Chapter 37
Chapter 37
jin da kamar akwai wani abu” “Babu komai kawai ina musu jan ajine saboda susan ba ko wanne mai neman aiki ba ne wulaƙantacce, zan koma aiki Inna ai dole ma ne na koma aikin ko dan na bawa marar ɗa kunya! Kuma ni kaina ina da buƙatar aikin saboda zai taimaka mana mi tallafawa kan mu da kan mu” Na faɗa ina sauke ajiyar zuciya Inna kuma tana amsa sallamar Malam Haruna mai gidan da muke haya...! *RAI BIYU...♥️🖤* Wattpad @Khadeeja_Candy 2⃣5⃣ Bayan Inna ta amsa sallamar ta je ta ɗauko hijbinta ta saka sannan ta ƙarasa ƙofar gida suka gaisa da shi. Sama-sama na ke jiyo firar da suke har Inna na faɗin Innalillahi, kamar na unƙura na tashi sai kuma wata zuciyar ta ce na zauna tunda maganar manya ce ake ko ma minene idan ta zo ai zanji, sai dai jikina na ta raya min ba abun daɗi ba ne. Sun ɗan ɗauki lokaci suna maganar daga bisani na ji muryar Inna tana roƙon a tausaya mana shi kuma yana faɗin babu yadda zaiyi. Bayan sun gama maganar Inna ta dawo cikin gida jikinta a sanyaye fuskarta kuma na nuna alamun damuwa. “Lafiya Inna miya faru?” Zama ta yi kusa da ni tana nuna min kuɗin dake hannunta. “Wai an sai da gidan ya kawo mana ragowar kuɗin hayarmu na wata takwas kuma wai sati ɗaya wanda ya siye gidan ya bamu” Kamar daga sama aka jefo maganar haka na jita cikin kunena, zuciyata ta hau bugawa da hauri na zaro ido hannuna a ƙirji na ce “Sati ɗaya kuma? Waya siye gidan ne?” “Oho” Ta faɗa idonta cike da ƙwalla, furucin da na yi na ɗazun ne ya fito da Sakina, Jamila da kuma Noor da gudu suka nufo inda muke zauna suna ta rabon idon da son jin abunda muke tattaunawa. “Inna miya faru?” “Tashi zamu yi Sakina an saida gidan” Inna ta amsata cikin wani irin kalar murya marar daɗi. “Tau ina zamu koma, waya siye gidan hala?” Jamila ta tambayi Inna. “Allah masani” Dukansu ɓata fuska suka yi da alama suma maganar tashin be musu daɗi ba domin sun saba da unguwar anan haifesu ga ƙawaye da ƴan'uwa kusa da su taya zasu jidaɗin tashin? Idan muka tashi ina zamu koma ? Babban gida ko ina? “Haya yanzu tsada take ina ma zamuje a bamu ɗaki ban sani ba, babban gida ma idan muka ce zamu zauna babu guri tun da duk sun kame ɗakunan waya ma zai bamu haya da dubu ashirin datara da suka rage mana na ragowar kwanakinmu kai Innalillahi wannan rayuwa daga wannan sai wannan” Cewar Inna hawaye na zuba a idonta, ni kuma na kalleta na ce “Ko dai karin kuɗin hayar yake so?” “Na tambayeshi yace aa shi ai ya riga ya siyar da gidan” Na yi shiru inata nazari wannan wane irin saida gidana ne ba a shigo ciki anga yadda gudan yake ba kawai sai muji labarin an siye shi kuma wai sati ɗaya mu tashi? Lallai wannan daga gani shiri ne, kuma ba zai wuce Mustapha ba shine kawai na ke zargi. “Inna ki kwantar da hankalinki zan koma aiki idan aka biyani kuɗin aikin sai mu haɗa da wannan mu kama wani gidan haya, zan roƙeshi ya yi mana haƙuri har ƙarshen wata zamu tashi mu bar masa gidansa” Na faɗa ina kallon Inna sai Sakina ta ce “Ko kuma a faɗawa Ya Bilal” Na katsa mata tsawa. “Ke wane irin Bilal kuma Wallahi duk wacce taje cikinku ta faɗa masa sai na ɓata mata rai, haka kawai sai mu ɗauki lalurar duniya mu aza masa, shi ma