Chapter 100
Chapter 100
Inna ta kasa ce masa komai, ni da nake zaune nesa da ita na kalleshi cikin hawaye na ce “Ban san komai a akan batan Noor ba, idan kuma baka yarda da ni ba, zaka iya sakawa a kulleni kamar yadda ka yi ma Bilal” “Na rasa mahaifiyata Nawwara a lokacin da ban san miye duniya ba, ban sani ba ko zan iya jure rashin Noor” Haka kawai ya fada ya mike tsaye ya shafa kansa ya fice. Sai da ya fice sannan Inna ta ce “Miyasa baki fada masa gaskiya akan abokinsa ba? Mai yiyuwa shi ya sace Noor” “Idan kuma ba shi bane fa Inna? Sai mu dauki laifin mu dora masa? Mai yuyuwa yan satar mutane ne suka sace shi ko kuma yan garkuwa da mutane sai mu dauki laifin mu dora masa?” “Amman idan ba a bullowa wannan matsalar da wuri ba zata iya zama babba, kina da dalili da hujja mai karfi ta zargin wannan mutumen kuma shi kadai ya rage a yanzu wanda zamu iya zargi” Tabbas ni kaina zuciyata a yanzu Siraj take zargi, amman ina cikin kwankwanto saboda kar na yi zargi na jefa rayuwarsa cikin matsala daga karshe kuma ya zama ba shi din ne ba. Ina jin kewar da na sosai kullum mafarkinsa na ke yadda muke rayuwa da shi a cikin gidan yana ta min gizo a ido wani lokacin har ji na ke kamar yana kirana. JIBRIL POV. Daga gidansu Nawwara kai tsaye ya nufo gida har ya iso be daina hawaye ba, zuciyarsa kuna bata daina kuna ba, nan da nan ya fara tarin jini sai da ya saka tissue ya goge, babu wanda idanuwansa suke son gani kunnuwansa suke son jin muryarsa a yanzu irin Noor, daman tun kamin faruwar hakan jikinsa yake masa ba dadi ashe na rabuwa da dansa ba, rabuwansu na karshe ya tuno lokacin da yaje daukarsa yace Bilal zai fita da shi, rumgumar da ya yi masa ya dingajin kamar yanzu yake masa ita. “Ina kake Noor ina kake?” Ya tambaya yana buga sitarin motarsa yana kuka sosai kamar makaramin yaro. “Miyasa nake ta rasa abubuwan da suke da muhimmanci a rayuwata ne? Miyasa ne? Allah karka karbi rayuwar da na a yanzu da na fi bukatarsa Allah kada ba basu damar cutar da shi Allah ka kubutar min da dana” Kamar zai fadi haka ya fito daga motar yana kuka be damu da ma'aikatan gidan su ga kukansa ba shi dai matsalarsa da isheshi. A falo ya zauna yana ta misalta irin yadda Noor yake idan ya zo gidan, sai kuma ya dauko wayarsa ya bude gallery yana kallon hotunan Noor da kuma wanda suka yi tare. “Wa zai min haka a duniyar nan? Mina tarewa wani? Bilal mi na maka? Oh Allah” Ya mike tsaye yana share hawayensa, a dare kasa bachi yayi kamar dai ko wane dare yana ta aikin sallah da rokon Allah ya fito masa da dansa, kudi mai yawa ya diba ya bawa Malamin nan mai koya masa karatu akan yasa a yi masa addu'a Allah ya bayyana masa dansa. Yana zaune yana shan ruwan tea kamar kullum domin tun da abun ya faru baya cin komai sai ruwan tea maganinsa ma ya daina sha. Sai ga Kiran Abbah ya shigo wayarsa cikin yanayin damuwa ya daga. “Assalamu Alaikum” “Wa'alaikassalam Jibril ka zo gida yanzu nan ina jiranka” “Okay” Yana kashe wayar ya mike tsaye ya shiga bedroom ya canja kayan jikinsa daga jallabiya zuwa kananan kaya, a gaggauce ya fito saboda yasan yau Abbah zai bar sokoto yasan dalilin kiransa