Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 6

Chapter 6

Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ta buɗe yayinda ni nake zaune ina karatun ƙur'ane. Ina jin lokacin da ta zauna kusa da ni sai dai ban kalleta ba har sai da na kai ƙarshen ayar da na ke karantawa, sannan na rufe ƙur'anen ina ambatar sunanta “Jidda” “Na'am Nawwara, jiya cikin dare na ke jin abunda ya faru kuma kin san Abba baya bari mu fita da dare, da gaske ne?” Na ɗaga mata kai hawaye na bin fuskata. “Baba ba zai yi sata ba, sai dai idan wani sheri ne aka masa” Cikin kuka na zayyana mata abunda Inna ta faɗa mana. A take ta fashe da kuka. “Nawwara ki yi haƙuri jaka ƙaddara take zuwa wani lokacin, yanzu bari na je na shirya sai muje mu ganshi” “Babu ko naira hannuna Jidda” “Ina da ɗari uku zasu ishemu” “Tau Jidda na gode” Miƙewa ta yi tsaye ta fice, ni kuma na tashi na nufi ɗakin Inna, gaisheta na fara yi sannan na faɗa mata yadda muka yi da Jidda. “Tau bari na jira har ku dawo sannan muje” Tashi na yi na koma ɗakinmu na cire tufafin jikina na ɗaura zane na ɗibi ruwa a robar da muke wanka na shiga banɗaki na yi wanka da ruwan sanyi. Tufafin jiya na ɗauka na saka ban damu da shafa mai ba, domin ba kwaliyarce a gabana ba, sai takwas har da ƴan mintuna sannan Jidda ta dawo, baƙar abaya ce jikinta sai jan mayafi, hannunta ɗauke da kular abincin. “Nawwara zo muje” Abunda ta faɗa kenan tana shigowa. Inna ce ta rigani fitowa tana gaisawa da Jidda. Sannan na fito sanye da hijabi. “Jidda sai yanzu?” “Yi haƙuri dan Allah taliya na tsaya dafa masa” Ta faɗa cike da damuwa. Jidda ƙawar arzikice dukan abunda ya dame ni kamar ya sameta ne, tana damuwa sosai da duk abunda ya shafi rayuwarta, shiyasa bana da ƙawa a duniyar nan da ta wuce Jidda. Tare muka fita tana min bita kan haƙuri da yarda da ƙaddara, ni ko bana iya cewa komai sai hawaye da ke min zuba, ganin haka yasa ta daina maganar domin tana ƙara min ƙarsashin abun ne kawai. Tun da muka shiga Napep har muka fita ni da ita babu wanda ya ce Uffan, gabana ya faɗi sosai lokacin da muka doshi station ɗin wata ƙila saboda ban saba ba ne ko kuma ina fargabar ganin halin da Baba yake ciki ne. Jidda ta lura da hakan shiyasa ta wuce gaba ta bar ni a baya saboda kawai ta ƙarfafamin guiwa. Ƴan sanda da yawa muka tarar a gurin, ta kuma ɗai-ɗaikun jama'a waɗanda nake sa ran suma sun zo kan nasu matsalar ne, muna shirin tambayar sai na hango Baba Sulaiman wato ƙanen mahaifina da kuma yayyunsa. Cikin rashin kuzari da raunin zuciya na ƙarasa kusa da su idona na zubar da ƙwalla. Baba na zaune saman tebur fuskarsa a buge jini har ya dasƙare masa saman kai da alama tun jiya suka dake shi ko kuma da dare. Ƙasa na zauna kusa da shi na riƙe masa ƙafafu kasancewar shi yana zaune saman banci ne tare da ƴan'uwansa. Kasa kallona yayi wannan baya rasa nasaba da kukan da na ke wata ƙila baya son kuka a gaban jama'a ne. Kwanon ɗumame na gefen da na zauna nasan su Baba Sulaiman ne suka zo da shi. Tsawar da Baba Ayuba ya katsa min ne yasa ni tsagaita kukan da nake har na dawo hayyacina. “Ai yanzu sun yarda za su bada belinsa amman wai sai an bada dubu ashiri” Cewar Baba Salisu yayan Baba. Ni ko na dafe kai ina sauke ajiyar zuciya, ko yanzu