar na yi na koma dakin Inna sai gashi ya kira na mikawa Noor suka gaisa, sun dade suna waya daga karshe Noor ya fita daga dakin ya koma can gurin bandaki yana magana kadan-kadan da alama wani abun yake fada masa, sannan ya dawo ya kawo min wayar. “Momy wai ya ce yana gaida Inna da kowa da kowa amman ba da ke ba” Ya fada yana dariya, tabe baki na yi na tashi naje ya dauko kofi na zuba koko nasa suga na dawo dakin na zauna ina sha, domin shi kadai na ke jin zan iya sha kasancewar bana cikin dadin rai. Guraren goma da kwata ina yi ma Noor wanka tsakar gida sai ga Baba Sulaiman ya shigo
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119