ba zai wuce ya fada masa Maganganun hakuri ba. Ko da ya isa Abdullah fodio road ya tararda Abbah tare da wani bako, bayan sun gaisa sai Abbah ya gabatar masa da shi. “Ga Dsp Sani Muazu nan na fada masa komai akan case din Noor, abunda yasa na ce kasa a saki Bilal saboda a bullo masa ta wata hanyar, tun da har ya kwashe kwana uku a station da duk irin wahalar da ake bashi be fadi gaskiya ba zai taba fada ta hanyar tsiya ba, so wannan dsp ya san yadda xai bibiyi Bilal har a gano gaskiyar lamarin” “Thank you Abbah” Abbah ya dafashi. “Ka kwantar da hankalinka Jibril Noor dinka yana nan lafiya kalau, kuma za a gano shi da yarda Allah duk wani bayani sai kanyi masa ni yanzu zan wuce” Sai da Abbah ya koma ciki yayi yan mintuna sannan ya fito Jibril ya raka shi har gurin mota suka yi sallama dan baya jin xai iya binsa har airport, bayan Abbah ya wuce ne Jibril ya dawo ya cigaba da yi ma Dsp bayani akan abunda ya sani a game da Bilal sai Dsp ya nemi hoton Bilal da addirensa da komai nasa. Suna haka wayar Jibril ta yi ringing yana dubawa ya ga Number Siraj cikin sauri ya dauko a tunaninsa ko zai sanar da shi wani abun ne, domin shi ma ya damu sosai akan batan Noor duk wani shiga da fita da ake tare da shi ake yinsa. “Hello Siraj” “Jibril kana ina ne?” “Ina nan Abdullah Fodio Road lafiya?” “Nawwara ce ta kirani a waya tana kuka tana min magiya wai na fada mata inda danta yake” “What? Ita da kanta?” “Yes ita ce ni abun ya bani mamaki ne” “Kana ina ne? ” “Ina gida” “Bari naje na sameta” Yana kashe wayar ya mike tsaye yana kallon Dsp “Taso muje can inda zamu samu hotonshi” Tare suka fito sai Dsp ya shiga motar Jibril suka nufo gidansu Nawwara. Sai da ya tsaya nesa da gidansu Bilal ya nunawa dsp gidan sannan ya karaso kofar gidansu Nawwara, kiranta ya yi ya sanar mata yana kofar gida yana son magana da ita sai ta ce ya shigo ciki. Ko da ya shigo ya sameta tsakar gida tana aikin kuka duk ta rame ta yi baki sosai kamar ba ita ba, sai da ya gaisa da Inna sannan ya zauna saman tabarmar da Inna ta shinfida masa yana kallon Nawwara har cikin ransa yake jin kukanta. “Ki yi hakuri Nawwara dan Allah ki daina kukan nan kina tada min da hankali” “Jibril Siraj ne ya sace Noor” Ta fada cikin kuka. “What?” Ya kalli Inna sai kuma ya maida dubansa gurin Nawwara a tunaninsa bakinciki ne yake son taba ta. “Listen Nawwara...” “Wallahi ba karya na ke ba, shi ya kade Noor kuma yana cikin plan dinsa kashe Noor da ni da kuma kai” “Okay na ji shikenan zan masa magana” “Ba hauka na ke ba Jibril ka tambayi Rabi ka ji ita ta fada min komai, shiyasa na koma aiki tare da kai nasa ka karbe kamfanin daga hannunsa ya dawo hannunsa shine yake kiran Abbah ya fada masa komai saboda ya lalata maka rayuwa yasa ka fara shan cocaine, kuma shi ya kade Noor da mota lokacin da suka taso makaranta, Noor ya ganshi shiyasa ya ki yarda su yi ido hudu da Noor saboda karya nuna shi” “No Nawwara Bilal ne ya kade Noor” “Ba shi ya kade ba, lokacin da Noor ya yi hadari Bilal yana kamfaninka yana aiki, shine duk ya tsara wannan Jibril ka karda da ni, Rabi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119