Chapter 67
Chapter 67
na ɓakinciki da jin zafi, yanzu irin wannan mutunen ne na haihu da shi? Ina baƙincikin da ya kasance uban Noor sam, ɗa na be yi dacen uba ba, dan haka ban zan nuna masa ko kuma faɗa masa cewar Jibril ne ubansa na gaskiya ba. “Bana neman mata Naj, Aisha ce kawai na ke taraiya da ita ma kuma na daina na tuba, cocaine ɗin ma akwai dalili shanta da na ke, amman na ji kamar kin yi wata magana, na ji kin ce ɗa me kike nufi akwai abunda ya kamata na sani ne?” Ganin yadda yake matsowa yasa na yi hanzarin miƙewa tsaye har ina ɗauke numfashi, shi kuma yana ta kallona kamar mai karantar abu a fuskata, sai takowa yake har sai da ya kowa daf da ni...! “Ina da ɗa ko Nawwara...?” ____________________________________ Zaku ga wasu kalmomin kamar ba a ƙarasa ba wasu kuma ana mistakes da yawa ana dai akwai errors or omissions a ciki, hakan yana faruwa ne saboda rashin editing, idan har na ce zan tsaya editing zai ɗauke ni tsawon lokaci ban yi updated ba domin editing ya fi bani wahala fiye da typing. Fatar zaku fahimta kuma zaku min uzuri 🙏 FOLLOW ME VOTE COMMENT SHARE *RAI BIYU...♥️🖤* Wattpad @Khadeeja_Candy *Dedicated to My Asmee* 4⃣0⃣ JIBRIL POV. “Ee kana da ɗa” Shine kawai abunda Jibril yake son jin ya fito daga bakin Nawwara, wani irin bugawa zuciyarsa take da sauri, ido cikin ido yake kallon Nawwara tsantsar gaskiyarta yake son ganewa, yadda ta saki baki tana kallonsa shi kansa yasan subul da baka ta yi, yadda take numfashi yake karantar da shi irin faɗuwar gaban da ke ranta. “Kana da ɗa mana ƴaƴama zan ce, ba ka auri Aisha ba ta haifa maka ƴaƴa, na tuna ai tun kamin ka aureta ma ta samu ciki, wanda kake labarwa abokinka farinciki fal a ranka, kuma bayan ita maybe ka ƙara auren wasu matan sun mahaifa maka ƴaƴa ko kuma ka musu cikin shege” Lumshe ido ya yi ya haɗe yawun dake bakinsa ya dunƙula hannunsa ya matse sosai kamar zai dake, har ga Allah baya jindaɗin kalamanta, duk lokacin da ya tuna rayuwarsa ta baya yana jin babu daɗi ballr kuma ace ita ce da kanta take tuna masa da wannan, hakan na karantar da shi cewar ba zata taɓa yafe masa ba kuma ba zata manta ba. “Ina cikin da na barki da shi?” Ya faɗa yayinda da buɗe idonsa da suka rine suka yi ja sosai. “Cikin da ka kace ba naka ba ne? Ai na zubar domin ba zan iya ɗaukar shege a cikina ba” “Ba zaki iya zubarwa ba, ba zaki iya kashe rai ba ko da kuwa ɗan shegen ne da gaske” Kallonsa ta yi sai ta yi murmushi. “Ashe kai da kanka ka san ba ɗan shege na ɗauka a cikina ba, amman ka ce ba naka ba ne ka haɗa hotona da hoton wani namiji wanda ban taɓa sanin inda ya fito ba, saboda kawai kana neman rabuwa da ni? Da na dawo da ciki sai suka kira da karuwa wannan dalili yasa na zubar da cikin” Ta faɗa hawaye na fitowa daga idonta fuskarta kuma ɗauke da murmushi. Wani irin ƙuna yake ji a cikin ransa, zuciyarsa zafi take kamar an kunna masa wuta, yana jin rashin kyautawa a duk lokacin da ya tuna abunda ya aikata mata, tabbas yanzu ya yarda akwai wawanci, shashanci a tare da shi, duƙursawa ya yi ƙasan guiwoyinsa ya kama Hijabinta sa gashi yana hawaye. “Dan Allah Nawwara ki yi haƙuri dan Allah ki yafe min” “Daman na faɗa, saboda ka