ai yana da tashi lalurar” Haka muka wuni gidan shiru-shiru kamar wanɗanda aka yi ma mutuwa duk jikinmu ya yi sanyi, tsoron kwana da muke ji a gidan sai ma ya cire mana saboda hankalinmu ya karkata kan wannan matsalar. Bayan sallah magariba Inna tace naje Babba gida na faɗa musu halin da ake ciki, ba musu na tashi na ɗauki Hijabin da na cire wanda na yi sallah da shi na saka na kama hannun Jamila muka nufi ƙofar fita. Abun mamaki muna fitowa muka dami Mustapha a tsaye kamar daman can mu yake jira, kallon kallo muka riƙayi da shi, idonsa narau-narau fuskarsa abun tausayi kamar mai shirin yin kuka, ni ko babu komai a idona sai wuta mai tsananin ci a lokacin da ta ga maƙiyinta. “Guri....guri...gurin.. inna na..zo Daddy ne ya aiko...ni-” Haka maganar ta riƙa taƙe mishi kamar marar gaskiya, ni kuma abun sai ya bani mamaki kuma ya sakani murmushin takaici. “Like seriously? Wai Mustapha ko baka san gidansu Habiba ba ne? Baka san ni yayarta ba ce?” Sai ya amsa min da sauri. “Na sani! Zan iya rantsewa da Allah ni ban taɓa kula kina cikin unguwar nan ba sai da kika mareni, daga lokacin da kika mareni sai na sa aka min bincike kanki a maimakon na tsargu sai na samu kaina da tausayin halin rayuwar da kuke ciki kuma na yi nadamar abunda na yi ma Habiba kasancewarta ƙanwarki, a lokacin da ta sameni ta bani haƙuri akan karna cutar da ke ina ta shirya abunda zan miki na rama abunda kika min amman sai zuciyata ta hanani saboda tausayinki da take, kin fini kwarjini da ƙima Nawwara kuma ke jaruma ce na gano haka ne daga lokacin da kika ɗaga hannunki kika mareni bayan kuma ba dake nake faɗan ba siya kika yi, wannan ya karantar da ni wani abu a rayuwata lalle ni a idon wasu ba kowa bane tun har mace kamarki zata iya ɗaga hannu ta mareni a bainar jama'a, bayan ko ƴaƴan masu kuɗi basu taɓa unƙurin nuna min ko da yatsa ba balle kuma harara. Na rasa natsuwata daga lokacin da labarin mutuwar ƴar'uwarki ya same ni, mutuwar Habiba ta canja ni Nawwara, ta tunatar da ni abubuwa da dama da na manta i understand the distance between right and wrong, ta kuma ta sanar da ni abubuwan da ban sani ba a rayuwar duniya, if i begin to tell you how terrible i feel for what I did to your family Nawwara you will find a place in your heart to forgive me, da ace kun sanar da ni tana da ciki da na karɓi cikin kuma na ɗauki nauyin komai na ta, but it too late labarin mutuwarta kawai ya sameni ba a faɗa min dalilin mutuwarta ba amman ni na san cikine saboda ance ta yi zubar jini, Nawwara i'm looking forward to corrected all my mistakes, i made a mistake because I am only human dan Allah Nawwara ki yafe min” Ta yanayin muryarsa nake fahimtar hawayene suke zuba a idonsa, domin duhu ya sauko bana iya ganin fuskarsa da kyau, sai dai na fahimci hawaye yake kamar yadda nima nake tunawa da ƴar'uwata. “It's too early to ask my forgiveness Mustapha, i know you are here to play a game with me too” “No don't get me wrong, i know it too early i'm sorry i shouldn't talk about this, ga wannan ko zaku buƙaci yin wani abu da shi” Jamila na ganin damin kuɗin da ya miƙo min ta juya da gudu ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119