Chapter 86
Chapter 86
na yafe maka” Lumshe ido ya yi sai ga hawaye sun sauko masa, yaja wani dogon numfashi ya sauke, sannan ya bude idanuwansa ya kalleni “Yanzu za ki iya aure na kenan?” “Dan na yafe maka ba shi yake nufin zan iya sake zaman aure da kai ba, ni ina da wanda zuciyata take so” “Wa kike so Nawwara? Wanene wannan wanda ya fini sa'a da dacewa a rayuwa? Wanene wanda be shirya zaman duniya a yanzu ba?” Na shiru ina kallonsa. “Mustapha ne ko?” Kamin na ce wani abu sai wata nurse ta turo kofar dakin ta shigo hannunta rike da na Noor. “Sir an gama” “Thank you” Ya fada yana share hawayensa, sai da ta fice sannan ya nufi Noor ya dauke shi ya rumgume. “Come here my happiness” “Momy yanzu kika zo?” Na daga masa kai sai na karasa gurin gadon na zauna, Jibril kuma ya zauna a kujerar da ke fuskantata yana rumgume da Noor, idanuwansa na ta xika da hawaye tana kallona. Muna haka aka turo kofar dakin a aka shigo Zinatu ce tare da Rabi sai kuma wani bakon mutun da ban waye fuskarsa ba. Da dan farka ta karaso kusa da mu ta aje ledodin da ke hannunta sannan ya zauna kusa da ni tana kallon Jibril. “Ashe kana nan” “Akwai wani gurin da ya kamata na kasancene bayan nan?” Ya fada yana mikawa mutumen hannunsa su gaisa. Rabi kuma ya zo tana mikawa Noor hannu “Zo nan dan Daddynsa” Dariya kawai ya yi mata amman be yarda ya bar jikin Jibril ba, ya labe sosai kamar wani karamin yaro mai shan mama. “Sir Akwai maganar da ya kamata mu yi” “Tana da muhimmanci ne sosai?” “Eh akan abunda kasa ayi ne, kuma Siraj yana waje yana jiranka ya ce a gaishe da Noor” Zinatu ta mike tsaye ta karbi Noor shi kuma ya tashi ya fice dare da mutumen da kuma Rabi. “My Son ya jikinka?” “Na ji sauki Daddy ya ce nan da kwana biyu za a warware hannu” “Mashallah Allah ya tsare gaba ya kara lafiya” “Amin” Ya amsa bakin nan chakoi, sai ta kalleni. “Kin kusa komawa aiki kenan ko?” “Inshallah” Daga haka ban sake cewa wani abu ba, itama bata sake cewa ba, sai ma dauko ledar da ta zo da ita da tayi ta bude ta fiddo chocolate mai shegen tsada ta mikawa Noor. Bayan kamar mintuna talatin sai Rabi ta sake shigowa tana fadin. “Zinatu Siraj na kiranki wai ki zo zai wuce” Zinatu ta sauke Noor saman jikinta ta aje shi kasa tare da yi masa kiss. “Allah ya kara sauki da na” “Amin na gode” “Nawwara na wuce” “Mun gode Zinatu Allah ya bar zumunci” “Amin” Bayan ta fice, Rabi ta maida kofar dakin ta rufe ta nufo ni tana fadin. “Nawwara ina son muyi magana da ke mai muhimmanci” “Akan me?” “Akan ke da Noor da Jibril da kuma Siraj abunda ya shafi rayuwarku ne ku duka” Gabana ya fadi “Ban gane ba” “Asirrance na ke son mu yi maganar, amman kamin nan ko kin san cewar Jibril ya kori Bilal a kamfani tun last week? And there's something behind Noor accident...” Na mike tsaye da sauri. “When how i don't understand?” Kamin ta kara cewa wani abu sai ta ga Jibril ya turo kofar dakin ya shigo, sai ta yi saurin juyawa tana dariya. “Kin jiki Nawwara da wata magana, masu kudi ai suna can inda suke, ni dai na tafi Allah kara lafiya” Kamar na ce wani abu sai kuma na amsa da. “Amin na gode” Tana ficewa, Jibril ya kalleni ya ce. “Kin san an