tsugune bata ƙare ba, ina zamu samu wannan dubu ashirin ɗin. ‘Oh Allah mun gode maka’ Na faɗa a raina ina ta ƙoƙarin tare kukana. A nan Baba Sulaiman yake faɗa mana yadda matar take son a je kotu, wai ashe dpo ɗin station ɗin ne ƙanen wacce aka yi ma satar. Bamu ƙara minti goma a gurin ba, wani ɗan sanda ya zo yana faɗa mana lokaci yayi. Duk miƙewa muka yi tsaye a nan na samu kallon bayan mahaifina kasancewar ba shi da riga ne, babu komai sai kwancin sanduna, yanayin yadda baya son motsa jikinsa kaɗai ya isa ya karantar da kai jikin na masa zafi da ciwo ne. Ban san lokacin da kuka ya zo min ba, na rumgume bayansa ina mai jin kamar na yi tsuntsuwa ni da shi mu ɓace daga gurin gaba ɗaya. “Mahaifinku be yi sata ba Nawwara, kuma be taɓa yi, ki gamsar da ƴan'uwanki da wannan” Abunda Baba ya faɗa min kenan, ni kuma na ƙara ƙanƙanme shi. Hankalin duk wanda ke gurin sai da ya dawo kaina saboda kukan da nake, babu tausayi haka ɗan sanda nan ya tisa ƙetar Baba gaba suka wuce da shi ciki. Ni kuma Jidda ta rumgume muka riƙa kuka tare. “Haba Nawwara akan ki farau? Miyr haka wuce kuje gida, mu zamu koma can zamu san yadda za mu” Cewar Baba Sulaiman. Ƙarfin hali na yi na riƙa hannun Jidda muka fito tare, a nan Baba ya Ayuba yake faɗa min wai a tura Sakina ko Jamila ta karɓo mana ɗumame. Har muka iso gida kuka na ke, Jidda ce ta iya tsayawa ta zayyana ma Inna abunda ya faru. Ba laifi na ga farincikin Inna wata ƙiƙa saboda sun yarda zasu bada belinsa ne. Bayan Jidda ta wuce Sakina ta je karɓo abincin, ni kuma na tashi na nufi ɗaki kaina na mugun ciwo, abincin da aka karɓo ma ban iya ci ba, kamar yadda Inna da Habiba suka kasa ci duk da kasancewar muna jin yunwa. Ni dai ina cikin ɗakin har aka kira sallah azahar, bayan na yi sallah na nufi ɗakin Inna, a nan take tambayata Habiba. “Bata ɗaki na ɗauka tana nan ma” “Bata nan ƙila ta je baban gida” Haka kawai gabana ya faɗi zuciya ta riƙa nasalta min kamar ba can ta je ba. Babu wani hirar kirki tsakani na da Inna saboda bana son labarta mata halin da na samu Baba duk da kasancewar idanuwana sun saka goge hoton abunda suka gani. Misalin huɗu da rabi Baba Sulaiman ya shigo gida yana faɗar an haɗa dubu shida da ɗari takwas abun da ƴan'uwa masara son zumunci, taya za a ce duk yawan familyn Babban gida ace dubu shida kawai aka haɗa. Takaici da baƙinciki ya hanini cewa komai haka na koma cikin ƙarƙashin iccen dalbejiya na zauna. Ɗari da hansi ya cire a cikin kuɗi ya miƙawa Sakina wai su saye wani abu su ci. Inna kuma ta saka Hijabinta suka fita tare wai zasu je station ɗin su kai musu ko zasu karɓa. Ni dai nasan wahala ce kawai zasu yi, ƴan sanda da basa da imani, kuma sun ce dubu ashiri ya za'ayi su karɓi dubu shida. Noor ne ya zo ya zauna kusa da ni yasa hannunsa yana share min hawayen da ban san sun zubo ba. “Momy ki daina kuka” Murmushin ƙarfin hali na yi na shafa kansa. Kan Habiba na fara hangowa ta leƙo sai ta koma ta laɓe, hakan yasa ni miƙewa tsaye ni nufi ƙofar, ƙaton hijabinta ne na islamiya a jikinta, sam babu

Table of Contents

Chapters

119 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117
  118. 118 Chapter 118
  119. 119 Chapter 119
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});