riƙa neman yafiyata yasa ka cilasta min aiki a tare da kai” “Ba dan haka ba ne Nawwara, saboda na samu kusanci da ke, ina sonki sosai Nawwara” “Ni kuma bana son ka, bana kaunarka Jibril” “Na sani” Ya fada yana hade maganarta ciki da dacin rai. Zaunawa ta yi shi kuma ya mike tsaye na koma office dinsa, sam be gamsu ba shi da tsakaninsa da Nawwara ba, tabbas ya bar ta da ciki kuma ya san ba zata iya zubar da cikin ba. ‘Ta haife shi, idan har babu haihuwa tsakamina da ita mi zai sa ta yi wannan maganar?’ Shine abunda zuciyarsa take ta raya masa, wayarsa ya dauka ya kira Siraj bugu biyu Siraj ya yi picking. “Siraj ina son kasa a bincika min duk wani abu da ya shafi Nawwara, akwai da a tsakanina da ita Siraj kasa a abincika min” “Okay” Daga haka ya kashe wayar ya kira Abbah, sai da ta dade tana ringing sannan ya dauka yana kiran sunansa. “Hello” “Jibril” “Abbah ina wuni” “Lafiya kalau ya aiki?” “Al-hamdilillah, Abbah akwai da tsakanina da Nawwara” “Waya fada maka?” “Ita ta yi subul da baka” “Kaje gidansu ko? Bana fada maka karka je ba” “Ban je ba, Abbah a nan kamfanin take aiki” “How when?” Ya kwashe komai ya fada ma Abbah amman be fada masa zance ya cilas mata aiki a tare da shi ba. Abbah ya yi shiru kamar mai tunanin abunda zai ce. “Abbah we're meant to be” “Kana son ta ka saketa? Bana son ka zama cikin irin mazan nan da ake fada Jibril ni yanzu ko wani aure ban yarda ka kara yi ba sai ka gane kuskurenka” “Wallahi Allah Abbah na canja zan zauna da Nawwara zama na tsakani da Allah ba zan taba sakinta ba, Abbah ita kadai ce take so na tsakani da Allah” “No ba yanzu, kuma na fada maka karka kuskura taka kafarka gidan nan” “Tau Abbah ba zan yi ba, amman da Mahaifiyata tana da rai da ta roka min kai ka amince, rashinta ne yasa na rasa komai, ba ni da mata ba ni da ɗa sai kai kadai kai kuma ka kasa fahimta ta” Yana fadar haka ya kashe wayar ya aje saman table, sai ya dora hannayensa saman table din ya dafe kansa ya dinga rusar kuka kamar karamin yaro. Kuka yake sosai kuka ina zai saka kanshi, kuka neman mafita, be san mahaifiyarsa ba domin be tashi tare da ita ba, amman yana jin zafin rashinta kamar yanzu ta mutu ta barshi, ji yake ina ma tana raye da yanzu ta roka masa Nawwara ta yafe masa, ta shiga cikin lamarinsa ta gyara masa komai, be taba jin zafin rashin mahaifiya ba kamar yau. Hannunsa yasa ya janyo aljihun table din da take zaune ya dauko hoton wata matashiyar mata mai kama da shi yana ta kallonta yana kuka kamar mace. Kuka ya yi sosai har sai da ya soma jin kamar jiri yana dibarsa sannan ya tashi ya shiga bathroom ya wanke fuska ya dawo ya dauki ruwan freezer ya sha, sai ya dora gorar saman freezer ya nufi kofar fita. Ko da ya fito Nawwara na zaune tana duba abubuwan da suke cikin computer, ya samu thirty seconds yana kallonta mugun burgeshi take gani yake a duk duniya babu wata mace da ta kaita daraja da kima da kuma kyau, ji ya yi kamar yaje ya rumgume kamkam a kirji, sai dai yasan ba shi da wannan damar. Karasa ya yi inda take yana kallonta da manyan idanuwansa masu kamar madara kamar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117
- 118 Chapter 118
- 119 Chapter 119