kawo Mustapha a asibitinmu kuma ba shi da lafiya sosai, yana icu room 14” “Na sani” “Mi kike son a masa?” Na masa wani kallo kamar ban fahimci abunda yake cewa ba. Sai yasa hannunsa aljihu ya ciro karamin hoton Habiba ya mika min. Na karba hannuna na rawa sam na manta da inda na jefarda hoton ma. Ina karba sai ya juya ya fice ya bar nan tsaye da mamaki, ya aka yi yasan abunda Mustapha ya aikata? Ina ya samu hoton Habiba? Me yake nufi da abunda nake son a yi masa, ga kuma maganganun Rabi da suka tsaya min a rai. Saurin juyawa na yi na fita harabar asibitin ina tambayar inda icu yake, aka fada min sai na doshi gurin da sauri ina duba number din room din har na kai ga mai 14, ina dosar dakin sai Jibril ya fito tare da wasu Nurses, kallona kawai ya yi ya dauke kai ya fice, ni kuma na saki baki jikina a sanyaye ina kallon dakin, Mustapha nake hangowa da ke kwance kamar gawa, Mutanen da ke cikin dakin suna ta rusar kuka, ban san lokacin da nawa hawayen suka fara zuba ba, na juyo da sauri na biyo bayan Jibril hangosa na yi tsaye yana magana da wani likita na doshi inda yake ina hawayena bakina na rawa kafafuwana kuma kamar zan fadi. Yana hangoni ya yi saurin sallamar mutumen ya shige dakin, ni kuma ina isa na baki kofar office din na fada. “Me ka masa Jibril? Me ka masa?” Ya zauna saman kujera yana kallona “Duk mutumen da ya kashe rai shima kisa ne ya cancanta da shi, daukar fansar yar uwarki na yi miki” “Be kashe rai ba, fyade kawai ya yi mata miyasa zaka kasheshi mi ya kama?” “Ba shi kadai zan kashe ba?” “Mutum nawa zaka kashe?” “Adadin mutanen da zasu furta ko kuma su nuna soyayyarsu a gareki, kamar Bilal” Ya fada yana tabe baki, ni kuma na zaro ido naja baya baya har ina kokarin faduwa, sai kuma na juya a firgice na fice daga office din kamar mahaukaciya. ____________________________ Da gaske Jibril ya kashe Mustapha? Ko dai mafarki ne Nawwara take? Mai Rabi zata fadawa Nawwara mai muhimmaci har haka ne? Mi ta sani akan Siraj da Noor da kuma Nawwara? I can't wait for the next chapter 😍 KhadeejaCandy ce ✍️ [11/8, 9:37 PM] +234 703 352 5246: *RAI BIYU...♥🖤* Wattpad @KhadeejaCandy 4⃣8⃣ Har na kawo bakin gate din asibitin kuka na ke ina ta tunanin abun yi, wane irin mutum ne da zai kashe rai saboda cin ma wata bukata tasa ta kanshin kansa? Ko ni da na tsani Mustapha ba zan iya kasheshi ba ko na saka a kasheshi ba, bayan shi kuma ya ce Bilal ne next, dole ne na sanar da police wannan maganar ba zan iya kyalewa ba, wayata na dauko na kira Bilal bugu daya ya dauka muryarsa da walwala da alama yana cikin farinciki. “Nawancy” “Kana ina” “Ina kofar gidanmu” “Dan Allah ka sameni guiwa station yanzu” “Lafiya? Kuka kike yi” “Ka zo yanzu ka ji” “Okay tau” Daga haka na kashe wayar na tari achaba na hau domin shi ya fi kusa da station, ko da na isa har ya isa bakin station din yana ta yi min waya, yana ganina ya doso inda na ke yana tambaya dalilin kiransa da na yi. “Bilal Jibril ya kashe Mustapha kuma ya ce kai ne na biyu” “What? Nawancy kin san abunda kike fada kuwa” “Na sani na gani da idona ya kasheshi” Na fada ina
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119